< 2 Sarakuna 9 >
1 Sai Elisha ya kira wani daga cikin ƙungiyar annabawa, ya ce masa, “Ka sha ɗamara, ka ɗauki wannan kwalabar mai ka je Ramot Gileyad.
Tad pravietis Eliša sauca vienu no praviešu bērniem un uz to sacīja: apjozi savus gurnus un ņem savā rokā šo eļļas krūzi un ej uz Rāmotu Gileādā.
2 Da ka isa can, ka nemi Yehu ɗan Yehoshafat, ɗan Nimshi. Ka je wurinsa, ka ja shi gefe daga abokansa, ka shiga da shi ɗaki na ciki.
Un turp nonācis lūko, kur Jeūs, Jehošafata dēls, Nimšus dēla dēls, un ej iekšā un liec viņam celties no saviem brāļiem un ved viņu dibina(tālākā) istabā,
3 Sa’an nan ka ɗauki kwalabar man ka zuba a kansa, ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji ya faɗa, na naɗa ka sarkin Isra’ila.’ Sa’an nan ka buɗe ƙofa ka ruga a guje; kada ka ɓata lokaci!”
Un ņem to eļļas krūzi un izlej to pār viņa galvu un saki: tā saka Tas Kungs: Es tevi svaidu par ķēniņu pār Israēli. Pēc atdari durvis un bēdz un nekavējies.
4 Sai saurayin nan, annabi, ya tafi Ramot Gileyad.
Un šis jauneklis, tas pravieša puisis, nogāja uz Rāmotu Gileādā.
5 Da ya isa can, sai ya tarar da hafsoshin soji zaune a wuri guda. Sai ya ce, “Ina da saƙo dominka komanda.” Sai Yehu ya ce, “Wanne a cikinmu?” Sai ce, “Dominka, komanda.”
Un viņam ieejot, redzi, kara virsnieki tur sēdēja, un tas sacīja: man ar tevi kas jārunā, kara virsniek. Tad Jeūs sacīja: ar kuru no mums visiem? Un viņš sacīja: ar tevi, kara virsniek.
6 Sai Yehu ya tashi ya shiga cikin gida. Sa’an nan annabin ya zuba wa Yehu mai a kā, ya ce, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Na naɗa ka sarki a bisa jama’ar Ubangiji, wato, Isra’ila.
Tad viņš cēlās un gāja namā. Un tas izlēja to eļļu uz viņa galvu un uz to sacīja: tā saka Tas Kungs, Israēla Dievs: “Es tevi svaidu par ķēniņu pār Tā Kunga ļaudīm, pār Israēli.
7 Za aka hallaka gidan Ahab maigidanka, zan kuma ɗauki fansar jinin bayina annabawa da kuma jinin dukan bayin Ubangiji da Yezebel ta zub da.
Un tev būs sava kunga Ahaba namu kaut, lai Es atriebju pie Izebeles savu kalpu, to praviešu, asinis un visu Tā Kunga kalpu asinis.
8 Dukan gidan Ahab zai hallaka. Zan kashe dukan’ya’yan Ahab maza a Isra’ila, bayi ko’yantattu.
Un viss Ahaba nams ies bojā; un Es izdeldēšu no Ahaba nama visu, kas pie sienas mīž, mazu un lielu iekš Israēla.
9 Zan mai da gidan Ahab kamar gidan Yerobowam ɗan Nebat da kuma kamar gidan Ba’asha ɗan Ahiya.
Jo Es darīšu Ahaba namu kā Jerobeama, Nebata dēla, namu un kā Baešus, Ahijas dēla namu.
10 Game da Yezebel kuwa, karnuka za su cinye ta a fili a Yezireyel, ba kuwa wanda zai binne ta.’” Sa’an nan ya buɗe ƙofa ya ruga a guje.
Un suņi ēdīs Izebeli Jezreēles tīrumā, un neviena nebūs, kas to apraks.” Tad viņš atdarīja durvis un bēga.
11 Da Yehu ya koma wurin sauran hafsoshin sai ɗaya daga cikinsu ya tambaye shi, “Lafiya? Me ya kawo wannan mahaukaci a wurinka?” Sai Yehu ya ce, “Ka san mahaukacin nan da irin maganganunsa.”
