< 2 Sarakuna 9 >
1 Sai Elisha ya kira wani daga cikin ƙungiyar annabawa, ya ce masa, “Ka sha ɗamara, ka ɗauki wannan kwalabar mai ka je Ramot Gileyad.
And Elisha the prophet he summoned one from [the] sons of the prophets and he said to him gird up loins your and take [the] flask of oil this in hand your and go Ramoth Gilead.
2 Da ka isa can, ka nemi Yehu ɗan Yehoshafat, ɗan Nimshi. Ka je wurinsa, ka ja shi gefe daga abokansa, ka shiga da shi ɗaki na ciki.
And you will go there towards and look for there Jehu [the] son of Jehoshaphat [the] son of Nimshi and you will go and you will make rise him from among brothers his and you will bring him a room in a room.
3 Sa’an nan ka ɗauki kwalabar man ka zuba a kansa, ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji ya faɗa, na naɗa ka sarkin Isra’ila.’ Sa’an nan ka buɗe ƙofa ka ruga a guje; kada ka ɓata lokaci!”
And you will take [the] flask of oil and you will pour [it] on head his and you will say thus he says Yahweh I anoint you to king to Israel and you will open the door and you will flee and not you must delay.
4 Sai saurayin nan, annabi, ya tafi Ramot Gileyad.
And he went the young man the young man the prophet Ramoth Gilead.
5 Da ya isa can, sai ya tarar da hafsoshin soji zaune a wuri guda. Sai ya ce, “Ina da saƙo dominka komanda.” Sai Yehu ya ce, “Wanne a cikinmu?” Sai ce, “Dominka, komanda.”
And he came and there! [the] commanders of the army [were] sitting and he said a word [belongs] to me to you O commander and he said Jehu to whom? from all of us and he said to you O commander.
6 Sai Yehu ya tashi ya shiga cikin gida. Sa’an nan annabin ya zuba wa Yehu mai a kā, ya ce, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Na naɗa ka sarki a bisa jama’ar Ubangiji, wato, Isra’ila.
And he arose and he went the house towards and he poured the oil to head his and he said to him thus he says Yahweh [the] God of Israel I anoint you to king to [the] people of Yahweh to Israel.
7 Za aka hallaka gidan Ahab maigidanka, zan kuma ɗauki fansar jinin bayina annabawa da kuma jinin dukan bayin Ubangiji da Yezebel ta zub da.
And you will strike down [the] house of Ahab master your and I will avenge [the] blood of - servants my the prophets and [the] blood of all [the] servants of Yahweh from [the] hand of Jezebel.
8 Dukan gidan Ahab zai hallaka. Zan kashe dukan’ya’yan Ahab maza a Isra’ila, bayi ko’yantattu.
And it will perish all [the] house of Ahab and I will cut off to Ahab [one who] urinates on a wall and shut up and freed in Israel.
9 Zan mai da gidan Ahab kamar gidan Yerobowam ɗan Nebat da kuma kamar gidan Ba’asha ɗan Ahiya.
And I will make [the] house of Ahab like [the] house of Jeroboam [the] son of Nebat and like [the] house of Baasha [the] son of Ahijah.
10 Game da Yezebel kuwa, karnuka za su cinye ta a fili a Yezireyel, ba kuwa wanda zai binne ta.’” Sa’an nan ya buɗe ƙofa ya ruga a guje.
And Jezebel they will devour the dogs in [the] territory of Jezreel and there not [will be one who] buries [her] and he opened the door and he fled.
11 Da Yehu ya koma wurin sauran hafsoshin sai ɗaya daga cikinsu ya tambaye shi, “Lafiya? Me ya kawo wannan mahaukaci a wurinka?” Sai Yehu ya ce, “Ka san mahaukacin nan da irin maganganunsa.”
And Jehu he went out to [the] servants of master his and someone said to him ¿ peace why? did he come the mad [man] this to you and he said to them you you know the man and talk his.
12 Suka ce masa, “Ba gaskiya ba ne, ka dai faɗa mana.” Yehu ya ce, “Ga abin da ya ce mini, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce, na naɗa ka sarki a bisa Isra’ila.’”
And they said falsehood tell please to us and he said like this and like this he said to me saying thus he says Yahweh I anoint you to king to Israel.
13 Sai suka yi sauri suka ɗauki rigunansu suka shimfiɗa a ƙasa, suka busa kakaki, suka yi ihu, suka ce, “Yehu ne sarki.”
And they hurried and they took each garment his and they put [them] under him to [the] bone of the steps and they gave a blast on the trumpet and they said he is king Jehu.
14 Saboda haka, Yehu ɗan Yehoshafat, ɗan Nimshi, ya ƙulla wa Yoram maƙarƙashiya (To, Yoram da dukan Isra’ila suna kāre Ramot Gileyad daga Hazayel sarkin Aram,
And he conspired Jehu [the] son of Jehoshaphat [the] son of Nimshi against Joram and Joram he had been watching at Ramoth Gilead he and all Israel from before Hazael [the] king of Aram.
