< 2 Sarakuna 9 >
1 Sai Elisha ya kira wani daga cikin ƙungiyar annabawa, ya ce masa, “Ka sha ɗamara, ka ɗauki wannan kwalabar mai ka je Ramot Gileyad.
And Eliseus the prophet called one of the sons of the prophets, slid said to him: Gird up thy loins, and take this little bottle of oil in thy hand, and go to Ramoth Galaad.
2 Da ka isa can, ka nemi Yehu ɗan Yehoshafat, ɗan Nimshi. Ka je wurinsa, ka ja shi gefe daga abokansa, ka shiga da shi ɗaki na ciki.
And when thou art come thither, thou shalt see Jehu the son of Josaphat the son of Namsi: and going in thou shalt make him rise up from amongst his brethren, and carry him into an inner chamber.
3 Sa’an nan ka ɗauki kwalabar man ka zuba a kansa, ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji ya faɗa, na naɗa ka sarkin Isra’ila.’ Sa’an nan ka buɗe ƙofa ka ruga a guje; kada ka ɓata lokaci!”
Then taking the little bottle of oil, thou shalt pour it on his head, and shalt say: Thus saith the Lord: I have anointed thee king over Israel. And thou shalt open the door and flee, and shalt not stay there.
4 Sai saurayin nan, annabi, ya tafi Ramot Gileyad.
So the young man, the servant of the prophet, went awry to Ramoth Galaad,
5 Da ya isa can, sai ya tarar da hafsoshin soji zaune a wuri guda. Sai ya ce, “Ina da saƙo dominka komanda.” Sai Yehu ya ce, “Wanne a cikinmu?” Sai ce, “Dominka, komanda.”
And went in thither: and behold the captains of the army were sitting: and he said: I have a word to thee, O prince. And Jehu said: Unto whom of us all? And he said: To thee, O prince.
6 Sai Yehu ya tashi ya shiga cikin gida. Sa’an nan annabin ya zuba wa Yehu mai a kā, ya ce, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Na naɗa ka sarki a bisa jama’ar Ubangiji, wato, Isra’ila.
And he arose, and went into the chamber: and he poured the oil upon his head, and said: Thus saith the Lord God of Israel: I have anointed thee king over Israel, the people of the Lord.
7 Za aka hallaka gidan Ahab maigidanka, zan kuma ɗauki fansar jinin bayina annabawa da kuma jinin dukan bayin Ubangiji da Yezebel ta zub da.
And thou shalt cut off the house of Achab thy master, and I will revenge the blood of my servants the prophets, and the blood of all the servants of the Lord at the hand of Jezabel.
8 Dukan gidan Ahab zai hallaka. Zan kashe dukan’ya’yan Ahab maza a Isra’ila, bayi ko’yantattu.
And I will destroy all the house of Achab, and I will cut off from Achab him that pisseth against the well, and him that is shut up, and the meanest in Israel.
9 Zan mai da gidan Ahab kamar gidan Yerobowam ɗan Nebat da kuma kamar gidan Ba’asha ɗan Ahiya.
And I will make the house of Achab like the house of Jeroboam the son of Nabat, and like the house of Baasa the son of Ahias.
10 Game da Yezebel kuwa, karnuka za su cinye ta a fili a Yezireyel, ba kuwa wanda zai binne ta.’” Sa’an nan ya buɗe ƙofa ya ruga a guje.
And the dogs shall eat Jezabel in the field of Jezrahel, and there shall be no one to bury her. And he opened the door and fled.
11 Da Yehu ya koma wurin sauran hafsoshin sai ɗaya daga cikinsu ya tambaye shi, “Lafiya? Me ya kawo wannan mahaukaci a wurinka?” Sai Yehu ya ce, “Ka san mahaukacin nan da irin maganganunsa.”
Then Jehu went forth to the servants of his lord: and they said to him: Are all things well? why came this mad man to thee? And he said to them: You know the man, and what he said.
12 Suka ce masa, “Ba gaskiya ba ne, ka dai faɗa mana.” Yehu ya ce, “Ga abin da ya ce mini, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce, na naɗa ka sarki a bisa Isra’ila.’”
But they answered: It is false, but rather do thou tell us. And he said to them: Thus and thus did he speak to me: and he said: Thus saith the Lord: I have anointed thee king over Israel.
13 Sai suka yi sauri suka ɗauki rigunansu suka shimfiɗa a ƙasa, suka busa kakaki, suka yi ihu, suka ce, “Yehu ne sarki.”
Then they made haste and taking every man his garment laid it under his feet, after the manner of a judgment seat, and they sounded the trumpet, and said: Jehu is king.