Kad nu Jeūs izgāja pie sava kunga kalpiem, tad tie uz viņu sacīja: vai miers? Kāpēc šis trakais pie tevis nācis? Un viņš uz tiem sacīja: jūs jau pazīstat to vīru un viņa valodu.
12 Suka ce masa, “Ba gaskiya ba ne, ka dai faɗa mana.” Yehu ya ce, “Ga abin da ya ce mini, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce, na naɗa ka sarki a bisa Isra’ila.’”
Bet tie sacīja: tie ir meli, stāsti mums jel! Un tas sacīja: tā un tā tas uz mani runāja un sacīja: tā saka Tas Kungs: “Es tevi svaidu par ķēniņu pār Israēli.”
13 Sai suka yi sauri suka ɗauki rigunansu suka shimfiɗa a ƙasa, suka busa kakaki, suka yi ihu, suka ce, “Yehu ne sarki.”
Tad tie steidzās un ņēma ikkatrs savu drēbi un to lika viņam apakšā uz pakāpēm un pūta bazūnes un sacīja: Jeūs ir ķēniņš!
14 Saboda haka, Yehu ɗan Yehoshafat, ɗan Nimshi, ya ƙulla wa Yoram maƙarƙashiya (To, Yoram da dukan Isra’ila suna kāre Ramot Gileyad daga Hazayel sarkin Aram,
Tā Jeūs, Jehošafata dēls, Nimšus dēla dēls, cēla dumpi pret Joramu. Bet Jorams ar visu Israēli bija apmeties ap Rāmotu Gileādā, pret Azaēli, Sīriešu ķēniņu.
15 amma Sarki Yoram ya koma Yezireyel don yă farfaɗo daga raunukan da Arameyawa suka ji masa a wata gabzawar da ya yi da Hazayel sarkin Aram.) Yehu ya ce, “In haka kuke ji, kada ku bar wani yă sulluɓe daga birnin yă kai labarin Yezireyel.”
Un ķēniņš Jorams bija pārnācis, likties dziedināties Jezreēlē no tām vainām, ko Sīrieši viņam bija situši, kad tas karoja pret Azaēli, Sīriešu ķēniņu. Un Jeūs sacīja: ja tas jūsu prāts, tad lai neviens no pilsētas neizmūk un nenoiet, to stāstīt Jezreēlē.
16 Sai ya tashi ya ɗauki keken yaƙinsa ya tafi Yezireyel gama Yoram yana hutawa a can. Ga kuma Ahaziya sarkin Yahuda ya je don yă gan shi.
Tad Jeūs sēdās ratos un brauca uz Jezreēli, jo Jorams tur gulēja. Un Ahazija, Jūda ķēniņš, bija nācis, Joramu apraudzīt.
17 Mai tsaro kuwa yana tsaye a kan hasumiya a Yezireyel, sai ya hangi rundunar Yehu sa’ad da yake zuwa. Ya ce, “Na ga wata runduna.” Sai Yoram ya umarta, “Nemi mahayin doki a aike shi yă tarye su, yă kuma tambaye su, ‘Lafiya?’”
Un tas vaktnieks, kas stāvēja Jezreēles tornī, ieraudzīja Jeūs pulku nākam un sacīja: es redzu vienu pulku. Tad Jorams sacīja: ņem vienu jātnieku un sūti to viņiem pretī, un lai tas prasa: vai miers?
18 Sai mahayin dokin ya hau, ya ruga, ya taryi Yehu, ya ce, “Ga abin da sarki ya ce, ‘Lafiya?’” Sai Yehu ya ce masa, “Ina ruwanka da zancen lafiya? Ka shiga layi.” Sai mai tsaron ya ce wa sarki, “Ɗan saƙon ya kai wurinsu, amma ba ya dawowa.”
Un tas jātnieks tam jāja pretī un sacīja: tā saka ķēniņš: vai miers? Bet Jeūs sacīja: kas tev par mieru? Stājies man iepakaļ! Tad tas vaktnieks teica un sacīja: tas vēstnesis pie tiem nonācis, bet nenāk atpakaļ.
