< 2 Sarakuna 5 >
1 Na’aman babban hafsan hafsoshin rundunar sarkin Aram ne, kuma ƙasaitaccen mutum ne mai martaba a idon maigidansa, domin ta wurinsa Ubangiji ya ba Aram nasara. Na’aman jarumi ne ƙwarai, amma yana da kuturta.
And Na'aman, the captain of the army of the king of Syria, was a great man before his Lord, and highly honored; because by him had the Lord given victory unto Syria: and this man was valiant in war, [but] a leper.
2 To, daga cikin hare haren da mutanen Aram suke kaiwa, sai suka kama wata yarinya daga ƙasar Isra’ila, aka sa ta zama mai yi wa matar Na’aman aiki.
And the Syrians had gone out in predatory troops, and had brought away captive out of the land of Israel a little maiden; and she waited on Na'aman's wife.
3 Sai ta ce wa uwargijiyarta, “Da dai shugabana zai ga annabin da yake Samariya, da annabin zai warkar da shi daga kuturtarsa.”
And she said unto her mistress, Oh that my Lord were but before the prophet that is in Samaria! then would he heal him of his leprosy.
4 Sai Na’aman ya je wurin maigidansa ya faɗa masa abin da yarinyan nan daga Isra’ila ta faɗa.
And he went in, and told his lord, saying, Thus and thus hath spoken the maiden that is from the land of Israel.
5 Sarkin Aram ya ce, “Ko ta ƙaƙa, ka tafi, zan aika da wasiƙa ga sarkin Isra’ila.” Sai Na’aman ya tashi, ɗauke da talenti goma na azurfa, shekel dubu shida na zinariya, da tufafi kashi goma.
And the king of Syria said, Go to, go, and I will send a letter unto the king of Israel. And he departed, and took with him ten talents of silver, and six thousand pieces of gold, and ten changes of garments.
6 Wasiƙar da ya kai wa sarkin Isra’ila ta ce, “Da wannan wasiƙa ina aika Na’aman gare ka don ka warkar da kuturtarsa.”
And he brought the letter to the king of Israel, which said, And now when this letter cometh unto thee, behold, I have sent to thee Na'aman my servant, that thou mayest heal him of his leprosy.
7 Da sarkin Isra’ila ya karanta wasiƙar, sai ya yayyage tufafinsa, ya ce, “Ni Allah ne? Zan iya ɗauke rai ko in mai da shi? Me ya sa wannan mutum ya turo mini wannan mutum in warkar da kuturtarsa? Dubi fa yadda yake nemana da faɗa!”
And it came to pass, when the king of Israel read the letter, that he rent his clothes, and said, Am I God, to kill and to make alive, that this one doth send unto me to heal a man of his leprosy? for know to a certainty, I pray you, and see that he but seeketh a quarrel against me.
8 Da Elisha mutumin Allah ya ji cewa sarkin Isra’ila ya yayyage tufafinsa, sai ya aika masa da wannan saƙo, “Don me za ka yayyage tufafinka? Ka sa mutumin yă zo wurina, zai kuwa san cewa akwai annabi a Isra’ila.”
And it happened, when Elisha' the man of God heard that the king of Israel had rent his clothes, that he sent to the king, saying, Wherefore hast thou rent thy clothes? let him but come to me, and he shall know that there is a prophet in Israel.
9 Saboda haka Na’aman ya tafi da dawakansa da keken yaƙinsa, ya tsaya a ƙofar gidan Elisha.
And Na'aman came with his horses and with his chariot, and remained at the door of the house of Elisha'.
10 Sai Elisha ya aika’yan saƙo su ce masa, “Je, ka nutse sau bakwai a Urdun, fatar jikinka za tă koma daidai, ka kuma tsarkaka.”
And Elisha' sent a messenger unto him, saying, Go and bathe seven times in the Jordan, and thy flesh shall be restored [healthy] to thee, and thou shalt become clean.
11 Amma Na’aman ya tashi daga can da fushi yana cewa, “Na yi tsammani zai fito ne wurina yă tsaya, yă yi kira bisa ga sunan Ubangiji Allahnsa, yă kaɗa hannunsa inda kuturtar take, yă warkar da ni.
But Na'aman became wroth, and went away, and said, Behold, I had thought, He will surely come out to me, and stand, and call on the name of the Lord his God, and swing his hand over the place, and heal the leper.
12 Ashe, Amana da Farfa, kogunan da suke Damaskus, ba su fi dukan ruwan da suke Isra’ila ba? Me zai sa ba zan nutse cikinsu in tsarkaka ba?” Sai ya juya ya yi tafiyarsa da fushi.
Are not Amanah and Pharpar, the rivers of Damascus, better than all the waters of Israel? may I not bathe in them, and become clean? and he turned and went away in a rage.
13 Sai bayin Na’aman suka je kusa da shi suka ce, “Baba, da a ce annabin ya ce ka yi wani abu mai wuya, da ba za ka yi ba? Balle fa cewa kawai ya yi, ‘Ka yi wanka ka kuma tsarkaka’!”
And his servants came near, and spoke unto him, and they said, My father, if the prophet had bidden thee a great thing, wouldst thou not do it? how much rather then, when he hath said to thee, Bathe, and become clean?
14 Saboda haka Na’aman ya je ya nutse sau bakwai a Urdun, yadda mutumin Allah ya ce masa, sai fatarsa ta koma kamar ta ɗan yaro.
Then went he down, and dived seven times in the Jordan, according to the word of the man of God: and his flesh was restored [healthy] like the flesh of a little boy, and he became clean.