14 Saboda haka, Yehu ɗan Yehoshafat, ɗan Nimshi, ya ƙulla wa Yoram maƙarƙashiya (To, Yoram da dukan Isra’ila suna kāre Ramot Gileyad daga Hazayel sarkin Aram,
So Jehu the son of Josaphat the son of Namsi conspired against Joram. Now Joram had besieged Ramoth Galaad, he and all Israel fighting with Hazael king of Syria:
15 amma Sarki Yoram ya koma Yezireyel don yă farfaɗo daga raunukan da Arameyawa suka ji masa a wata gabzawar da ya yi da Hazayel sarkin Aram.) Yehu ya ce, “In haka kuke ji, kada ku bar wani yă sulluɓe daga birnin yă kai labarin Yezireyel.”
And was returned to be healed in Jezrahel of his wounds, for the Syrians had wounded him, when he fought with Hazael king of Syria. And Jehu said: If it please you, let no mall go forth or flee out of the city, lest he go, and tell in Jezrahel.
16 Sai ya tashi ya ɗauki keken yaƙinsa ya tafi Yezireyel gama Yoram yana hutawa a can. Ga kuma Ahaziya sarkin Yahuda ya je don yă gan shi.
And he got up, and went into Jezrahel: for Joram was sick there, and Ochozias king of Juda was come down to visit Joram.
17 Mai tsaro kuwa yana tsaye a kan hasumiya a Yezireyel, sai ya hangi rundunar Yehu sa’ad da yake zuwa. Ya ce, “Na ga wata runduna.” Sai Yoram ya umarta, “Nemi mahayin doki a aike shi yă tarye su, yă kuma tambaye su, ‘Lafiya?’”
The watchmen therefore, that stood upon the tower of Jezrahel, saw the troop of Jehu coming, and said: I see a troop. And Joram said: Take a chariot, and send to meet them, and let him that goeth say: Is all well?
18 Sai mahayin dokin ya hau, ya ruga, ya taryi Yehu, ya ce, “Ga abin da sarki ya ce, ‘Lafiya?’” Sai Yehu ya ce masa, “Ina ruwanka da zancen lafiya? Ka shiga layi.” Sai mai tsaron ya ce wa sarki, “Ɗan saƙon ya kai wurinsu, amma ba ya dawowa.”
So there went one in a chariot to meet him, and said: Thus saith the king: Are all things peaceable? And Jehu said: What hast thou to do with peace? go behind and follow me. And the watchman told, saying: The messenger came to them, but he returneth not.
19 Saboda haka sarki ya sāke aika mahayin doki na biyu. Sa’ad da ya isa wurinsu sai ya ce, “Ga abin da sarki ya ce, ‘Lafiya?’” Yehu ya ce, “Ina ruwanka da zancen lafiya? Ka shiga layi.”
And he sent a second chariot of horses: and he came to them, and said: Thus saith the king: Is there peace? And Jehu said: What hast thou to do with peace? pass, and follow me.
20 Mai tsaro ya sāke cewa, “Ya kai wurinsu, amma shi ma ba ya dawowa. Ina ganin sukuwar kamar irin ta Yehu, jikan Nimshi, gama yakan yi sukuwa kamar mahaukaci.”
And the watchman told, saying: He came even to them, but returneth not: and the driving is like the driving of Jehu the son of Namsi, for he drives furiously.
21 Yoram ya umarta, “Haɗa mini keken yaƙi!” Da aka haɗa, sai Yoram sarkin Isra’ila, da Ahaziya sarkin Yahuda, suka hau suka tafi, kowa a keken yaƙinsa, don su taryi Yehu. Suka sadu da shi a filin da yake na Nabot mutumin Yezireyel.
And Joram said: Make ready the chariot. And they made ready his chariot, and Joram king of Israel, and Ochozias king of Juda went out, each in his chariot, and they went out to meet Jehu, and met him in the field of Naboth the Jezrahelite.
22 Sa’ad da Yoram ya ga Yehu sai ya tambaye shi, “Lafiya kuwa ka zo, Yehu?” Yehu ya ce, “Ina kuwa lafiya, da yake dukan bautar gumaka da bokancin mahaifiyarka Yezebel sun bazu ko’ina?”
And when Joram saw Jehu, he said: Is there peace, Jehu? And he answered: What peace? so long as the fornications of Jezabel thy mother, and her many sorceries are in their vigour.
23 Yoram ya juya, ya gudu, yana ce wa Ahaziya, “Cin amana, Ahaziya!”
And Joram turned his hand, and fleeing, said to Ochozias: There is treachery, Ochozias.
24 Sai Yehu ya ja bakansa ya harbi Yoram a tsakanin kafaɗunsa. Kibiyar ta same shi a zuciyarsa sai ya fāɗi a cikin keken yaƙinsa.
But Jehu bent Iris bow with his hand, and shot Joram between the shoulders: and the arrow went out through his heart, and immediately he fell in his chariot.
