< 2 Sarakuna 5 >

1 Na’aman babban hafsan hafsoshin rundunar sarkin Aram ne, kuma ƙasaitaccen mutum ne mai martaba a idon maigidansa, domin ta wurinsa Ubangiji ya ba Aram nasara. Na’aman jarumi ne ƙwarai, amma yana da kuturta.
Njalo uNamani induna yebutho lenkosi yeSiriya wayengumuntu omkhulu phambi kwenkosi yakhe, lohloniphekayo, ngoba ngaye uJehova wayenikile iSiriya ukukhululwa. Njalo lindoda yayiliqhawe elilamandla, kodwayayingumlephero.
2 To, daga cikin hare haren da mutanen Aram suke kaiwa, sai suka kama wata yarinya daga ƙasar Isra’ila, aka sa ta zama mai yi wa matar Na’aman aiki.
Njalo amaSiriya ayephumile ngamaviyo athumba intombazana elizweni lakoIsrayeli, eyayisima phambi komkaNamani.
3 Sai ta ce wa uwargijiyarta, “Da dai shugabana zai ga annabin da yake Samariya, da annabin zai warkar da shi daga kuturtarsa.”
Yasisithi enkosikazini yayo: Sengathi inkosi yami ingaba phambi komprofethi oseSamariya; khona ubezayiphilisa kubulephero bayo.
4 Sai Na’aman ya je wurin maigidansa ya faɗa masa abin da yarinyan nan daga Isra’ila ta faɗa.
Wasengena watshela inkosi yakhe esithi: Intombazana evela elizweni lakoIsrayeli itsho ukuthi lokuthi.
5 Sarkin Aram ya ce, “Ko ta ƙaƙa, ka tafi, zan aika da wasiƙa ga sarkin Isra’ila.” Sai Na’aman ya tashi, ɗauke da talenti goma na azurfa, shekel dubu shida na zinariya, da tufafi kashi goma.
Inkosi yeSiriya yasisithi: Suka, uhambe, ngizathumela incwadi enkosini yakoIsrayeli. Wasehamba wathatha esandleni sakhe amathalenta esiliva alitshumi lenhlamvu zegolide ezizinkulungwane eziyisithupha lezigqoko zokuntshintsha ezilitshumi.
6 Wasiƙar da ya kai wa sarkin Isra’ila ta ce, “Da wannan wasiƙa ina aika Na’aman gare ka don ka warkar da kuturtarsa.”
Waseletha incwadi enkosini yakoIsrayeli isithi: Khathesi-ke, lapho le incwadi isifikile kuwe, khangela, ngithume kuwe uNamani inceku yami ukuze umphilise kubulephero bakhe.
7 Da sarkin Isra’ila ya karanta wasiƙar, sai ya yayyage tufafinsa, ya ce, “Ni Allah ne? Zan iya ɗauke rai ko in mai da shi? Me ya sa wannan mutum ya turo mini wannan mutum in warkar da kuturtarsa? Dubi fa yadda yake nemana da faɗa!”
Kwasekusithi inkosi yakoIsrayeli isiyibalile leyoncwadi yadabula izigqoko zayo yathi: NginguNkulunkulu yini ukuthi ngibulale loba ngiphilise, ukuthi lo athumele kimi ukuthi ngiphilise umuntu kubulephero bakhe? Ngakho-ke, ake linanzelele libone ukuthi udinga ithuba lokumelana lami.
8 Da Elisha mutumin Allah ya ji cewa sarkin Isra’ila ya yayyage tufafinsa, sai ya aika masa da wannan saƙo, “Don me za ka yayyage tufafinka? Ka sa mutumin yă zo wurina, zai kuwa san cewa akwai annabi a Isra’ila.”
Kwasekusithi lapho uElisha umuntu kaNkulunkulu esizwa ukuthi inkosi yakoIsrayeli idabule izigqoko zayo, wathumela enkosini esithi: Udabuleleni izigqoko zakho? Akeze kimi ukuze azi ukuthi kukhona umprofethi koIsrayeli.
9 Saboda haka Na’aman ya tafi da dawakansa da keken yaƙinsa, ya tsaya a ƙofar gidan Elisha.
Ngakho uNamani weza lamabhiza akhe lenqola yakhe, wema emnyango wendlu kaElisha.
10 Sai Elisha ya aika’yan saƙo su ce masa, “Je, ka nutse sau bakwai a Urdun, fatar jikinka za tă koma daidai, ka kuma tsarkaka.”
