< 2 Sarakuna 5 >

1 Na’aman babban hafsan hafsoshin rundunar sarkin Aram ne, kuma ƙasaitaccen mutum ne mai martaba a idon maigidansa, domin ta wurinsa Ubangiji ya ba Aram nasara. Na’aman jarumi ne ƙwarai, amma yana da kuturta.
[A man named] Naaman was the commander of the army of Syria. Yahweh had enabled him to win many victories/battles. He was a great warrior, and as a result the king of Syria greatly respected him. But he had (leprosy/a dreaded skin disease).
2 To, daga cikin hare haren da mutanen Aram suke kaiwa, sai suka kama wata yarinya daga ƙasar Isra’ila, aka sa ta zama mai yi wa matar Na’aman aiki.
[Some time previously, ] groups of soldiers/marauders from Syria had raided/attacked the land of Israel, and they had captured a young girl [and taken her to Syria]. She became a servant for Naaman’s wife.
3 Sai ta ce wa uwargijiyarta, “Da dai shugabana zai ga annabin da yake Samariya, da annabin zai warkar da shi daga kuturtarsa.”
One day, that girl said to her, “I wish that (my master/your husband) would go to see the prophet in Samaria. That prophet would heal your husband from his leprosy.”
4 Sai Na’aman ya je wurin maigidansa ya faɗa masa abin da yarinyan nan daga Isra’ila ta faɗa.
[Naaman’s wife told her husband] what the girl from Israel had said, [and] Naaman told [that] to the king.
5 Sarkin Aram ya ce, “Ko ta ƙaƙa, ka tafi, zan aika da wasiƙa ga sarkin Isra’ila.” Sai Na’aman ya tashi, ɗauke da talenti goma na azurfa, shekel dubu shida na zinariya, da tufafi kashi goma.
The king said to him, “Okay, go [and see the prophet]. I will [write] a letter for you to take to the king of Israel, [saying that I sent you].” The king wrote in the letter, “I am sending this letter with [my army commander] Naaman, who serves me [faithfully]. I want you to heal him of his disease.” So Naaman, [assuming/thinking that the king of Israel was the prophet, took the letter and] 750 pounds of silver, 150 pounds of gold, and ten sets of clothing, to give to the king of Israel, [and he went to Samaria, taking along several servants].
6 Wasiƙar da ya kai wa sarkin Isra’ila ta ce, “Da wannan wasiƙa ina aika Na’aman gare ka don ka warkar da kuturtarsa.”
7 Da sarkin Isra’ila ya karanta wasiƙar, sai ya yayyage tufafinsa, ya ce, “Ni Allah ne? Zan iya ɗauke rai ko in mai da shi? Me ya sa wannan mutum ya turo mini wannan mutum in warkar da kuturtarsa? Dubi fa yadda yake nemana da faɗa!”
[When he arrived in Samaria, he gave the letter to the king] of Israel. The king read the letter. Then, being very dismayed, the king tore his clothes and said, “I am not God [RHQ]! I am not able to enable people to live or to die [RHQ]! Why does [the king] who wrote this letter request me to cure this man of his leprosy? I think that he is just wanting to start a fight with me!”
8 Da Elisha mutumin Allah ya ji cewa sarkin Isra’ila ya yayyage tufafinsa, sai ya aika masa da wannan saƙo, “Don me za ka yayyage tufafinka? Ka sa mutumin yă zo wurina, zai kuwa san cewa akwai annabi a Isra’ila.”
But the prophet Elisha heard that the king of Israel had torn his robe [and said that]. So he sent a message to the king, saying, “Why are you upset/frustrated [RHQ]? Send Naaman to me, and he will find out that [because] I am a true prophet [here] in Israel, [I can help/heal him].”
9 Saboda haka Na’aman ya tafi da dawakansa da keken yaƙinsa, ya tsaya a ƙofar gidan Elisha.
So Naaman went with his horses and chariots to Elisha’s house and waited outside the door.
10 Sai Elisha ya aika’yan saƙo su ce masa, “Je, ka nutse sau bakwai a Urdun, fatar jikinka za tă koma daidai, ka kuma tsarkaka.”