15 amma Sarki Yoram ya koma Yezireyel don yă farfaɗo daga raunukan da Arameyawa suka ji masa a wata gabzawar da ya yi da Hazayel sarkin Aram.) Yehu ya ce, “In haka kuke ji, kada ku bar wani yă sulluɓe daga birnin yă kai labarin Yezireyel.”
And he had returned Jehoram the king to get himself healed in Jezreel from the wounds which they wounded him [the] Arameans when fought he with Hazael [the] king of Aram and he said Jehu if there [is] mind your may not he go out an escapee from the city to go (to tell *Q(k)*) in Jezreel.
16 Sai ya tashi ya ɗauki keken yaƙinsa ya tafi Yezireyel gama Yoram yana hutawa a can. Ga kuma Ahaziya sarkin Yahuda ya je don yă gan shi.
And he rode in a chariot Jehu and he went Jezreel towards for Joram [was] lying there and Ahaziah [the] king of Judah he had come down to see Joram.
17 Mai tsaro kuwa yana tsaye a kan hasumiya a Yezireyel, sai ya hangi rundunar Yehu sa’ad da yake zuwa. Ya ce, “Na ga wata runduna.” Sai Yoram ya umarta, “Nemi mahayin doki a aike shi yă tarye su, yă kuma tambaye su, ‘Lafiya?’”
And the watchman [was] standing on the tower in Jezreel and he saw [the] crowd of Jehu when came he and he said a crowd I [am] seeing and he said Jehoram take a horseman and send [him] to meet them and he may say ¿ peace.
18 Sai mahayin dokin ya hau, ya ruga, ya taryi Yehu, ya ce, “Ga abin da sarki ya ce, ‘Lafiya?’” Sai Yehu ya ce masa, “Ina ruwanka da zancen lafiya? Ka shiga layi.” Sai mai tsaron ya ce wa sarki, “Ɗan saƙon ya kai wurinsu, amma ba ya dawowa.”
And he went [the] rider of the horse to meet him and he said thus he says the king ¿ peace and he said Jehu what? [is] to you and to peace go around to after me and he reported the watchman saying he came the messenger to they and not he has turned back.
19 Saboda haka sarki ya sāke aika mahayin doki na biyu. Sa’ad da ya isa wurinsu sai ya ce, “Ga abin da sarki ya ce, ‘Lafiya?’” Yehu ya ce, “Ina ruwanka da zancen lafiya? Ka shiga layi.”
And he sent a rider of a horse second and he came to them and he said thus he says the king peace and he said Jehu what? [is] to you and to peace go around to after me.
20 Mai tsaro ya sāke cewa, “Ya kai wurinsu, amma shi ma ba ya dawowa. Ina ganin sukuwar kamar irin ta Yehu, jikan Nimshi, gama yakan yi sukuwa kamar mahaukaci.”
And he reported the watchman saying he came to to them and not he has turned back and the driving [is] like [the] driving of Jehu [the] son of Nimshi for with madness he drives.
21 Yoram ya umarta, “Haɗa mini keken yaƙi!” Da aka haɗa, sai Yoram sarkin Isra’ila, da Ahaziya sarkin Yahuda, suka hau suka tafi, kowa a keken yaƙinsa, don su taryi Yehu. Suka sadu da shi a filin da yake na Nabot mutumin Yezireyel.
And he said Jehoram harness and someone harnessed chariot his and he went out Jehoram [the] king of Israel and Ahaziah [the] king of Judah each in chariot his and they went out to meet Jehu and they found him in [the] portion of land of Naboth the Jezreelite.
22 Sa’ad da Yoram ya ga Yehu sai ya tambaye shi, “Lafiya kuwa ka zo, Yehu?” Yehu ya ce, “Ina kuwa lafiya, da yake dukan bautar gumaka da bokancin mahaifiyarka Yezebel sun bazu ko’ina?”
And it was when saw Jehoram Jehu and he said ¿ peace O Jehu and he said what? [is] peace until [the] prostitutions of Jezebel mother your and sorceries her many.
23 Yoram ya juya, ya gudu, yana ce wa Ahaziya, “Cin amana, Ahaziya!”
And he turned around Jehoram hands his and he fled and he said to Ahaziah treachery O Ahaziah.
24 Sai Yehu ya ja bakansa ya harbi Yoram a tsakanin kafaɗunsa. Kibiyar ta same shi a zuciyarsa sai ya fāɗi a cikin keken yaƙinsa.
And Jehu he filled hand his with bow and he struck Jehoram between arms his and it came out the arrow from heart his and he sank down in chariot his.
