< 2 Sarakuna 7 >

1 Sai Elisha ya ce, “Ku ji maganar Ubangiji. Ga abin da Ubangiji ya ce, gobe war haka, za a sayar da mudun gari mai laushi a farashin shekel guda, mudu biyu na sha’ir kuma a shekel ɗaya a ƙofar birnin Samariya.”
Elisha replied to the king, “Listen to what Yahweh says: ‘He says that by this time tomorrow, at the marketplace here in Samaria, you will be able to buy (ten pounds/five kg.) of fine wheat or (20 pounds/ten kg.) of barley for [only] one piece of silver.’”
2 Sai wani hafsa mataimakin sarki ya ce wa mutumin Allah, “Kai, ko da Ubangiji zai buɗe tagogin sama, wannan abu ba zai yiwu ba!” Sai Elisha ya ce, “Za ka gani da idanunka, zai faru, amma ba za ka ci ba!”
The king’s officer said to Elijah, “That cannot happen! Even if Yahweh himself would open the windows of the sky [and send grain down to us], that certainly could not [RHQ] happen!” Elisha replied, “[Because you said that, ] you [SYN] will see it happen, but you will not be able to eat any of the food!”
3 To, akwai waɗansu kutare huɗu a ƙofar gari. Suka ce wa junansu, “Don me za mu zauna a nan sai mun mutu?
That day there were four men who had (leprosy/a dreaded skin disease) who were sitting outside the gate of Samaria [city. They said to each other, “(Why should we] wait here until we die?/[It is ridiculous for us to] wait here until we die.) [RHQ]
4 In muka ce, ‘Za mu shiga cikin birni’ yunwa tana can, za mu kuwa mutu. Idan kuwa muka zauna a nan, za mu mutu. Saboda haka, bari mu ƙetare zuwa sansanin Arameyawa mu miƙa kai. Idan suka bar mu da rai, to; idan kuwa suka kashe mu, shi ke nan.”
If we go into the city, we will die there, because there is no food there. If we remain sitting here, we will die here. So let’s go to where the army of Syria has set up their tents. If they kill us, we will die. But if they allow us to remain alive, we will not die.”
5 Da yamma sai suka tashi suka tafi sansanin Arameyawa. Yayinda suka shiga tsakiyar sansanin Arameyawa kuwa, sai suka tarar ba kowa a can,
So when it was getting dark, those four men went to the camp where the army of Syria had set up their tents. But when they reached the camp, they saw that there was no one there!
6 gama Ubangiji ya sa rundunar Arameyawa suka ji motsin kekunan yaƙi, da motsin dawakai, da na babban rundunar sojoji, saboda haka suka ce wa juna; “Duba, sarkin Isra’ila ya ɗauka hayar sarakuna Hittiyawa da sarakunan Masarawa don su yaƙe mu!”
What had happened was that Yahweh had caused the army of Syria to hear something that sounded like a large army marching with chariots and horses. So they said to each other, “Listen! The king of Israel has hired the kings of Egypt and the Heth people-group [and their armies], and they have come to attack us!”
7 Saboda haka suka tashi, suka gudu da yamma, suka bar tentunansu, da dawakansu, da jakunansu. Suka bar sansanin yadda yake, suka gudu don su ceci rayukansu.
So they all ran away that evening and left their tents and their horses and donkeys there, because [they were afraid that] they would be killed [if they stayed there].
8 Da kutaren nan suka kai bakin sansanin, sai suka shiga wani tenti, suka ci, suka sha, suka kwashi azurfa, da zinariya, da riguna, suka tafi, suka ɓoye su. Sa’an nan suka koma, suka shiga wani tenti, sai suka kwashi kaya daga ciki, suka kuma ɓoye su.
When those four lepers came to the edge of the area where the soldiers of Syria had set up their tents, they went into one tent, [and saw all the things that had been left there]. So they ate and drank what was there, and they took the silver and the gold and clothes. Then they went [outside the tent] and hid those things. Then they entered another tent, and took things from there, and then went outside and hid them, also.
9 Sa’an nan suka ce wa juna, “Ba mu yi abin kirki ba. Wannan rana ce ta albishiri amma muka yi shiru; in kuwa mun bari har gari ya waye, to, fa, wata masifa za tă fāɗo mana. Bari mu tafi nan take mu faɗa a fadan sarki.”
But then they said to each other, “We are not doing what is right. We have good news [to tell others] today. If we do not tell it to anyone now, and if we wait until morning to tell it, we will certainly be punished [by Yahweh]. So let’s go right now to the palace and tell it to the king’s officials!”
