< 2 Sarakuna 5 >

1 Na’aman babban hafsan hafsoshin rundunar sarkin Aram ne, kuma ƙasaitaccen mutum ne mai martaba a idon maigidansa, domin ta wurinsa Ubangiji ya ba Aram nasara. Na’aman jarumi ne ƙwarai, amma yana da kuturta.
Na: ima: ne da Silia dadi gagui wa: i ouligisudafa esalu. Silia hina bagade da Na: ima: ne ea houba: le, bagadewane nodone dawa: i. Bai Hina Gode da fidibiba: le, Na: ima: ne ea dadi gagui wa: i da ilima ha lai huluanema hasasali. E da dadi gagui dunu noga: idafa. Be amomane e da lebolosi aiya madelai.
2 To, daga cikin hare haren da mutanen Aram suke kaiwa, sai suka kama wata yarinya daga ƙasar Isra’ila, aka sa ta zama mai yi wa matar Na’aman aiki.
Eso afaega, Silia dunu da Isala: ili fi doagala: loba, ilia da Isala: ili uda mano fonobahadi amo gagulaligili, Silia sogega oule asi. Silia soge ganodini, amo uda mano da Na: ima: ne idua ea hawa: hamosu.
3 Sai ta ce wa uwargijiyarta, “Da dai shugabana zai ga annabin da yake Samariya, da annabin zai warkar da shi daga kuturtarsa.”
Eso afaega e da ea hina (Na: ima: ne idua) ema amane sia: i, “Na hanai da na ouligisu dunu Na: ima: ne da Samelia sogega esalebe balofede dunu Ilaisia, amo ba: la masunu da defea. E da ea oloi uhinisimu dawa:”
4 Sai Na’aman ya je wurin maigidansa ya faɗa masa abin da yarinyan nan daga Isra’ila ta faɗa.
Na: ima: ne da amo uda mano ea sia: be nababeba: le, e da Silia hina bagadema asili, amo uda mano ea sia: i amo ema olelei.
5 Sarkin Aram ya ce, “Ko ta ƙaƙa, ka tafi, zan aika da wasiƙa ga sarkin Isra’ila.” Sai Na’aman ya tashi, ɗauke da talenti goma na azurfa, shekel dubu shida na zinariya, da tufafi kashi goma.
Silia hina bagade da ema amane sia: i, “Di Isala: ili hina bagadema asili, na meloa dedei amo ema ima!” Amaiba: le, Na: ima: ne da asi. E da silifa fage 30,000 agoane amola gouli fage 6,000 agoane, amola ga: su abula noga: idafa nabuane agoane gaguli asi.
6 Wasiƙar da ya kai wa sarkin Isra’ila ta ce, “Da wannan wasiƙa ina aika Na’aman gare ka don ka warkar da kuturtarsa.”
Meloa dedei ea gaguli asi amoga da amane dedei dialebe ba: i, “Na dadi gagui wa: i ouligisu dunu Na: ima: ne da amo meloa dedei gaguli misi. Na hanai da ea oloi, dia uhinisima: mu!”
7 Da sarkin Isra’ila ya karanta wasiƙar, sai ya yayyage tufafinsa, ya ce, “Ni Allah ne? Zan iya ɗauke rai ko in mai da shi? Me ya sa wannan mutum ya turo mini wannan mutum in warkar da kuturtarsa? Dubi fa yadda yake nemana da faɗa!”
Isala: ili hina bagade da amo meloa idilalu, e da da: i dione fofogadigili, ea abula gadelale, amane sia: i, “Abuliba: le, Silia hina bagade da nama na da amo dunu ea oloi uhinisima: ne sia: sala: ? E da na Godeyale dawa: bela: ? Na da bogoi dunu bu uhinisimu dawa: bela: ? Na da Gode hame! Na dawa: loba, e da nama gegemusa: logo hogolala.”
