< 2 Sarakuna 6 >

1 Sai ƙungiyar annabawa suka ce wa Elisha, “Duba, wurin da muke taruwa ya kāsa mana.
One day a group of prophets said to Elisha, “Look, this place where we meet together with you is very small.
2 Bari mu je Urdun, inda kowannenmu zai saro itace; mu gina inda za mu zauna.” Sai ya ce musu, “Ku je.”
Allow us to go to the Jordan [River and cut down some trees to make] logs to build a new meeting place.” So Elisha said, “Okay, go.”
3 Sai ɗayansu ya ce, “Ba za ka zo tare da bayinka ba?” Sai Elisha ya ce “Zan zo.”
One of them said to Elisha, “Please come with us.” So Elisha replied, “Okay, I will go with you.”
4 Ya kuma tafi tare da su. Suka tafi Urdun suka fara saran itatuwa.
So they went together. When they reached the Jordan [River], they cut down some trees.
5 Yayinda ɗayansu yake cikin saran itace, sai kan gatarin ya fāɗi a ruwa, sai ya ce, “Kash, ranka yă daɗe, kayan aro ne fa!”
But while one of them was cutting down a tree, suddenly the axe head [separated from the handle and] fell into the water. He cried out to Elisha, “O, Master, what shall I do? [The axe is not mine]; I borrowed it!”
6 Sai mutumin Allah ya ce, “Daidai ina ya fāɗa?” Da ya nuna masa wurin, sai Elisha ya yanka ɗan sanda ya jefa a wurin, ya sa kan gatarin ya taso sama.
Elisha replied, “Where did it fall into the water?” After the man showed him the place, Elisha cut off a stick, and threw it into the water, and caused the iron axe head to float [on top of the water].
7 Sai ya ce masa, “Ka ɗauko.” Sai mutumin ya miƙa hannu ya ɗauka.
Elisha said, “Take it out of the water.” So the man reached his hand down and picked up the axe head.
8 To, fa, sarkin Aram yana yaƙi da Isra’ila. Bayan ya tattauna da hafsoshinsa, sai ya ce, “Zan kafa sansanina a wurin kaza da kaza.”
Whenever the king of Syria [prepared to send his army to] fight against Israel, he first consulted his officers, and then told them where they should set up their tents.
9 Sai mutumin Allah ya aika wa sarkin Isra’ila cewa, “Ka yi hankali da wuce wuri kaza, domin Arameyawa za su gangara can.”
But each time, Elisha would send a message to warn the king of Israel, [telling him where the army of Syria was planning to attack them, ] saying, “Be sure that your army does not go near that place, because the army of Syria has set up their tents there.”
10 Saboda haka sarkin Isra’ila ya lura da inda mutumin Allah ya ambata. Sau da sau Elisha yakan yi wa sarki kashedi, don haka ya riƙa taka yi tsantsan a wuraren nan.
So the king of Israel would send [messengers] to warn [the people who lived in] that place, and the people would remain on guard. That happened several times.
11 Wannan ya husata sarkin Aram. Ya kira hafsoshinsa ya tambaye su ya ce, “Ku faɗa mini, wane ne a cikinmu yake gefen sarkin Isra’ila?”
The king of Syria was very upset/disturbed/angry about that. So he summoned his army officers and said to them, “[Obviously] one of you is (betraying us/revealing our plans) to the king of Israel. Which one of you is doing it?”
12 Sai ɗaya daga cikin hafsoshinsa ya ce, “Babu waninmu, ranka yă daɗe; Elisha, annabin da yake a Isra’ila ne, yake faɗa wa sarkin Isra’ila dukan zancen da ka yi a ɗakinka.”
One of his officers answered, “Your Majesty, it is not one of us. Elisha the prophet [knows what we plan to do, and he] tells the king of Israel everything. He even knows what you say in your own bedroom!”
13 Sai sarki ya ba da umarni ya ce, “Ku je ku tabbatar da inda yake don in aika mutane a kamo shi.” Sai ya sami rahoto cewa, “Yana a Dotan.”
The king of Syria replied, “Go and find out where he is, and I will send [some men there] to capture him.” Someone told him, “People say that he is in Dothan [town north of Samaria].”
