< 2 Sarakuna 9 >
1 Sai Elisha ya kira wani daga cikin ƙungiyar annabawa, ya ce masa, “Ka sha ɗamara, ka ɗauki wannan kwalabar mai ka je Ramot Gileyad.
Elisha the prophet called one of the sons of the prophets and said to him, “Dress for travel, then take this little bottle of oil in your hand and go to Ramoth Gilead.
2 Da ka isa can, ka nemi Yehu ɗan Yehoshafat, ɗan Nimshi. Ka je wurinsa, ka ja shi gefe daga abokansa, ka shiga da shi ɗaki na ciki.
When you arrive, look for Jehu son of Jehoshaphat son of Nimshi, and go in and make him arise up from among his companions, and conduct him to an inner chamber.
3 Sa’an nan ka ɗauki kwalabar man ka zuba a kansa, ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji ya faɗa, na naɗa ka sarkin Isra’ila.’ Sa’an nan ka buɗe ƙofa ka ruga a guje; kada ka ɓata lokaci!”
Then take the bottle of oil and pour it on his head and say, 'Yahweh says this: “I have anointed you king over Israel.”' Then open the door, and run off; do not delay.”
4 Sai saurayin nan, annabi, ya tafi Ramot Gileyad.
So the young man, the young prophet, went to Ramoth Gilead.
5 Da ya isa can, sai ya tarar da hafsoshin soji zaune a wuri guda. Sai ya ce, “Ina da saƙo dominka komanda.” Sai Yehu ya ce, “Wanne a cikinmu?” Sai ce, “Dominka, komanda.”
When he arrived, behold, the captains of the army were sitting. So the young prophet said, “I have come on an errand to you, captain.” Jehu replied, “To which of us?” The young prophet answered, “To you, captain.”
6 Sai Yehu ya tashi ya shiga cikin gida. Sa’an nan annabin ya zuba wa Yehu mai a kā, ya ce, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Na naɗa ka sarki a bisa jama’ar Ubangiji, wato, Isra’ila.
So Jehu arose and went into the house, and the prophet poured the oil on his head and said to Jehu, “Yahweh, the God of Israel, says this: 'I have anointed you king over the people of Yahweh, over Israel.
7 Za aka hallaka gidan Ahab maigidanka, zan kuma ɗauki fansar jinin bayina annabawa da kuma jinin dukan bayin Ubangiji da Yezebel ta zub da.
You must kill the family of Ahab your master, so that I may avenge the blood of my servants the prophets, and the blood of all the servants of Yahweh, who were murdered by the hand of Jezebel.
8 Dukan gidan Ahab zai hallaka. Zan kashe dukan’ya’yan Ahab maza a Isra’ila, bayi ko’yantattu.
For the whole family of Ahab will perish, and I will cut off from Ahab every male child, whether he is a slave or a free person.
9 Zan mai da gidan Ahab kamar gidan Yerobowam ɗan Nebat da kuma kamar gidan Ba’asha ɗan Ahiya.
I will make the house of Ahab like the house of Jeroboam son of Nebat and like the house of Baasha son of Ahijah.
10 Game da Yezebel kuwa, karnuka za su cinye ta a fili a Yezireyel, ba kuwa wanda zai binne ta.’” Sa’an nan ya buɗe ƙofa ya ruga a guje.
The dogs will eat Jezebel in Jezreel, and there will be no one to bury her.'” Then the prophet opened the door and ran off.
11 Da Yehu ya koma wurin sauran hafsoshin sai ɗaya daga cikinsu ya tambaye shi, “Lafiya? Me ya kawo wannan mahaukaci a wurinka?” Sai Yehu ya ce, “Ka san mahaukacin nan da irin maganganunsa.”
Then Jehu came out to the servants of his master, and one said to him, “Is everything alright? Why did this mad fellow come to you?” Jehu answered them, “You know the man and the kinds of things he says.”
12 Suka ce masa, “Ba gaskiya ba ne, ka dai faɗa mana.” Yehu ya ce, “Ga abin da ya ce mini, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce, na naɗa ka sarki a bisa Isra’ila.’”
They said, “That is a lie. Tell us.” Jehu answered, “He said this and that to me, and he also said, 'This is what Yahweh says: I have anointed you as king over Israel.'”
13 Sai suka yi sauri suka ɗauki rigunansu suka shimfiɗa a ƙasa, suka busa kakaki, suka yi ihu, suka ce, “Yehu ne sarki.”
Then each of them quickly took off his outer garment and put it under Jehu at the top of the steps. They blew the trumpet and said, “Jehu is king.”