10 Saboda haka suka je suka kira masu tsaron ƙofar birni, suka ce musu, “Mun je sansanin Arameyawa, ga shi kuwa ba mu iske kowa a can ba, babu ko motsin wani, sai dai dawakai da jakuna a daure, tentunan kuwa suna nan yadda suke.”
So they went to the guards at the city gates and called out to them, “We went to where the army of Syria had set up their tents, but we did not see or hear anyone there. Their horses and donkeys were still tied up, but their tents were all deserted/abandoned!”
11 Sai matsaran ƙofar suka sanar da labarin a cikin fada.
The guards shouted the news, and some people [who heard it] went to the palace and reported it there.
12 Sai sarki ya tashi da daren nan ya ce wa hafsoshinsa, “Na san abin da Arameyawan suke shiri! Sun san game da yunwar da muke ciki a nan, domin haka sun bar sansaninsu suka shiga jeji suka ɓuya, suna nufin sa’ad da muka fita daga birni, sai su kama mu da rai, sa’an nan su shiga birnin.”
[When] the king [heard it, he] got up out of his bed and said to his officials, “I will tell you what the army of Syria is planning to do. They know that we have no food here, so they have left their tents and are hiding in the fields. They think that we will leave the city [to find some food], and then they will capture us and capture the city.”
13 Ɗaya daga cikin fadawan sarki ya ce, “A sa waɗansu mutane su ɗauki dawakai biyar da suka ragu cikin birni, idan ba su tsira ba, za su zama kamar sauran Isra’ilawan da suka riga suka mutu ne. Bari mu aika, mu gani.”
But one of his officials said, “Many of our Israeli people have already died [from (hunger/not having anything to eat]). If those of us who are still alive all stay here, we also will die anyway. So let’s send some men with five of our horses that are still alive to go and see [what has really happened].”
14 Saboda haka suka zaɓi kekunan yaƙi biyu tare da dawakansu, sarki kuwa ya aike su su bi bayan sojojin Arameyawa. Ya umarci masu tuƙinsu ya ce, “Ku je ku bincika abin da ya faru.”
So they chose some men and told them to go in a chariot and find out what had happened to the army of Syria.
15 Suka bi sawunsu har Urdun, suka ga tufafi da makamai barjat ko’ina a hanya waɗanda Arameyawa suka zubar yayinda suke gudu. Sai’yan aika suka dawo suka ba wa sarki labari.
They went as far as the Jordan [River]. All along the road they saw clothes and equipment that the soldiers from Syria had thrown away while they were running away very quickly. So the men returned to the king and reported [what they had seen].
16 Sa’an nan jama’a suka fita suka kwashi ganima a sansanin Arameyawa. Aka kuwa sayar da gari mai laushi a farashin shekel guda, mudu biyu na sha’ir kuma a shekel guda, yadda Ubangiji ya faɗi.
Then many of the people of Samaria also went [out of the city and went] to where the army of Syria had previously set up their tents. They entered all the tents and took everything. [So there was now plenty of everything!] As a result people could buy ten pounds of fine wheat or 20 pounds of barley for only one piece of silver, which was what Yahweh had said would happen!
17 Sai ya kasance cewa Sarki ya sa dogari wanda ya raka shi wajen Elisha ya tsare ƙofar birnin. Sai mutane suka tattake shi a ƙofar har ya mutu, kamar yadda annabi Elisha ya faɗa sa’ad da sarki ya tafi wurinsa.
The king of Israel had appointed the officer who was his assistant to supervise what was happening at the marketplace. But as he was standing near the gate, all the people [who were rushing outside the city] trampled on him, and he died, which was what Elisha had said would happen to him when Elisha previously went to talk to the king.
18 Haka kuwa ya kasance kamar yadda mutumin Allah ya ce wa sarki, “Gobe war haka, za a sayar da mudun gari shekel guda, mudun sha’ir biyu ma a shekel guda, a ƙofar Samariya.”
Elisha had told him that by the next day there would be plenty of food, with the result that anyone could buy ten pounds of fine wheat or 20 pounds of barley for only one piece of silver.
19 Hafsan ya riga ya ce wa mutumin Allah, “Kai, ko da Ubangiji zai buɗe tagogin sama, wannan abu ba zai yiwu ba!” Mutumin Allah kuwa ya faɗa masa, “Za ka gani da idanunka sai dai ba za ka ci ba!”
And the officer had answered, “That certainly cannot [RHQ] happen! Even if Yahweh himself would open the sky and send down some grain, that could not happen.” And Elisha had replied, “[Because you said that, ] you [SYN] will see it happen, but you will not be able to eat any of the food!”
20 Haka kuwa ya kasance, gama mutane sun tattake shi a hanyar shiga, har ya mutu.
And that is what happened to him. The people [who were rushing out of] the city gate trampled on him, and he died.

< 2 Sarakuna 7 >