But Elisha [did not come to the door. Instead, he] sent a messenger to Naaman, to tell him, “Go to the Jordan [River] and wash yourself seven times in the river. Then your skin will be restored/healed, and you will no longer have leprosy.”
11 Amma Na’aman ya tashi daga can da fushi yana cewa, “Na yi tsammani zai fito ne wurina yă tsaya, yă yi kira bisa ga sunan Ubangiji Allahnsa, yă kaɗa hannunsa inda kuturtar take, yă warkar da ni.
But Naaman became very angry. He said, “I thought that surely he would wave his hand over the leprosy, and pray to Yahweh his god, and heal me!
12 Ashe, Amana da Farfa, kogunan da suke Damaskus, ba su fi dukan ruwan da suke Isra’ila ba? Me zai sa ba zan nutse cikinsu in tsarkaka ba?” Sai ya juya ya yi tafiyarsa da fushi.
Surely the Abana River and the Pharpar River in Damascus [in my own country of Syria] are [RHQ] better than any of the rivers in Israel! Why can I not wash in those rivers and be healed?” [RHQ] So he turned and walked away with great anger/disgust.
13 Sai bayin Na’aman suka je kusa da shi suka ce, “Baba, da a ce annabin ya ce ka yi wani abu mai wuya, da ba za ka yi ba? Balle fa cewa kawai ya yi, ‘Ka yi wanka ka kuma tsarkaka’!”
But his servants came to him, and [one of them] said, “Sir, if that prophet had told you to do something difficult, you would certainly [RHQ] have done it. So you should certainly do what he says and wash [in the Jordan River] to be healed!” [RHQ]
14 Saboda haka Na’aman ya je ya nutse sau bakwai a Urdun, yadda mutumin Allah ya ce masa, sai fatarsa ta koma kamar ta ɗan yaro.
So Naaman went down to the Jordan [River] and washed himself seven times, as (the prophet/Elisha) told him to do. Then his skin was restored/healed, and it became healthy/smooth, like the skin of a young child.
15 Sai Na’aman da dukan masu hidimarsa suka koma wurin mutumin Allah. Na’aman ya tsaya a gaban mutumin Allah ya ce, “Yanzu na san cewa babu wani Allah a duk duniya sai a Isra’ila. Ina roƙonka ka karɓi kyauta daga hannun bawanka.”
Then Naaman and those who were with him went back to talk to Elisha. They stood in front of him, and Naaman said, “Now I know that there are no real gods anywhere else in the world, but there is a God here in Israel! So now please accept these gifts that I [have brought to you]!”
16 Annabin ya amsa ya ce, “Muddin Ubangiji wanda nake bauta masa yana a raye, ba zan karɓi kome ba.” Ko da yake Na’aman ya yi ta roƙonsa, amma ya ƙi.
But Elisha replied, “Just as certainly as Yahweh, the one whom I serve, lives, I will not accept any gifts.” Naaman kept urging him [to accept the gifts], but Elisha kept refusing.
17 Sai Na’aman ya ce, “In ba za ka karɓa ba, ina roƙonka, bari a ba wa bawanka ƙasa gwargwadon abin da jakuna biyu za su iya ɗauka, gama bawanka ba zai sāke yin hadaya ta ƙonawa, ko wata hadaya ga wani allah ba, sai ga Ubangiji.
Then Naaman said, “Okay, but [I have one request. This dirt here in Israel is holy, so] please allow me to take some dirt from this place and put it [in sacks] on two mules. Then I will take it back home with me [and make an altar on this dirt]. From now on, I will offer sacrifices to Yahweh [on that altar]. I will not offer sacrifices to any other god.
18 Amma ina fata Ubangiji zai gafarta wa bawanka saboda abu guda. Bari yă gafarta mini sa’ad da na raka sarkina zuwa haikalin Rimmon domin yă yi sujada, bari Ubangiji yă yi wa bawanka gafara saboda wannan.”
However, when my master, [the king, ] goes into the temple of the god Rimmon to worship him/it there, and he is leaning on my arm, I hope/desire that Yahweh will forgive me because I will have to bow down, too.”
