< 2 Sarakuna 6 >

1 Sai ƙungiyar annabawa suka ce wa Elisha, “Duba, wurin da muke taruwa ya kāsa mana.
Et les fils des prophètes dirent à Élisée: Tu vois que le lieu où nous habitons devant toi est trop étroit pour nous.
2 Bari mu je Urdun, inda kowannenmu zai saro itace; mu gina inda za mu zauna.” Sai ya ce musu, “Ku je.”
Allons, s’il te plaît, jusqu’au Jourdain, et nous y prendrons chacun une pièce de bois, et nous y bâtirons un lieu pour y habiter. Et il dit: Allez.
3 Sai ɗayansu ya ce, “Ba za ka zo tare da bayinka ba?” Sai Elisha ya ce “Zan zo.”
Et l’un d’eux dit: Consens, je te prie, à venir avec tes serviteurs. Et il dit: J’irai.
4 Ya kuma tafi tare da su. Suka tafi Urdun suka fara saran itatuwa.
Et il alla avec eux; et ils vinrent au Jourdain, et coupèrent des arbres.
5 Yayinda ɗayansu yake cikin saran itace, sai kan gatarin ya fāɗi a ruwa, sai ya ce, “Kash, ranka yă daɗe, kayan aro ne fa!”
Et il arriva, comme l’un d’eux abattait une pièce de bois, que le fer tomba dans l’eau; et il s’écria et dit: Hélas, mon maître! il était emprunté!
6 Sai mutumin Allah ya ce, “Daidai ina ya fāɗa?” Da ya nuna masa wurin, sai Elisha ya yanka ɗan sanda ya jefa a wurin, ya sa kan gatarin ya taso sama.
Et l’homme de Dieu dit: Où est-il tombé? Et il lui montra l’endroit; et [Élisée] coupa un morceau de bois, et l’y jeta, et fit surnager le fer;
7 Sai ya ce masa, “Ka ɗauko.” Sai mutumin ya miƙa hannu ya ɗauka.
et il dit: Enlève-le. Et il étendit sa main, et le prit.
8 To, fa, sarkin Aram yana yaƙi da Isra’ila. Bayan ya tattauna da hafsoshinsa, sai ya ce, “Zan kafa sansanina a wurin kaza da kaza.”
Or le roi de Syrie faisait la guerre contre Israël; et il tint conseil avec ses serviteurs, disant: En tel et tel lieu sera mon camp.
9 Sai mutumin Allah ya aika wa sarkin Isra’ila cewa, “Ka yi hankali da wuce wuri kaza, domin Arameyawa za su gangara can.”
Et l’homme de Dieu envoya au roi d’Israël, disant: Garde-toi de passer par ce lieu-là; car les Syriens y sont descendus.
10 Saboda haka sarkin Isra’ila ya lura da inda mutumin Allah ya ambata. Sau da sau Elisha yakan yi wa sarki kashedi, don haka ya riƙa taka yi tsantsan a wuraren nan.
Et le roi d’Israël envoya au lieu au sujet duquel l’homme de Dieu lui avait parlé et l’avait averti, et il y fut gardé. [Cela eut lieu] non pas une fois, ni deux fois.
11 Wannan ya husata sarkin Aram. Ya kira hafsoshinsa ya tambaye su ya ce, “Ku faɗa mini, wane ne a cikinmu yake gefen sarkin Isra’ila?”
Et le cœur du roi de Syrie fut agité à cause de cela; et il appela ses serviteurs, et leur dit: Ne me déclarerez-vous pas qui d’entre nous est pour le roi d’Israël?
12 Sai ɗaya daga cikin hafsoshinsa ya ce, “Babu waninmu, ranka yă daɗe; Elisha, annabin da yake a Isra’ila ne, yake faɗa wa sarkin Isra’ila dukan zancen da ka yi a ɗakinka.”
Et l’un de ses serviteurs [lui] dit: Personne, ô roi, mon seigneur! mais Élisée, le prophète qui est en Israël, déclare au roi d’Israël les paroles que tu dis dans ta chambre à coucher.
13 Sai sarki ya ba da umarni ya ce, “Ku je ku tabbatar da inda yake don in aika mutane a kamo shi.” Sai ya sami rahoto cewa, “Yana a Dotan.”
Et il dit: Allez, et voyez où il est, et j’enverrai et je le prendrai. Et on lui rapporta, disant: Le voilà à Dothan.