19 Saboda haka sarki ya sāke aika mahayin doki na biyu. Sa’ad da ya isa wurinsu sai ya ce, “Ga abin da sarki ya ce, ‘Lafiya?’” Yehu ya ce, “Ina ruwanka da zancen lafiya? Ka shiga layi.”
Tad viņš izsūtīja citu jātnieku, un tas pie tiem nonāca un sacīja: tā saka ķēniņš: vai miers? Bet Jeūs sacīja: kas tev par mieru? Stājies man iepakaļ.
20 Mai tsaro ya sāke cewa, “Ya kai wurinsu, amma shi ma ba ya dawowa. Ina ganin sukuwar kamar irin ta Yehu, jikan Nimshi, gama yakan yi sukuwa kamar mahaukaci.”
Tad tas vaktnieks teica un sacīja: viņš pie tiem nonācis, bet negriežas atpakaļ, un skriešana ir kā Jeūs, Nimšus dēla, skriešana, jo viņš skrien kā traks.
21 Yoram ya umarta, “Haɗa mini keken yaƙi!” Da aka haɗa, sai Yoram sarkin Isra’ila, da Ahaziya sarkin Yahuda, suka hau suka tafi, kowa a keken yaƙinsa, don su taryi Yehu. Suka sadu da shi a filin da yake na Nabot mutumin Yezireyel.
Tad Jorams sacīja: iejūdziet! Tad viņa rati tapa iejūgti, un Jorams, Israēla ķēniņš, izgāja, arī Ahazija, Jūda ķēniņš, ikkatrs savos ratos, un tie izgāja Jeūm pretī un to sastapa Nābata, tā Jezreēlieša, tīrumā.
22 Sa’ad da Yoram ya ga Yehu sai ya tambaye shi, “Lafiya kuwa ka zo, Yehu?” Yehu ya ce, “Ina kuwa lafiya, da yake dukan bautar gumaka da bokancin mahaifiyarka Yezebel sun bazu ko’ina?”
Kad nu Jorams Jeū redzēja, tad viņš sacīja: vai miers, Jeū? Bet tas sacīja: kāds miers, kamēr tavas mātes Izebeles maucība un māņi augumā aug?
23 Yoram ya juya, ya gudu, yana ce wa Ahaziya, “Cin amana, Ahaziya!”
Tad Jorams grieza apkārt un bēga un sacīja uz Ahaziju: viltus, Ahazija.
24 Sai Yehu ya ja bakansa ya harbi Yoram a tsakanin kafaɗunsa. Kibiyar ta same shi a zuciyarsa sai ya fāɗi a cikin keken yaƙinsa.
Bet Jeūs kampa stopu rokā un šāva Joramam starp viņa pleciem, ka bulta izskrēja caur viņa sirdi, un viņš nokrita savos ratos.
25 Yehu ya ce wa Bidkar, hafsan keken yaƙinsa, “Ka ɗauke shi ka jefar a filin da yake na Nabot mutumin Yezireyel. Ka tuna yadda ni da kai muke a kekunan yaƙi a bayan Ahab mahaifinsa sa’ad da Ubangiji ya yi wannan annabci game da shi,
Un (Jeūs) sacīja uz savu virsnieku Bidekaru: ņem un met viņu uz Nabata, tā Jezreēlieša, tīrumu, Jo atminies, ka es un tu mēs abi jājām pakaļ viņa tēvam Ahabam, un Tas Kungs lika šo spriedumu uz viņu:
26 ‘Jiya na ga jinin Nabot da jinin’ya’yansa, in ji Ubangiji, kuma ba shakka zan ɗauki fansa a wannan fili, in ji Ubangiji.’ Saboda haka, ka ɗauke shi ka jefar da shi a bisa wannan fegi, bisa ga faɗin Ubangiji. Saboda haka, ka ɗauke shi ka jefar a filin, in ji Ubangiji.”
Tiešām, Es vakar esmu redzējis Nābata asinis un viņa bērnu asinis, saka Tas Kungs. Un Es tev to atmaksāšu tai pašā tīrumā, saka Tas Kungs. Un nu ņem un met viņu uz to tīrumu pēc Tā Kunga vārda.