14 Sai ya aika da dawakai da kekunan yaƙi da babban rukunin soja zuwa can. Suka bi dare, suka kewaye birnin.
So the king sent a large group of soldiers [to Dothan] with horses and chariots. They arrived at night and surrounded the town.
15 Sa’ad da bawan mutumin Allah ya farka ya kuma fita kashegari da sassafe, sai ga mayaƙa tare da dawakai da kekunan yaƙi sun kewaye birni. Sai bawan ya ce, “Ranka yă daɗe! Me za mu yi?”
Early the next morning, Elisha’s servant got up and went outside the house. He saw the soldiers of Syria with their horses and chariots surrounding the town. So he went inside [the house and reported it to Elisha] and exclaimed, “O, sir! What are we going to do?”
16 Sai annabin ya ce, “Kada ka ji tsoro, waɗanda suke tare da mu sun fi waɗanda suke tare da su.”
Elisha replied, “Do not be afraid! Those who will be helping us will be more than those who will be helping them!”
17 Sa’an nan Elisha ya yi addu’a ya ce, “Ya Ubangiji, ka buɗe idanunsa yă gani!” Sai Ubangiji ya buɗe idanun bawan, ya duba, ya ga tuddai cike da dawakai da keken yaƙin wuta kewaye da Elisha.
Then he prayed, “Yahweh, I request that you open my servant’s eyes in order that he can see [what is out there]!” So Yahweh enabled the servant to look out and see that surrounding the hill on which the town [was built] was a huge number of horses, and chariots made of fire!
18 Yayinda abokan gāba suka gangaro wajensa, sai Elisha ya yi addu’a ga Ubangiji ya ce, “Ka sa mutanen nan su zama makafi.” Sai Ubangiji ya buge su da makanta kamar yadda Elisha ya roƙa.
When the army of Syria prepared to attack Elisha, he prayed again, saying, “Yahweh, cause all these soldiers to become blind!” Yahweh answered his prayer and caused them to be unable to see clearly.
19 Elisha ya ce musu, “Wannan ba ita ce hanyar ba, ba kuma gari ke nan ba, ku bi ni, zan kuwa kai ku wurin mutumin da kuke nema!” Sai ya kai su Samariya.
Then Elisha went to them and said, “You are not on the right road; this is not the city that you are searching for. I will take you to the man whom you are searching for.” But he led them to Samaria, [the capital of Israel]!
20 Bayan suka shiga birnin, sai Elisha ya ce, “Ubangiji, ka buɗe idanun mutanen nan don su gani.” Sa’an nan Ubangiji ya buɗe idanunsu suka ga kansu a tsakiyar Samariya.
As soon as they entered Samaria, Elisha prayed again, saying, “Yahweh, now enable these soldiers to see correctly again!” So Yahweh enabled them to see correctly, and they were surprised to see that they were inside Samaria [city].
21 Da sarkin Isra’ila ya gan su, sai ya tambayi Elisha ya ce, “In kashe su ne, mahaifina? In kashe su?”
When the king of Israel saw them, he said to Elisha, “Sir, shall I [tell my soldiers to] kill them? Shall we kill all of them?”
22 Elisha ya ce, “Kada ka kashe su. Za ka kashe mutanen da ka kame da takobi ko bakanka? Ka ba su abinci da ruwa su ci, su sha, sa’an nan su koma wurin maigidansu.”
Elisha replied, “No, you must not kill them. If your army captured many of your enemies in a battle, you would certainly not [RHQ] kill them. Give these men something to eat and drink, and then allow them to return to their king.”
23 Saboda haka aka shirya musu babban liyafa, bayan sun ci, suka kuma sha, sai ya tura su zuwa wurin maigidansu. Ta haka’yan harin Aram suka daina kai hari a yankin Isra’ila.
So the king of Israel did that. He told his servants to provide a big feast for them. And when they had eaten and drunk plenty, he sent them away. They returned to the king of Syria [and told him what had happened]. So for a while after that, soldiers from Syria stopped raiding/attacking towns in Israel.
24 Bayan wani lokaci, Ben-Hadad sarkin Aram ya tattara dukan rundunarsa, ya je ya kewaye Samariya da yaƙi.
But some time later, Ben-Hadad, the king of Syria, assembled his entire army, and they went to Samaria and surrounded the city [for a long time].