14 Sai ya aika da dawakai da kekunan yaƙi da babban rukunin soja zuwa can. Suka bi dare, suka kewaye birnin.
Et il y envoya des chevaux, et des chars, et de grandes forces; et ils allèrent de nuit, et environnèrent la ville.
15 Sa’ad da bawan mutumin Allah ya farka ya kuma fita kashegari da sassafe, sai ga mayaƙa tare da dawakai da kekunan yaƙi sun kewaye birni. Sai bawan ya ce, “Ranka yă daɗe! Me za mu yi?”
Et celui qui servait l’homme de Dieu se leva de bon matin et sortit: et voici, une armée entourait la ville, et des chevaux, et des chars. Et son jeune homme lui dit: Hélas! mon seigneur, comment ferons-nous?
16 Sai annabin ya ce, “Kada ka ji tsoro, waɗanda suke tare da mu sun fi waɗanda suke tare da su.”
Et il dit: Ne crains pas; car ceux qui sont avec nous sont en plus grand nombre que ceux qui sont avec eux.
17 Sa’an nan Elisha ya yi addu’a ya ce, “Ya Ubangiji, ka buɗe idanunsa yă gani!” Sai Ubangiji ya buɗe idanun bawan, ya duba, ya ga tuddai cike da dawakai da keken yaƙin wuta kewaye da Elisha.
Et Élisée pria, et dit: Éternel, je te prie, ouvre ses yeux, afin qu’il voie. Et l’Éternel ouvrit les yeux du jeune homme, et il vit: et voici la montagne était pleine de chevaux et de chars de feu autour d’Élisée.
18 Yayinda abokan gāba suka gangaro wajensa, sai Elisha ya yi addu’a ga Ubangiji ya ce, “Ka sa mutanen nan su zama makafi.” Sai Ubangiji ya buge su da makanta kamar yadda Elisha ya roƙa.
Et [les Syriens] descendirent vers Élisée; et il pria l’Éternel, et dit: Je te prie, frappe cette nation de cécité. Et il les frappa de cécité, selon la parole d’Élisée.
19 Elisha ya ce musu, “Wannan ba ita ce hanyar ba, ba kuma gari ke nan ba, ku bi ni, zan kuwa kai ku wurin mutumin da kuke nema!” Sai ya kai su Samariya.
Et Élisée leur dit: Ce n’est pas ici le chemin, et ce n’est pas ici la ville; venez après moi, et je vous mènerai vers l’homme que vous cherchez. Et il les mena à Samarie.
20 Bayan suka shiga birnin, sai Elisha ya ce, “Ubangiji, ka buɗe idanun mutanen nan don su gani.” Sa’an nan Ubangiji ya buɗe idanunsu suka ga kansu a tsakiyar Samariya.
Et il arriva, quand ils furent entrés à Samarie, qu’Élisée dit: Éternel, ouvre les yeux à ces [hommes], afin qu’ils voient. Et l’Éternel ouvrit leurs yeux, et ils virent: et voici, [ils étaient] au milieu de Samarie.
21 Da sarkin Isra’ila ya gan su, sai ya tambayi Elisha ya ce, “In kashe su ne, mahaifina? In kashe su?”
Et le roi d’Israël dit à Élisée, quand il les vit: Frapperai-je, frapperai-je, mon père?
22 Elisha ya ce, “Kada ka kashe su. Za ka kashe mutanen da ka kame da takobi ko bakanka? Ka ba su abinci da ruwa su ci, su sha, sa’an nan su koma wurin maigidansu.”
Et il dit: Tu ne frapperas point; ceux que tu aurais faits captifs avec ton épée et ton arc, les frapperais-tu? Mets du pain et de l’eau devant eux; et qu’ils mangent et boivent, et qu’ils s’en aillent vers leur seigneur.
23 Saboda haka aka shirya musu babban liyafa, bayan sun ci, suka kuma sha, sai ya tura su zuwa wurin maigidansu. Ta haka’yan harin Aram suka daina kai hari a yankin Isra’ila.
Et il leur prépara un grand festin, et ils mangèrent et burent; et il les renvoya, et ils s’en allèrent vers leur seigneur. Et les bandes des Syriens ne revinrent plus dans le pays d’Israël.