UElisha wasethuma isithunywa kuye esithi: Hamba uyegeza kasikhombisa eJordani, inyama yakho izabuyela kuwe, uhlambuluke.
11 Amma Na’aman ya tashi daga can da fushi yana cewa, “Na yi tsammani zai fito ne wurina yă tsaya, yă yi kira bisa ga sunan Ubangiji Allahnsa, yă kaɗa hannunsa inda kuturtar take, yă warkar da ni.
Kodwa uNamani wathukuthela, wahamba, wathi: Khangela, bengisithi uzaphuma sibili eze kimi, eme, abize ibizo leNkosi uNkulunkulu wakhe, ahambahambise isandla sakhe phezu kwendawo, aphilise umlephero.
12 Ashe, Amana da Farfa, kogunan da suke Damaskus, ba su fi dukan ruwan da suke Isra’ila ba? Me zai sa ba zan nutse cikinsu in tsarkaka ba?” Sai ya juya ya yi tafiyarsa da fushi.
IAbana leFaripari imifula yeDamaseko kayingcono yini kulawo wonke amanzi akoIsrayeli? Bengingegeze kiyo ngihlambuluke yini? Wasetshibilika wahamba ngolaka oluvuthayo.
13 Sai bayin Na’aman suka je kusa da shi suka ce, “Baba, da a ce annabin ya ce ka yi wani abu mai wuya, da ba za ka yi ba? Balle fa cewa kawai ya yi, ‘Ka yi wanka ka kuma tsarkaka’!”
Kodwa inceku zakhe zasondela zakhuluma laye zathi: Baba, aluba umprofethi ubekhulume lawe ulutho olukhulu, ubungayikulwenza yini? Pho, kakhulu kangakanani uba ethe kuwe: Geza uhlambuluke?
14 Saboda haka Na’aman ya je ya nutse sau bakwai a Urdun, yadda mutumin Allah ya ce masa, sai fatarsa ta koma kamar ta ɗan yaro.
Wasesehla, wazigxamuza eJordani kasikhombisa njengokwelizwi lomuntu kaNkulunkulu, lenyama yakhe yabuyela yafanana lenyama yomntwana omncinyane, wahlambuluka-ke.
15 Sai Na’aman da dukan masu hidimarsa suka koma wurin mutumin Allah. Na’aman ya tsaya a gaban mutumin Allah ya ce, “Yanzu na san cewa babu wani Allah a duk duniya sai a Isra’ila. Ina roƙonka ka karɓi kyauta daga hannun bawanka.”
Wasebuyela kumuntu kaNkulunkulu, yena lalo lonke ixuku lakhe, wafika wema phambi kwakhe, wathi: Khangela sengisazi ukuthi kakulaNkulunkulu emhlabeni wonke, ngaphandle kwakoIsrayeli; khathesi-ke ake wemukele isipho encekwini yakho.
16 Annabin ya amsa ya ce, “Muddin Ubangiji wanda nake bauta masa yana a raye, ba zan karɓi kome ba.” Ko da yake Na’aman ya yi ta roƙonsa, amma ya ƙi.
Kodwa wathi: Kuphila kukaJehova engimi phambi kwakhe, kangiyikuthatha lutho. Wasemncenga ukuthi athathe, kodwa wala.
17 Sai Na’aman ya ce, “In ba za ka karɓa ba, ina roƙonka, bari a ba wa bawanka ƙasa gwargwadon abin da jakuna biyu za su iya ɗauka, gama bawanka ba zai sāke yin hadaya ta ƙonawa, ko wata hadaya ga wani allah ba, sai ga Ubangiji.
UNamani wasesithi: Uba kungenjalo, akunikwe inceku yakho umthwalo wembongolo ezimbili wenhlabathi. Ngoba inceku yakho kayisayikwenza umnikelo wokutshiswa lomhlatshelo kwabanye onkulunkulu, kodwa eNkosini.
18 Amma ina fata Ubangiji zai gafarta wa bawanka saboda abu guda. Bari yă gafarta mini sa’ad da na raka sarkina zuwa haikalin Rimmon domin yă yi sujada, bari Ubangiji yă yi wa bawanka gafara saboda wannan.”
Kulinto iNkosi kayithethelele inceku yakho: Nxa inkosi yami ingena endlini kaRimoni ukukhonza lapho, yeyame esandleni sami, lami ngikhonze endlini kaRimoni, lapho ngikhonza endlini kaRimoni, iNkosi ake ithethelele inceku yakho kulinto.