27 Sa’ad da Ahaziya sarkin Yahuda ya ga abin da ya faru, sai ya haura hanyar Bet Haggan a guje. Yehu ya bi shi yana ihu, “A kashe shi, shi ma!” Suka ji masa rauni a keken yaƙinsa a hanya zuwa Gur, kusa da Ibileyam amma ya tsere zuwa Megiddo ya mutu a can.
Kad Ahazija, Jūda ķēniņš, to redzēja, tad viņš bēga pa dārza nama ceļu. Bet Jeūs tam dzinās pakaļ un sacīja: kaujiet šo arīdzan ratos! - Augšām ejot uz Guru, kas ir pie Jeblaāmas; un viņš bēga uz Meģidu un tur nomira.
28 Barorinsa suka ɗauke shi cikin keken yaƙi zuwa Urushalima suka binne shi a kabarinsa tare da kakanninsa a birnin Dawuda.
Un viņa kalpi to noveda uz Jeruzālemi un to apraka viņa kapā pie viņa tēviem Dāvida pilī.
29 (A shekara ta goma sha ɗaya ta Yoram ɗan Ahab, Ahaziya ya zama sarkin Yahuda.)
Jorama, Ahaba dēla, vienpadsmitā gadā Ahazija bija par ķēniņu palicis pār Jūdu.
30 Sa’an nan Yehu ya je Yezireyel. Sa’ad da Yezebel ta sami labari, sai ta sha kwalliya ta gyara gashin kanta, ta zauna tana kallo daga taga.
Un kad Jeūs nonāca Jezreēlē un Izebele to dzirdēja, tad viņa svaidīja savas acis un izgreznoja savu galvu un skatījās pa logu ārā.
31 Yayinda Yehu ya shiga ƙofa, sai ta ce, “Lafiya, kai Zimri, mai kashe maigidansa?”
Kad nu Jeūs pa vārtiem ienāca, tad tā sacīja: vai miers Zimrum, sava kunga slepkavam?
32 Sai ya ɗaga ido ya dubi tagan ya ce, “Wa yake gefena? Wane ne?” Sai bābānni biyu ko uku suka leƙo suka dube shi.
Un viņš pacēla savas acis uz to logu un sacīja: kas manā pusē, kas? Tad uz to skatījās kādi divi, trīs kambarjunkuri.
33 Yehu ya ce musu, “Ku jefa ta ƙasa!” Sai suka jefar da ita, jininta ya fantsama a jikin bango da kuma a jikin dawakai yayinda suke tattaka ta.
Un viņš sacīja: gāziet to zemē, un tie to nogāza, tā ka no viņas asinīm siena un zirgi tapa aptraipīti, un viņš to samina.
34 Yehu ya shiga ya ci, ya kuma sha. Ya ce, “Ku san yadda za ku yi da la’ananniyan nan, ku binne ta, gama’yar sarki ce.”
Kad nu viņš bija ienācis un ēdis un dzēris, tad viņš sacīja: lūkojiet pēc tās nolādētās un aprociet to, jo tā ir ķēniņa meita.
35 Amma sa’ad da suka je don su binne ta, ba su sami kome ba sai ƙoƙon kanta, ƙafafunta da kuma hannuwanta.
Bet kad tie nogāja viņu aprakt, tad tie no tās nekā neatrada, kā vien galvaskausu, kājas un roku plaukstas.
36 Suka komo suka faɗa wa Yehu, wanda ya ce, “Wannan ita ce maganar da Ubangiji ya faɗa ta bakin bawansa Iliya mutumin Tishbe. A fili, a Yezireyel, karnuka za su cinye naman Yezebel.
Tad tie nāca atpakaļ un viņam to stāstīja, un viņš sacīja: tas ir Tā Kunga vārds, ko viņš runājis caur savu kalpu Eliju no Tizbes, sacīdams: Jezreēles tīrumā suņiem būs ēst Izebeles miesu,
37 Gawar Yezebel zai zama kamar juji a ƙasa, a fili, a Yezireyel, har ba wanda zai iya cewa, ‘Wannan Yezebel ce.’”
Un Izebeles maita paliks kā sūdi laukā Jezreēles tīrumā, ka nevarēs sacīt: tā ir Izebele.