25 Yehu ya ce wa Bidkar, hafsan keken yaƙinsa, “Ka ɗauke shi ka jefar a filin da yake na Nabot mutumin Yezireyel. Ka tuna yadda ni da kai muke a kekunan yaƙi a bayan Ahab mahaifinsa sa’ad da Ubangiji ya yi wannan annabci game da shi,
And Jehu said to Badacer his captain: Take him, and cast him into the field of Naboth the Jezrahelite: for I remember when I and thou sitting in a chariot followed Achab this man’s father, that the Lord laid this burden upon him, saying:
26 ‘Jiya na ga jinin Nabot da jinin’ya’yansa, in ji Ubangiji, kuma ba shakka zan ɗauki fansa a wannan fili, in ji Ubangiji.’ Saboda haka, ka ɗauke shi ka jefar da shi a bisa wannan fegi, bisa ga faɗin Ubangiji. Saboda haka, ka ɗauke shi ka jefar a filin, in ji Ubangiji.”
If I do not requite thee in this field, saith the Lord, for the blood of Naboth, and for the blood of his children, which I saw yesterday, saith the Lord. So now take him, and cast him into the field, according to the word of the Lord.
27 Sa’ad da Ahaziya sarkin Yahuda ya ga abin da ya faru, sai ya haura hanyar Bet Haggan a guje. Yehu ya bi shi yana ihu, “A kashe shi, shi ma!” Suka ji masa rauni a keken yaƙinsa a hanya zuwa Gur, kusa da Ibileyam amma ya tsere zuwa Megiddo ya mutu a can.
But Ochozias king of Juda seeing this, fled by the way of the garden house: and Jehu pursued him, and said: Strike him also in his chariot. And they struck him in the going up to Gaver, which is by Jeblaam: and he fled into Mageddo, and died there.
28 Barorinsa suka ɗauke shi cikin keken yaƙi zuwa Urushalima suka binne shi a kabarinsa tare da kakanninsa a birnin Dawuda.
And his servants laid him upon his chariot, and carried him to Jerusalem: and they buried him in his sepulchre with his fathers in the city of David.
29 (A shekara ta goma sha ɗaya ta Yoram ɗan Ahab, Ahaziya ya zama sarkin Yahuda.)
In the eleventh year of Joram the son of Achab, Ochozias reigned over Juda,
30 Sa’an nan Yehu ya je Yezireyel. Sa’ad da Yezebel ta sami labari, sai ta sha kwalliya ta gyara gashin kanta, ta zauna tana kallo daga taga.
And Jehu came into Jezrahel. But Jezabel hearing of his coming in, painted her face with stibic stone, and adorned her head, and looked out of a window
31 Yayinda Yehu ya shiga ƙofa, sai ta ce, “Lafiya, kai Zimri, mai kashe maigidansa?”
At Jehu coming in at the gate, and said: Can there be peace for Zambri, that hath killed his master?
32 Sai ya ɗaga ido ya dubi tagan ya ce, “Wa yake gefena? Wane ne?” Sai bābānni biyu ko uku suka leƙo suka dube shi.
And Jehu lifted up his face to the window, and said: Who is this? And two or three eunuchs bowed down to him.
33 Yehu ya ce musu, “Ku jefa ta ƙasa!” Sai suka jefar da ita, jininta ya fantsama a jikin bango da kuma a jikin dawakai yayinda suke tattaka ta.
And he said to them: Throw her down headlong: and they threw her down, and the wall was sprinkled with her blood, and the hoofs of the horses trod upon her.
34 Yehu ya shiga ya ci, ya kuma sha. Ya ce, “Ku san yadda za ku yi da la’ananniyan nan, ku binne ta, gama’yar sarki ce.”
And when he was come in, to eat, and to drink, he said: Go, and see after that cursed woman, and bury her: because she is a king’s daughter.
35 Amma sa’ad da suka je don su binne ta, ba su sami kome ba sai ƙoƙon kanta, ƙafafunta da kuma hannuwanta.
And when they went to bury her, they found nothing but the skull, and the feet, and the extremities of her hands.
36 Suka komo suka faɗa wa Yehu, wanda ya ce, “Wannan ita ce maganar da Ubangiji ya faɗa ta bakin bawansa Iliya mutumin Tishbe. A fili, a Yezireyel, karnuka za su cinye naman Yezebel.
And coming back they told him. And Jehu said: It is the word of the Lord, which he spoke by his servant Elias the Thesbite, saying: In the field of Jezrahel the dogs shall eat the flesh of Jezabel,
37 Gawar Yezebel zai zama kamar juji a ƙasa, a fili, a Yezireyel, har ba wanda zai iya cewa, ‘Wannan Yezebel ce.’”
And the flesh of Jezabel shall be as dung upon the face of the earth in the field of Jezrahel, so that they who pass by shall say: Is this that same Jezabel?