25 Yehu ya ce wa Bidkar, hafsan keken yaƙinsa, “Ka ɗauke shi ka jefar a filin da yake na Nabot mutumin Yezireyel. Ka tuna yadda ni da kai muke a kekunan yaƙi a bayan Ahab mahaifinsa sa’ad da Ubangiji ya yi wannan annabci game da shi,
And he said to Bidkar (officer his *Q(K)*) pick [him] up throw him in [the] portion of [the] field of Naboth the Jezreelite for remember I and you [were] riding pairs behind Ahab father his and Yahweh he lifted up on him the oracle this.
26 ‘Jiya na ga jinin Nabot da jinin’ya’yansa, in ji Ubangiji, kuma ba shakka zan ɗauki fansa a wannan fili, in ji Ubangiji.’ Saboda haka, ka ɗauke shi ka jefar da shi a bisa wannan fegi, bisa ga faɗin Ubangiji. Saboda haka, ka ɗauke shi ka jefar a filin, in ji Ubangiji.”
If not [the] blood of Naboth and [the] blood of sons his I saw yesterday [the] utterance of Yahweh and I will repay to you on the portion of land this [the] utterance of Yahweh and therefore pick [him] up throw him on the portion of land according to [the] word of Yahweh.
27 Sa’ad da Ahaziya sarkin Yahuda ya ga abin da ya faru, sai ya haura hanyar Bet Haggan a guje. Yehu ya bi shi yana ihu, “A kashe shi, shi ma!” Suka ji masa rauni a keken yaƙinsa a hanya zuwa Gur, kusa da Ibileyam amma ya tsere zuwa Megiddo ya mutu a can.
And Ahaziah [the] king of Judah he saw and he fled [the] direction Beth Haggan and he pursued after him Jehu and he said also him strike down him into the chariot at [the] ascent of Gur which [is] with Ibleam and he fled Megiddo and he died there.
28 Barorinsa suka ɗauke shi cikin keken yaƙi zuwa Urushalima suka binne shi a kabarinsa tare da kakanninsa a birnin Dawuda.
And they caused to ride him servants his Jerusalem towards and they buried him in grave his with ancestors his in [the] city of David.
29 (A shekara ta goma sha ɗaya ta Yoram ɗan Ahab, Ahaziya ya zama sarkin Yahuda.)
And in year one [plus] ten year of Joram [the] son of Ahab he had become king Ahaziah over Judah.
30 Sa’an nan Yehu ya je Yezireyel. Sa’ad da Yezebel ta sami labari, sai ta sha kwalliya ta gyara gashin kanta, ta zauna tana kallo daga taga.
And he went Jehu Jezreel towards and Jezebel she heard and she set with eye-paint eyes her and she made good head her and she looked down through the window.
31 Yayinda Yehu ya shiga ƙofa, sai ta ce, “Lafiya, kai Zimri, mai kashe maigidansa?”
And Jehu he came in the gate and she said ¿ peace O Zimri [the] murderer of master his.
32 Sai ya ɗaga ido ya dubi tagan ya ce, “Wa yake gefena? Wane ne?” Sai bābānni biyu ko uku suka leƙo suka dube shi.
And he lifted up face his to the window and he said who? [is] with me who? and they looked down to him two three court-officials.
33 Yehu ya ce musu, “Ku jefa ta ƙasa!” Sai suka jefar da ita, jininta ya fantsama a jikin bango da kuma a jikin dawakai yayinda suke tattaka ta.
And he said (let fall her *Q(K)*) and they let fall her and it spattered some of blood her to the wall and to the horses and he trampled her.
34 Yehu ya shiga ya ci, ya kuma sha. Ya ce, “Ku san yadda za ku yi da la’ananniyan nan, ku binne ta, gama’yar sarki ce.”
And he went and he ate and he drank and he said attend to please the accursed [woman] this and bury her for [was] a daughter of a king she.
35 Amma sa’ad da suka je don su binne ta, ba su sami kome ba sai ƙoƙon kanta, ƙafafunta da kuma hannuwanta.
And they went to bury her and not they found in her that except the skull and the feet and [the] palms of the hands.
36 Suka komo suka faɗa wa Yehu, wanda ya ce, “Wannan ita ce maganar da Ubangiji ya faɗa ta bakin bawansa Iliya mutumin Tishbe. A fili, a Yezireyel, karnuka za su cinye naman Yezebel.
And they returned and they told to him and he said [is] [the] word of Yahweh it which he spoke by [the] hand of servant his Elijah the Tishbite saying in [the] territory of Jezreel they will devour the dogs [the] flesh of Jezebel.
37 Gawar Yezebel zai zama kamar juji a ƙasa, a fili, a Yezireyel, har ba wanda zai iya cewa, ‘Wannan Yezebel ce.’”
(And it will be *Q(k)*) [the] corpse of Jezebel like dung on [the] surface of the field in [the] territory of Jezreel that not people will say this [is] Jezebel.