8 Da Elisha mutumin Allah ya ji cewa sarkin Isra’ila ya yayyage tufafinsa, sai ya aika masa da wannan saƙo, “Don me za ka yayyage tufafinka? Ka sa mutumin yă zo wurina, zai kuwa san cewa akwai annabi a Isra’ila.”
Balofede dunu Ilaisia da amo hou nababeba: le, e da Isala: ili hina bagadema amane sia: si, “Di da abuliba: le fofogadigili da: i diobela: ? Amo dunu nama asunasima! Na da ema, balofede dunu da Isala: ili soge ganodini esala, amo ema olelemu.”
9 Saboda haka Na’aman ya tafi da dawakansa da keken yaƙinsa, ya tsaya a ƙofar gidan Elisha.
Amaiba: le, Na: ima: ne amola ea hosi amola ‘sa: liode’ da asili, Ilaisia ea diasu logo holei gadenene aligi.
10 Sai Elisha ya aika’yan saƙo su ce masa, “Je, ka nutse sau bakwai a Urdun, fatar jikinka za tă koma daidai, ka kuma tsarkaka.”
Ilaisia da hawa: hamosu dunu afae, Na: ima: nema amane adola masa: ne asunasi, “Di da asili, Yodane Hano amoga fesuale agoane ulima! Amasea, dia oloi da uhi dagoi ba: mu.”
11 Amma Na’aman ya tashi daga can da fushi yana cewa, “Na yi tsammani zai fito ne wurina yă tsaya, yă yi kira bisa ga sunan Ubangiji Allahnsa, yă kaɗa hannunsa inda kuturtar take, yă warkar da ni.
Be Na: ima: ne da amo sia: nabalu, ougi bagadeba: le, asi. E amane sia: i, “Na da agoane dawa: i! Ilaisia hisu da gadili, nama misini, ea Hina Godema sia: ne gadolalu, ea lobo na oloi da: iya gadodili sisiga: lu, na oloi uhinisimu da defea galu.
12 Ashe, Amana da Farfa, kogunan da suke Damaskus, ba su fi dukan ruwan da suke Isra’ila ba? Me zai sa ba zan nutse cikinsu in tsarkaka ba?” Sai ya juya ya yi tafiyarsa da fushi.
Aba: na Hano amola Faba Hano amo ilia da ninia Silia soge moilai bai bagade Dama: saga: se amoga, Isala: ili hano huluane ilia hou baligisa! Na da amo ganodini ulalu, uhi ba: mu da defea galu!”
13 Sai bayin Na’aman suka je kusa da shi suka ce, “Baba, da a ce annabin ya ce ka yi wani abu mai wuya, da ba za ka yi ba? Balle fa cewa kawai ya yi, ‘Ka yi wanka ka kuma tsarkaka’!”
Na: ima: ne ea hawa: hamosu dunu da ema asili, amane sia: i, “Hina! Balofede dunu da dima gasa bagade liligi hamoma: ne sia: noba, di da amo hamona: noba! Amaiba: le, asaboi liligi ea sia: i, amo defele hano ulima, amo hamonanu, uhinisi ba: mu da defea.”
14 Saboda haka Na’aman ya je ya nutse sau bakwai a Urdun, yadda mutumin Allah ya ce masa, sai fatarsa ta koma kamar ta ɗan yaro.
Amaiba: le, Na: ima: ne da Ilaisia ea hamoma: ne sia: i defele, Yodane Hanoa asili, fesuale agoane ulalu, ea oloi da uhi dagoi ba: i. Ea da: i da noga: idafa amola bobonomane, mano fonobahadi ea da: i defele bai.
15 Sai Na’aman da dukan masu hidimarsa suka koma wurin mutumin Allah. Na’aman ya tsaya a gaban mutumin Allah ya ce, “Yanzu na san cewa babu wani Allah a duk duniya sai a Isra’ila. Ina roƙonka ka karɓi kyauta daga hannun bawanka.”
