< 2 Sarakuna 8 >

1 To, Elisha ya riga ya ce wa matan da ya tā da ɗanta daga matattu, “Ki kwashe iyalinki ku tafi duk inda za ku tafi na ɗan lokaci, domin Ubangiji ya sa a yi yunwa na shekara bakwai a ƙasar.”
I govori Jelisije ženi kojoj sina povrati u život, i reèe: ustani i idi s domom svojim, i skloni se gdje možeš; jer je Gospod dozvao glad koja æe doæi i biti na zemlji sedam godina.
2 Sai macen ta yi kamar yadda mutumin Allah ya faɗa. Ita da iyalinta suka tafi ƙasar Filistiyawa suka zauna shekara bakwai.
A žena usta, i uèini kako reèe èovjek Božji, jer otide s domom svojim i osta u zemlji Filistejskoj sedam godina.
3 A ƙarshen shekara bakwai ɗin sai ta dawo daga ƙasar Filistiyawa, ta kuma tafi wajen sarki ta roƙa a mayar mata da gidanta da filinta.
A kad proðe sedam godina, vrati se žena iz zemlje Filistejske, i otide da moli cara za kuæu svoju i za njivu svoju.
4 Sarki kuwa yana magana da Gehazi bawan mutumin Allah, ya ce masa, “Ba ni labarin dukan abubuwan banmamakin da Elisha ya yi.”
A car govoraše s Gijezijem, momkom èovjeka Božijega, i reèe: pripovjedi mi sva velika djela koja je uèinio Jelisije.
5 A sa’ad da Gehazi yana cikin ba shi labarin yadda Elisha ya tā da matacce ke nan, sai ga macen da aka tā da ɗanta daga matattu ta shigo don tă roƙi sarki yă mayar mata da gidanta da filinta. Gehazi ya ce, “Ranka yă daɗe, ai, ga macen, ga kuma ɗan da Elisha ya tā da daga matattu.”
A kad on pripovjedaše caru kako je mrtva oživio, gle, žena, kojoj je sina oživio, stade moliti cara za kuæu svoju i za njivu svoju. A Gijezije reèe: gospodaru moj, care, ovo je ona žena i ovo je sin njezin, kojega je Jelisije oživio.
6 Sarki ya tambayi macen game da al’amarin, ita kuwa ta faɗa masa. Sa’an nan ya sa wani hafsa yă dubi damuwarta ya kuma ce masa, “Ka mayar mata kome da yake nata, haɗe da dukan kuɗin da aka samo daga filin, daga ranar da ta bar ƙasar har yă zuwa yanzu.”
Tada car zapita ženu, i ona mu pripovjedi. I car joj dade jednoga dvoranina i reèe mu: povrati joj sve što je njezino i sve prihode od njiva od dana kad je ostavila zemlju dori do sada.
7 Sai Elisha ya tafi Damaskus, Ben-Hadad mutumin Aram kuwa yana ciwo. Sa’ad da aka faɗa wa sarki, “Mutumin Allah ya hauro tun daga can zuwa nan,”
Poslije toga doðe Jelisije u Damasak, a car Sirski Ven-Adad bijaše bolestan, i javiše mu govoreæi: došao je èovjek Božji ovamo.
8 sai ya ce wa Hazayel, “Ɗauki wannan tare da kai ka tafi ka taryi mutumin Allah. Ka nemi nufin Ubangiji ta wurinsa; ka tambaye shi, ‘Zan warke daga ciwon nan?’”
A car reèe Azailu: uzmi sa sobom dar i idi na susret èovjeku Božijemu, i preko njega pitaj Gospoda hoæu li ozdraviti od ove bolesti.
9 Sai Hazayel ya tafi taryen Elisha, ya ɗauka kyauta na kowane irin kaya masu kyau na Damaskus tare da shi a raƙuma arba’in. Ya shiga ya tsaya a gaban Elisha ya ce, “Ɗanka Ben-Hadad na Aram ya aike ni in tambaye ka, ‘Zan warke daga ciwon nan?’”