15 Sai Na’aman da dukan masu hidimarsa suka koma wurin mutumin Allah. Na’aman ya tsaya a gaban mutumin Allah ya ce, “Yanzu na san cewa babu wani Allah a duk duniya sai a Isra’ila. Ina roƙonka ka karɓi kyauta daga hannun bawanka.”
And he returned to the man of God, he with all his camp, and came and stood before him, and said, Behold, now I know that there is no god on all the earth, but in Israel; and now, I pray thee, take a present from thy servant.
16 Annabin ya amsa ya ce, “Muddin Ubangiji wanda nake bauta masa yana a raye, ba zan karɓi kome ba.” Ko da yake Na’aman ya yi ta roƙonsa, amma ya ƙi.
But he said, As the Lord liveth before whom I have stood, I will take none: and he urged him to take it; but he refused.
17 Sai Na’aman ya ce, “In ba za ka karɓa ba, ina roƙonka, bari a ba wa bawanka ƙasa gwargwadon abin da jakuna biyu za su iya ɗauka, gama bawanka ba zai sāke yin hadaya ta ƙonawa, ko wata hadaya ga wani allah ba, sai ga Ubangiji.
And Na'aman said, If [thou wilt] not, [then] let there be given, I pray thee, unto thy servant two mules' burden of earth; for thy servant will not offer henceforth either burnt-offering or peace-sacrifice unto other gods, except unto the Lord.
18 Amma ina fata Ubangiji zai gafarta wa bawanka saboda abu guda. Bari yă gafarta mini sa’ad da na raka sarkina zuwa haikalin Rimmon domin yă yi sujada, bari Ubangiji yă yi wa bawanka gafara saboda wannan.”
For this thing may the Lord pardon thy servant, that when my Lord goeth into the house of Rimmon to prostrate himself there, and he leaneth on my hand, and I prostrate myself also in the house of Rimmon: when I prostrate myself in the house of Rimmon, may the Lord pardon thy servant for this thing.
19 Sai Elisha ya ce, “Ka sauka lafiya.” Bayan Na’aman ya yi ɗan nisa,
And he said unto him, Go in peace: so he departed from him some distance.
20 sai Gehazi, bawan Elisha mutumin Allah, ya yi tunani a ransa ya ce, “Maigidana ya yi wa Na’aman mutumin Aram nan ƙaramci da bai karɓi duk abin da ya kawo ba. Muddin Ubangiji yana a raye, zan bi shi a guje in karɓi wani abu daga gare shi.”
But Gechazi, the servant of Elisha' the man of God, said, Behold, my master hath spared Na'aman, this Syrian, in not receiving from his hand what he had brought; but, as the Lord liveth, I will run after him, and take some little thing from him.
21 Saboda haka Gehazi ya bi Na’aman a guje. Da Na’aman ya hango shi yana zuwa a guje, sai ya sauka daga keken yaƙinsa ya tarye shi ya ce, “Lafiya?”
So Gechazi hurried after Na'aman; and when Na'aman saw him running after him, he lighted doom from the chariot to meet him, and said, Is [all] well?
22 Gehazi ya amsa ya ce, “Lafiya ƙalau. Maigidana ne ya aiko ni cewa, ‘Samari biyu daga ƙungiyar annabawa sun ziyarce ni daga ƙasa mai duwatsu na yankin Efraim. Ina roƙonka ka ba su talenti na azurfa da tufafi kashi biyu.’”
And he said, [all] is well. My master hath sent me, saying, Behold, even now there are come to me from the mountain of Ephraim two young men of the sons of the prophets: do give them, I pray thee, a talent of silver, and two changes of garments.
23 Na’aman ya ce, “Ba damuwa, karɓi talenti biyu.” Ya roƙi Gehazi yă karɓa, sa’an nan ya ƙunsa masa talentin biyu na azurfa ya sa masa a kan jakankuna biyu, ya haɗa da tufafi kashi biyu, ya ba bayinsa biyu suka ɗauka, ya ce su sha gaban Gehazi.
And Na'aman said, Give thy assent, take two talents. And he urged him, and bound up two talents of silver in two bags, with two changes of garments, and he gave them unto his two young men, and they carried them before him.
24 Da Gehazi ya isa wani tudu, sai ya karɓi kayan daga wurin bayin ya shiga da su a ɓoye a cikin gida. Sa’an nan ya sallami mutanen suka tafi.
And when he came to the hill, he took them from their hand, and bestowed them in the house: and he dismissed the men, and they departed.
25 Sa’an nan ya shiga ya tsaya a gaban maigidansa Elisha. Sai Elisha ya tambaye shi ya ce, “Ina ka je, Gehazi?” Sai Gehazi ya amsa ya ce, “Bawanka bai je ko’ina ba.”
But he went in, and stood before his master. And Elisha' said unto him, Whence comest thou, Gechazi? And he said, Thy servant went not hither or thither.
26 Amma Elisha ya ce masa, “Ashe, ba ina tare da kai a ruhu ba sa’ad da mutumin ya sauko daga keken yaƙinsa ya tarye ka. Kana gani wannan lokaci ne da za a karɓi kuɗi, da riguna, da gonar inabi, da tumaki, da bijimai, da bayi maza da mata?
And he said unto him, My mind was not gone, when the man turned round from his chariot to meet thee. Is it a time to take money, and to take garments, and oliveyards, and vineyards, and sheep, and oxen, and men-servants, and maid-servants?
27 Kuturtar Na’aman zai manne maka da zuriyarka har abada.” Sai Gehazi ya fita daga gaban Elisha a kuturce, fari fat kamar dusar ƙanƙara.
May then the leprosy of Na'aman cleave unto thee, and unto thy seed for ever. And he went out from his presence a leper [as white] as snow.