24 Bayan wani lokaci, Ben-Hadad sarkin Aram ya tattara dukan rundunarsa, ya je ya kewaye Samariya da yaƙi.
Et il arriva, après cela, que Ben-Hadad, roi de Syrie, rassembla toute son armée, et monta, et assiégea Samarie.
25 Aka yi babban yunwa a cikin birnin. Saboda daɗewar wannan kewayewar da aka yi wa birnin, sai yunwa ta ɓarke a birnin, har ana sayar da kan jaki a kan shekel tamanin, kashin kurciya kuma a kan shekel biyar.
Et il y eut une grande famine dans Samarie; et voici, ils la serraient de près, jusqu’à ce que la tête d’un âne fut à 80 [sicles] d’argent, et le quart d’un kab de fiente de pigeon à cinq [sicles] d’argent.
26 Yayinda sarkin Isra’ila yake wucewa kusa da katanga, sai wata mace ta yi masa kuka ta ce, “Ka taimake ni, ranka yă daɗe, sarki!”
Et il arriva, comme le roi d’Israël passait sur la muraille, qu’une femme lui cria, disant: Sauve-moi, ô roi, mon seigneur!
27 Sai sarki ya amsa ya ce, “In Ubangiji bai taimake ki ba, me zan iya yi? Ina da hatsi ko ruwan inabin da zan ba ki ne?”
Et il dit: Si l’Éternel ne te sauve pas, comment te sauverais-je? Serait-ce au moyen de l’aire ou de la cuve?
28 Sa’an nan ya tambaye ta ya ce, “Me ya faru?” Sai ta amsa ta ce, “Wannan mace ta ce mini, ‘Kawo ɗanki mu ci yau, gobe kuwa mu ci ɗana.’
Et le roi lui dit: Qu’as-tu? Et elle dit: Cette femme-là m’a dit: Donne ton fils, et nous le mangerons aujourd’hui; et demain nous mangerons mon fils.
29 Saboda haka muka dafa ɗana muka ci. Kashegari na ce mata, ‘Kawo ɗanki mu ci,’ amma ta ɓoye shi.”
Et nous avons bouilli mon fils, et nous l’avons mangé; et le jour après, je lui ai dit: Donne ton fils, et nous le mangerons. Et elle a caché son fils.
30 Da sarki ya ji maganar macen sai ya yage rigunansa. Sa’ad da sarki yake wucewa a kan katangar birnin, sai mutane suka gan yana saye da rigar makoki a ciki.
Et aussitôt que le roi entendit les paroles de la femme, il déchira ses vêtements. Et comme il passait sur la muraille, le peuple le vit: et voici, il avait un sac sur sa chair, en dedans.
31 Ya ce, “Bari Allah yă yi mini hukunci mai tsanani har ma fiye da haka, idan ban cire kan Elisha ɗan Shafat yau ba!”
Et [le roi] dit: Ainsi Dieu me fasse, et ainsi il y ajoute, si la tête d’Élisée, fils de Shaphath, demeure sur lui aujourd’hui!
32 To, Elisha yana zaune a cikin gidansa, dattawa kuwa suna zaune tare da shi. Sai sarki ya aiki ɗan aika yă ci gaba, amma kafin ɗan aikan yă isa, Elisha ya ce wa dattawan, “Kun gani ko? Wannan mai kisa ya aiko a cire mini kai! To, idan ɗan aikan ya iso, sai ku rufe ƙofar da ƙarfi, ku bar shi a waje. Ba da jimawa ba, maigidansa zai bi bayansa?”
Et Élisée était assis dans sa maison, et les anciens étaient assis avec lui, et [le roi] envoya un homme devant lui. Avant que le messager arrive auprès de lui, [Élisée] dit aux anciens: Voyez-vous que ce fils d’un meurtrier envoie pour m’ôter la tête? Voyez quand le messager entrera; fermez la porte, et repoussez-le avec la porte: n’est-ce pas le bruit des pieds de son maître après lui?
33 Yana magana da su ke nan, sai ga ɗan aikan ya gangaro wajensa. Sarki kuma ya ce, “Wannan bala’in daga wurin Ubangiji ya fito. Don me zan sa zuciya ga Ubangiji kuma?”
Il parlait encore avec eux, quand voici, le messager descendit vers lui. Et [le roi] dit: Voici, ce mal est de par l’Éternel; pourquoi m’attendrais-je encore à l’Éternel?

< 2 Sarakuna 6 >