14 Saboda haka, Yehu ɗan Yehoshafat, ɗan Nimshi, ya ƙulla wa Yoram maƙarƙashiya (To, Yoram da dukan Isra’ila suna kāre Ramot Gileyad daga Hazayel sarkin Aram,
In this way Jehu son of Jehoshaphat son of Nimshi conspired against Joram. Now Joram had been defending Ramoth Gilead, he and all Israel, because of Hazael king of Aram,
15 amma Sarki Yoram ya koma Yezireyel don yă farfaɗo daga raunukan da Arameyawa suka ji masa a wata gabzawar da ya yi da Hazayel sarkin Aram.) Yehu ya ce, “In haka kuke ji, kada ku bar wani yă sulluɓe daga birnin yă kai labarin Yezireyel.”
but King Joram had gone back to Jezreel to be healed of the wounds that the Arameans had given him, when he had fought against Hazael king of Aram. Jehu said to the servants of Joram, “If this is your opinion, then let no one escape and go out of the city, in order to go tell this news in Jezreel.”
16 Sai ya tashi ya ɗauki keken yaƙinsa ya tafi Yezireyel gama Yoram yana hutawa a can. Ga kuma Ahaziya sarkin Yahuda ya je don yă gan shi.
So Jehu rode in a chariot to Jezreel; for Joram was resting there. Now Ahaziah king of Judah had come down to see Joram.
17 Mai tsaro kuwa yana tsaye a kan hasumiya a Yezireyel, sai ya hangi rundunar Yehu sa’ad da yake zuwa. Ya ce, “Na ga wata runduna.” Sai Yoram ya umarta, “Nemi mahayin doki a aike shi yă tarye su, yă kuma tambaye su, ‘Lafiya?’”
The watchman was standing on the tower in Jezreel, and he saw the company of Jehu as he came at a distance; he said, “I see a group of men coming.” Joram said, “Take a horseman, and send him out to meet them; tell him to say, 'Are you coming in peace?'”
18 Sai mahayin dokin ya hau, ya ruga, ya taryi Yehu, ya ce, “Ga abin da sarki ya ce, ‘Lafiya?’” Sai Yehu ya ce masa, “Ina ruwanka da zancen lafiya? Ka shiga layi.” Sai mai tsaron ya ce wa sarki, “Ɗan saƙon ya kai wurinsu, amma ba ya dawowa.”
So a man was sent on horseback to meet him; he said, “The king says this: 'Are coming in peace?'” So Jehu said, “What have you to do with peace? Turn and ride behind me.” Then the watchman told the king, “The messenger has met them, but he is not coming back.”
19 Saboda haka sarki ya sāke aika mahayin doki na biyu. Sa’ad da ya isa wurinsu sai ya ce, “Ga abin da sarki ya ce, ‘Lafiya?’” Yehu ya ce, “Ina ruwanka da zancen lafiya? Ka shiga layi.”
Then he sent out a second man on horseback, who came to them and said, “The king says this: 'Are you coming in peace?'” Jehu answered, “What have you to do with peace? Turn and ride behind me.”
20 Mai tsaro ya sāke cewa, “Ya kai wurinsu, amma shi ma ba ya dawowa. Ina ganin sukuwar kamar irin ta Yehu, jikan Nimshi, gama yakan yi sukuwa kamar mahaukaci.”
Again the watchman reported, “He has met them, but he is not coming back. For the way that the chariot is being driven is the way that Jehu son of Nimshi drives; he is driving wildly.”
21 Yoram ya umarta, “Haɗa mini keken yaƙi!” Da aka haɗa, sai Yoram sarkin Isra’ila, da Ahaziya sarkin Yahuda, suka hau suka tafi, kowa a keken yaƙinsa, don su taryi Yehu. Suka sadu da shi a filin da yake na Nabot mutumin Yezireyel.
So Joram said, “Get my chariot ready.” They prepared his chariot, and Joram king of Israel and Ahaziah king of Judah rode out, each in his chariot, to meet Jehu. They found him at the property of Naboth the Jezreelite.
22 Sa’ad da Yoram ya ga Yehu sai ya tambaye shi, “Lafiya kuwa ka zo, Yehu?” Yehu ya ce, “Ina kuwa lafiya, da yake dukan bautar gumaka da bokancin mahaifiyarka Yezebel sun bazu ko’ina?”
When Joram saw Jehu, he said, “Are you coming in peace, Jehu?” He answered, “What peace is there, when the idolatrous acts of prostitution and witchcraft of your mother Jezebel are so many?”
23 Yoram ya juya, ya gudu, yana ce wa Ahaziya, “Cin amana, Ahaziya!”
So Joram turned his chariot and fled and said to Ahaziah, “There is treachery, Ahaziah.”
24 Sai Yehu ya ja bakansa ya harbi Yoram a tsakanin kafaɗunsa. Kibiyar ta same shi a zuciyarsa sai ya fāɗi a cikin keken yaƙinsa.
Then Jehu drew his bow with his full strength and shot Joram between his shoulders; the arrow went through his heart, and he sank down in his chariot.