19 Sai Elisha ya ce, “Ka sauka lafiya.” Bayan Na’aman ya yi ɗan nisa,
Elisha replied, “Go home, and do not worry about that.” So Naaman [and his servants] started to travel home.
20 sai Gehazi, bawan Elisha mutumin Allah, ya yi tunani a ransa ya ce, “Maigidana ya yi wa Na’aman mutumin Aram nan ƙaramci da bai karɓi duk abin da ya kawo ba. Muddin Ubangiji yana a raye, zan bi shi a guje in karɓi wani abu daga gare shi.”
But then Elisha’s servant Gehazi said to himself, “It is not good that my master allowed this Syrian man to leave like this. He should have accepted his gifts. So just as certainly as Yahweh lives, I will go and catch up with Naaman and get something from him.”
21 Saboda haka Gehazi ya bi Na’aman a guje. Da Na’aman ya hango shi yana zuwa a guje, sai ya sauka daga keken yaƙinsa ya tarye shi ya ce, “Lafiya?”
So Gehazi hurried to catch up with Naaman. When Naaman saw Gehazi running toward him, he [stopped] the chariot [in which he was riding, ] jumped out, and went to see what Gehazi wanted. He asked him, “Is everything all right?”
22 Gehazi ya amsa ya ce, “Lafiya ƙalau. Maigidana ne ya aiko ni cewa, ‘Samari biyu daga ƙungiyar annabawa sun ziyarce ni daga ƙasa mai duwatsu na yankin Efraim. Ina roƙonka ka ba su talenti na azurfa da tufafi kashi biyu.’”
Gehazi replied, “Yes, but two young prophets from the hilly area where the descendants of Ephraim live have just arrived. Elisha has sent me to tell you that he would like 75 pounds of silver and two sets of clothing to give to them.”
23 Na’aman ya ce, “Ba damuwa, karɓi talenti biyu.” Ya roƙi Gehazi yă karɓa, sa’an nan ya ƙunsa masa talentin biyu na azurfa ya sa masa a kan jakankuna biyu, ya haɗa da tufafi kashi biyu, ya ba bayinsa biyu suka ɗauka, ya ce su sha gaban Gehazi.
Naaman replied, “Certainly! You can have 150 pounds of silver!” He urged Gehazi to take it. He also gave him two sets of clothing. He tied up the silver in two bags and gave them to two of his servants to carry back to Elisha.
24 Da Gehazi ya isa wani tudu, sai ya karɓi kayan daga wurin bayin ya shiga da su a ɓoye a cikin gida. Sa’an nan ya sallami mutanen suka tafi.
But when they arrived at the hill [where Elisha lived], Gehazi took the silver and the clothes from Naaman’s servants and sent the servants back to Naaman. Then he took those things into his house and hid them.
25 Sa’an nan ya shiga ya tsaya a gaban maigidansa Elisha. Sai Elisha ya tambaye shi ya ce, “Ina ka je, Gehazi?” Sai Gehazi ya amsa ya ce, “Bawanka bai je ko’ina ba.”
When he went to Elisha, Elisha asked him, “Where did you go, Gehazi?” Gehazi replied, “I did not go anywhere.”
26 Amma Elisha ya ce masa, “Ashe, ba ina tare da kai a ruhu ba sa’ad da mutumin ya sauko daga keken yaƙinsa ya tarye ka. Kana gani wannan lokaci ne da za a karɓi kuɗi, da riguna, da gonar inabi, da tumaki, da bijimai, da bayi maza da mata?
Elisha asked him, [“Do you not realize that] my spirit was there when Naaman got out of his chariot to talk with you? This is certainly not [RHQ] the time to accept gifts of money and clothes and olive groves and vineyards and sheep and oxen and servants!
27 Kuturtar Na’aman zai manne maka da zuriyarka har abada.” Sai Gehazi ya fita daga gaban Elisha a kuturce, fari fat kamar dusar ƙanƙara.
Because you have done this, you and your children and all your descendants, forever, will have leprosy just like Naaman had!” And when Gehazi left the room, he was a leper! His skin was as white as snow!

< 2 Sarakuna 5 >