19 Sai Elisha ya ce, “Ka sauka lafiya.” Bayan Na’aman ya yi ɗan nisa,
Wasesithi kuye: Hamba ngokuthula. Wasesuka kuye ummango omfitshane.
20 sai Gehazi, bawan Elisha mutumin Allah, ya yi tunani a ransa ya ce, “Maigidana ya yi wa Na’aman mutumin Aram nan ƙaramci da bai karɓi duk abin da ya kawo ba. Muddin Ubangiji yana a raye, zan bi shi a guje in karɓi wani abu daga gare shi.”
Kodwa uGehazi inceku kaElisha umuntu kaNkulunkulu wathi: Khangela, inkosi yami imyekele uNamani umSiriya lo ngokungemukeli esandleni sakhe lokho akulethileyo. Kuphila kukaJehova, ngizagijima ngimlandele, ngithathe kuye okuthile.
21 Saboda haka Gehazi ya bi Na’aman a guje. Da Na’aman ya hango shi yana zuwa a guje, sai ya sauka daga keken yaƙinsa ya tarye shi ya ce, “Lafiya?”
UGehazi wasegijima wamlandela uNamani. Kwathi uNamani ebona ogijimayo emva kwakhe, wehla enqoleni ukuze amhlangabeze, wathi: Kulungile yini?
22 Gehazi ya amsa ya ce, “Lafiya ƙalau. Maigidana ne ya aiko ni cewa, ‘Samari biyu daga ƙungiyar annabawa sun ziyarce ni daga ƙasa mai duwatsu na yankin Efraim. Ina roƙonka ka ba su talenti na azurfa da tufafi kashi biyu.’”
Wasesithi: Kulungile. Inkosi yami ingithumile, isithi: Khangela, ngitsho khathesi kufikile kimi amajaha amabili evela entabeni yakoEfrayimi awamadodana abaprofethi; ake uwanike ithalenta lesiliva lezigqoko ezimbili zokuntshintsha.
23 Na’aman ya ce, “Ba damuwa, karɓi talenti biyu.” Ya roƙi Gehazi yă karɓa, sa’an nan ya ƙunsa masa talentin biyu na azurfa ya sa masa a kan jakankuna biyu, ya haɗa da tufafi kashi biyu, ya ba bayinsa biyu suka ɗauka, ya ce su sha gaban Gehazi.
UNamani wasesithi: Vuma, uthathe amathalenta amabili. Wasemcindezela, wabophela amathalenta amabili emigodleni emibili, lezembatho zokuntshintsha ezimbili, wakunika ababili benceku zakhe, bakuthwala phambi kwakhe.
24 Da Gehazi ya isa wani tudu, sai ya karɓi kayan daga wurin bayin ya shiga da su a ɓoye a cikin gida. Sa’an nan ya sallami mutanen suka tafi.
Esefike oqaqeni, wakuthatha esandleni sazo, wakubeka endlini; waseyekela amadoda ahamba, asesuka.
25 Sa’an nan ya shiga ya tsaya a gaban maigidansa Elisha. Sai Elisha ya tambaye shi ya ce, “Ina ka je, Gehazi?” Sai Gehazi ya amsa ya ce, “Bawanka bai je ko’ina ba.”
Yena wasengena wema phambi kwenkosi yakhe; uElisha wasesithi kuye: Uvela ngaphi, Gehazi? Wasesithi: Inceku yakho ibingayanga le lale.
26 Amma Elisha ya ce masa, “Ashe, ba ina tare da kai a ruhu ba sa’ad da mutumin ya sauko daga keken yaƙinsa ya tarye ka. Kana gani wannan lokaci ne da za a karɓi kuɗi, da riguna, da gonar inabi, da tumaki, da bijimai, da bayi maza da mata?
Wasesithi kuye: Inhliziyo yami ayihambanga yini lapho lowomuntu etshibilika enqoleni yakhe ukukuhlangabeza? Kuyisikhathi sokwemukela imali yini, lokwemukela izigqoko, lezivande zemihlwathi, lezivini, lezimvu, lezinkabi, lezinceku, lezincekukazi?
27 Kuturtar Na’aman zai manne maka da zuriyarka har abada.” Sai Gehazi ya fita daga gaban Elisha a kuturce, fari fat kamar dusar ƙanƙara.
Ngakho ubulephero bukaNamani buzanamathela kuwe lenzalweni yakho kuze kube nininini. Wasephuma ebukhoneni bakhe engumlephero emhlophe njengeliqhwa elikhithikileyo.

< 2 Sarakuna 5 >