25 Aka yi babban yunwa a cikin birnin. Saboda daɗewar wannan kewayewar da aka yi wa birnin, sai yunwa ta ɓarke a birnin, har ana sayar da kan jaki a kan shekel tamanin, kashin kurciya kuma a kan shekel biyar.
Because of that, after a while there was hardly any food left inside the city, with the result that eventually a donkey’s head, [which was usually worthless, ] cost eighty pieces of silver, and (one cup/0.3 liter) of dove’s dung cost five pieces of silver.
26 Yayinda sarkin Isra’ila yake wucewa kusa da katanga, sai wata mace ta yi masa kuka ta ce, “Ka taimake ni, ranka yă daɗe, sarki!”
One day when the king of Israel was walking on top of the city wall, a woman cried out to him, “Your Majesty, help me!”
27 Sai sarki ya amsa ya ce, “In Ubangiji bai taimake ki ba, me zan iya yi? Ina da hatsi ko ruwan inabin da zan ba ki ne?”
He replied, “If Yahweh will not help you, I certainly cannot [RHQ] help you. I certainly [RHQ] do not have any wheat or wine!
28 Sa’an nan ya tambaye ta ya ce, “Me ya faru?” Sai ta amsa ta ce, “Wannan mace ta ce mini, ‘Kawo ɗanki mu ci yau, gobe kuwa mu ci ɗana.’
What is your problem?” She replied, “Several days ago, that woman [over there] said to me, ‘[Because we have nothing left to eat, ] let’s kill your son today, in order that we can eat his flesh. Then tomorrow we can [kill] my son [and] eat his flesh.’
29 Saboda haka muka dafa ɗana muka ci. Kashegari na ce mata, ‘Kawo ɗanki mu ci,’ amma ta ɓoye shi.”
So we [killed my son and cut his body up and] boiled his flesh and ate it. The next day, I said to her, ‘Now give your son to me, in order that we can [kill him and cook his flesh and] eat it.’ But she has hidden her son!”
30 Da sarki ya ji maganar macen sai ya yage rigunansa. Sa’ad da sarki yake wucewa a kan katangar birnin, sai mutane suka gan yana saye da rigar makoki a ciki.
When the king heard what the woman said, he tore his robe [to show that he was very distressed]. The people who were standing close to the wall were able to see that the king was wearing rough cloth underneath his robe [because he was very distressed].
31 Ya ce, “Bari Allah yă yi mini hukunci mai tsanani har ma fiye da haka, idan ban cire kan Elisha ɗan Shafat yau ba!”
The king exclaimed, “I wish/hope that God will strike me dead if I do not cut off the head of Elisha today, [because he is the one who has caused these terrible things to happen to us]!”
32 To, Elisha yana zaune a cikin gidansa, dattawa kuwa suna zaune tare da shi. Sai sarki ya aiki ɗan aika yă ci gaba, amma kafin ɗan aikan yă isa, Elisha ya ce wa dattawan, “Kun gani ko? Wannan mai kisa ya aiko a cire mini kai! To, idan ɗan aikan ya iso, sai ku rufe ƙofar da ƙarfi, ku bar shi a waje. Ba da jimawa ba, maigidansa zai bi bayansa?”
So the king sent an officer to get Elisha. Before the officer arrived, Elisha was sitting in his house with some Israeli elders who were talking with him. Elisha said to them, “That murderer, [the king of Israel, ] is sending someone here to kill me. Listen: When he arrives, shut the door and do not allow him to come in. And the king will be coming right behind that officer!”
33 Yana magana da su ke nan, sai ga ɗan aikan ya gangaro wajensa. Sarki kuma ya ce, “Wannan bala’in daga wurin Ubangiji ya fito. Don me zan sa zuciya ga Ubangiji kuma?”
And while he was still speaking, the king and the officer arrived. The king said, “It is Yahweh who has caused us to have all this trouble/suffering. (Why should I wait any longer [RHQ] for him to do something [to help us]?/It is useless for me to wait any longer for him [to help us]!)”

< 2 Sarakuna 6 >