Tada otide Azailo na susret njemu ponesavši dar, svakojakih dobrijeh stvari iz Damaska natovarenijeh na èetrdeset kamila; i došav stade pred njim i reèe: sin tvoj Ven-Adad car Sirski posla me k tebi govoreæi: hoæu li ozdraviti od ove bolesti?
10 Elisha ya amsa ya ce, “Je ka ce masa, ‘Ba shakka za ka warke’; ammaUbangiji ya nuna mini cewa ba shakka zai mutu.”
A Jelisije mu reèe: idi, reci mu: ozdraviæeš; ali mi je Gospod pokazao da æe umrijeti.
11 Sai ya zuba wa Hazayel ido har sai da Hazayel ya ji kunya. Sa’an nan mutumin Allah ya fara kuka.
I uprvši oèi u nj gledaše dugo i zaplaka se èovjek Božji.
12 Hazayel ya ce masa, “Me ya sa ranka yă daɗe yake kuka?” Elisha ya amsa, “Domin na san illar da za ka yi wa Isra’ilawa. Za ka ƙona biranensu masu katanga, ka karkashe majiya ƙarfinsu da takobi, ka fyaffyaɗe ƙananan yaransu da ƙasa, ka tsattsage matansu masu ciki.”
A Azailo mu reèe: što plaèe gospodar moj? A on reèe: jer znam kakvo æeš zlo uèiniti sinovima Izrailjevijem, gradove æeš njihove paliti ognjem, i mladiæe æeš njihove sjeæi maèem, i djecu æeš njihovu razbijati i trudne žene njihove rastrzati.
13 Hazayel ya ce, “Yaya bawanka, wanda yake kare kawai, zai iya aikata wannan irin abu?” Elisha ya ce, “Ubangiji ya nuna mini cewa za ka zama sarkin Aram.”
A Azailo reèe: a šta je sluga tvoj, pas, da uèini tako veliku stvar? A Jelisije mu reèe: pokazao mi je Gospod da æeš ti biti car u Siriji.
14 Sai Hazayel ya rabu da Elisha ya koma wurin maigidansa. Da Ben-Hadad ya yi tambaya, “Me Elisha ya ce maka?” Sai Hazayel ya amsa, “Ya faɗa mini cewa tabbatacce za ka warke.”
Tada otišav od Jelisija doðe ka gospodaru svojemu; a on mu reèe: što ti reèe Jelisije? A on odgovori: reèe mi da æeš ozdraviti.
15 Amma kashegari sai ya ɗauki tsumma mai kauri, ya jiƙa shi, ya rufe fuskar sarki da shi, har sai da sarki ya mutu. Sai Hazayel ya gāje shi a matsayin sarki.
Ali sjutradan uze Azailo pokrivaè i zamoèivši ga u vodu prostrije mu po licu, te umrije. A na njegovo mjesto zacari se Azailo.
16 A shekara ta biyar ta mulkin Yoram ɗan Ahab, sarkin Isra’ila, sa’ad da Yehoshafat yake sarautar Yahuda, Yoram ɗan Yehoshafat, ya fara mulkinsa a matsayin sarkin Yahuda.
Pete godine carovanja Jorama sina Ahavova nad Izrailjem, kad Josafat bješe car Judin, poèe carovati Joram sin Josafatov car Judin.
17 Yana da shekara talatin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki na tsawon shekara takwas a Urushalima.
Imaše trideset i dvije godine kad poèe carovati, i carova osam godina u Jerusalimu.
18 Ya bi gurbin sarakunan Isra’ila, yadda gidan Ahab ta yi, gama ya auri’yar Ahab. Ya yi mugunta a gaban Ubangiji.
I hoðaše putem careva Izrailjevijeh, kao što je èinio dom Ahavov; jer kæi Ahavova bješe mu žena, te on èinjaše što je zlo pred Gospodom.