25 Yehu ya ce wa Bidkar, hafsan keken yaƙinsa, “Ka ɗauke shi ka jefar a filin da yake na Nabot mutumin Yezireyel. Ka tuna yadda ni da kai muke a kekunan yaƙi a bayan Ahab mahaifinsa sa’ad da Ubangiji ya yi wannan annabci game da shi,
Then Jehu said to Bidkar his captain, “Pick him up and throw him in the field of Naboth the Jezreelite. Think about how when you and I rode together after Ahab his father, Yahweh placed this prophecy against him:
26 ‘Jiya na ga jinin Nabot da jinin’ya’yansa, in ji Ubangiji, kuma ba shakka zan ɗauki fansa a wannan fili, in ji Ubangiji.’ Saboda haka, ka ɗauke shi ka jefar da shi a bisa wannan fegi, bisa ga faɗin Ubangiji. Saboda haka, ka ɗauke shi ka jefar a filin, in ji Ubangiji.”
'Yesterday I saw the blood of Naboth and the blood of his sons—declares Yahweh—and I will surely make you pay for it on this field—declares Yahweh. Now then, pick him up and throw him on this field, according to the word of Yahweh.”
27 Sa’ad da Ahaziya sarkin Yahuda ya ga abin da ya faru, sai ya haura hanyar Bet Haggan a guje. Yehu ya bi shi yana ihu, “A kashe shi, shi ma!” Suka ji masa rauni a keken yaƙinsa a hanya zuwa Gur, kusa da Ibileyam amma ya tsere zuwa Megiddo ya mutu a can.
When Ahaziah the king of Judah saw this, he fled up the road to Beth Haggan. But Jehu followed him, and said, “Kill him also in the chariot,” and they shot him at the ascent of Gur, which is by Ibleam. Ahaziah fled to Megiddo and died there.
28 Barorinsa suka ɗauke shi cikin keken yaƙi zuwa Urushalima suka binne shi a kabarinsa tare da kakanninsa a birnin Dawuda.
His servants carried his body in a chariot to Jerusalem and buried him in his tomb with his fathers in the city of David.
29 (A shekara ta goma sha ɗaya ta Yoram ɗan Ahab, Ahaziya ya zama sarkin Yahuda.)
Now it was in the eleventh year of Joram son of Ahab that Ahaziah had begun to reign over Judah.
30 Sa’an nan Yehu ya je Yezireyel. Sa’ad da Yezebel ta sami labari, sai ta sha kwalliya ta gyara gashin kanta, ta zauna tana kallo daga taga.
When Jehu came to Jezreel, Jezebel heard of it, and she painted her eyes, arranged her hair, and looked out the window.
31 Yayinda Yehu ya shiga ƙofa, sai ta ce, “Lafiya, kai Zimri, mai kashe maigidansa?”
As Jehu was entering the gate, she said to him, “Are you coming in peace, you Zimri, your master's murderer?”
32 Sai ya ɗaga ido ya dubi tagan ya ce, “Wa yake gefena? Wane ne?” Sai bābānni biyu ko uku suka leƙo suka dube shi.
Jehu looked up at the window and said, “Who is on my side? Who?” Then two or three eunuchs looked out.
33 Yehu ya ce musu, “Ku jefa ta ƙasa!” Sai suka jefar da ita, jininta ya fantsama a jikin bango da kuma a jikin dawakai yayinda suke tattaka ta.
So Jehu said, “Throw her down.” So they threw Jezebel down, and some of her blood spattered on the wall and the horses, and Jehu trampled her underfoot.
34 Yehu ya shiga ya ci, ya kuma sha. Ya ce, “Ku san yadda za ku yi da la’ananniyan nan, ku binne ta, gama’yar sarki ce.”
When Jehu entered the palace, he ate and drank. Then he said, “See now to this cursed woman and bury her, for she is a king's daughter.”
35 Amma sa’ad da suka je don su binne ta, ba su sami kome ba sai ƙoƙon kanta, ƙafafunta da kuma hannuwanta.
They went to bury her, but they found no more of her than the skull, the feet, and the palms of her hands.
36 Suka komo suka faɗa wa Yehu, wanda ya ce, “Wannan ita ce maganar da Ubangiji ya faɗa ta bakin bawansa Iliya mutumin Tishbe. A fili, a Yezireyel, karnuka za su cinye naman Yezebel.
So they came back and told Jehu. He said, “This is the word of Yahweh which he spoke by his servant Elijah the Tishbite, saying, 'In the land at Jezreel the dogs will eat the flesh of Jezebel,
37 Gawar Yezebel zai zama kamar juji a ƙasa, a fili, a Yezireyel, har ba wanda zai iya cewa, ‘Wannan Yezebel ce.’”
and the body of Jezebel will be like dung on the surface of the fields in the land at Jezreel, so that no one will be able to say, “This is Jezebel.”'”