19 Duk da haka, saboda bawansa Dawuda, Ubangiji bai ragargaza Yahuda ba. Ya riga ya yi alkawari zai bar wa Dawuda magāji har abada.
Ali Gospod ne htje zatrti Jude radi Davida sluge svojega, kao što mu bješe rekao da æe mu dati vidjelo izmeðu sinova njegovijeh dovijeka.
20 A kwanakin Yoram, Edom ta yi wa Yahuda tawaye, ta naɗa wa kanta sarki.
Za njegova vremena odvrže se Edom da ne bude pod Judom, i postavi cara nad sobom.
21 Saboda haka Yehoram ya tafi Zayir da dukan kekunan yaƙinsa. Sojojin Edom suka kewaye shi a can, amma da dare sai Yoram ya ɓarke ya gudu, sojojinsa kuma suka watse zuwa gidajensu.
Zato otide Joram u Sair i sva kola njegova s njim; i usta noæu i udari na Edomce, koji ga bijahu opkolili, i na zapovjednike od kola, i pobježe narod u svoje šatore.
22 Har yă zuwa yau, Edom tana yi wa Yahuda tawaye. A lokaci ɗaya ne Libna ma ta yi tawaye.
Ipak se odvrgoše Edomci da ne budu pod Judom, do današnjega dana. U isto vrijeme odmetnu se i Livna.
23 Game da waɗansu abubuwan da suka faru a zamanin Yoram, ba suna a rubuce a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda ba?
A ostala djela Joramova i sve što je èinio, nije li to zapisano u dnevniku careva Judinijeh?
24 Yoram ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a birnin Dawuda. Sai Ahaziya ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
I Joram poèinu kod otaca svojih, i bi pogreben kod otaca svojih u gradu Davidovu. A na njegovo se mjesto zacari sin njegov Ohozija.
25 A shekara ta goma sha biyu ta Yoram ɗan Ahab, sarkin Isra’ila, Ahaziya ɗan Yehoram, sarkin Yahuda ya fara mulki.
Godine dvanaeste carovanja Jorama sina Ahavova nad Izrailjem poèe carovati Ohozija sin Joramov, car Judin.
26 Ahaziya yana da shekara ashirin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara ɗaya. Sunan mahaifiyarsa Ataliya, jikanyar Omri, sarkin Isra’ila.
Imaše Ohozija dvadeset i dvije godine kad se zacari, i carova godinu dana u Jerusalimu. Materi mu bješe ime Gotolija, kæi Amrija cara Izrailjeva.
27 Ya bi gurbin gidan Ahab, ya yi mugunta a gaban Ubangiji yadda gida Ahab ta yi, gama yana da dangantaka ta aure da gidan Ahab.
On hoðaše putem doma Ahavova, i èinjaše što je zlo pred Gospodom, kao dom Ahavov, jer bješe zet domu Ahavovu.
28 Ahaziya ya tafi tare da Yoram ɗan Ahab don su yaƙi Hazayel sarkin Aram a Ramot Gileyad. Arameyawa suka yi wa Yoram rauni;
Zato poðe s Joramom sinom Ahavovijem na vojsku na Azaila cara Sirskoga u Ramot Galadski; ali Sirci razbiše Jorama.
29 saboda haka Sarki Yoram ya koma zuwa Yezireyel don yă yi jinyar raunin da Arameyawa suka ji masa a Rama a yaƙinsa da Hazayel sarkin Aram. Sai Ahaziya ɗan Yehoram, sarkin Yahuda ya gangara zuwa Yezireyel yă dubi Yoram ɗan Ahab domin an yi masa rauni.
I vrati se car Joram da se lijeèi u Jezraelu od rana koje mu zadaše Sirci u Rami, kad se bijaše s Azailom carem Sirskim; a Ohozija sin Joramov car Judin otide da vidi Jorama sina Ahavova u Jezraelu, jer bijaše bolestan.

< 2 Sarakuna 8 >