Na: ima: ne amola ea dunu huluane da Ilaisiama buhagili, e da Ilaisia: ma amane sia: i, “Na da wali dawa: , Godedafa da Isala: ili fi ilia Gode fawane! Eno da hame gala! Amaiba: le, hina! Na da hahawane iasu dima imunu!”
16 Annabin ya amsa ya ce, “Muddin Ubangiji wanda nake bauta masa yana a raye, ba zan karɓi kome ba.” Ko da yake Na’aman ya yi ta roƙonsa, amma ya ƙi.
Ilaisia da bu adole i, “Na da Hina Gode, Ea hawa: hamosu hamonana. Amo Ea Dioba: le na da dafawane ilegele sia: sa. Na da dia hahawane iabe liligi amo hamedafa lamu.” Na: ima: ne da ea iabe lama: ne ouwalei, be Ilaisia da hamedafa lamu sia: i.
17 Sai Na’aman ya ce, “In ba za ka karɓa ba, ina roƙonka, bari a ba wa bawanka ƙasa gwargwadon abin da jakuna biyu za su iya ɗauka, gama bawanka ba zai sāke yin hadaya ta ƙonawa, ko wata hadaya ga wani allah ba, sai ga Ubangiji.
Amaiba: le, Na: ima: ne da amane sia: i, “Defea! Di da na hahawane iasu amo hame labeba: le, na da miule aduna amo da: iya ligisimu defele, osobo lale, na sogega bu gaguli masunu da defeala: ? Bai wali winini, na da eno ‘gode’ma gobele salasu hou hamedafa hamomu. Na da Hina Godedafa, Ema fawane gobele salimu.
18 Amma ina fata Ubangiji zai gafarta wa bawanka saboda abu guda. Bari yă gafarta mini sa’ad da na raka sarkina zuwa haikalin Rimmon domin yă yi sujada, bari Ubangiji yă yi wa bawanka gafara saboda wannan.”
Amola, na da agoane hanai gala. Na hina (Silia hina bagade) ani da Limone (Silia ‘gode’) amo ea debolo diasuga, ema nodone sia: ne gadomusa: ahoasea, Hina Gode da amo hou gogolema: ne olofomu na da hanai. Amabela: ? E da amo hou gogolema: ne olofoma: bela: ?”
19 Sai Elisha ya ce, “Ka sauka lafiya.” Bayan Na’aman ya yi ɗan nisa,
Ilaisia da amane sia: i, “Di hahawane olofole masa!” Amalu, Na: ima: ne da fisili, asi. E da logoga asi mae sedagiliwane ahoanoba,
20 sai Gehazi, bawan Elisha mutumin Allah, ya yi tunani a ransa ya ce, “Maigidana ya yi wa Na’aman mutumin Aram nan ƙaramci da bai karɓi duk abin da ya kawo ba. Muddin Ubangiji yana a raye, zan bi shi a guje in karɓi wani abu daga gare shi.”
Ilaisia ea hawa: hamosu dunu Gihaisai, da hisu asigi dawa: su ganodini amane dawa: i, “Na hina e da Na: ima: ne ea ema bidi amo mae iawane, udigili masa: ne, logo doasi dagoi. E da Na: ima: ne ea imunusa: sia: i amo lamu da defea galu. Na da Hina Gode Esala Ea Dioba: le agoane ilegesa. Na da ema fa: no bobogele, bidi ea gaguli buhagilalebe, amo na lamu.”
21 Saboda haka Gehazi ya bi Na’aman a guje. Da Na’aman ya hango shi yana zuwa a guje, sai ya sauka daga keken yaƙinsa ya tarye shi ya ce, “Lafiya?”
Amaiba: le, e da Na: ima: ne asi fa: no bobogei. Na: ima: ne da dunu ema hehenaia fa: no bobogelalebe ba: loba, e da e gousa: musa: ea ‘sa: liode’ da: iya esalu, amo gudu aliaguduli, ema amane adole ba: i, “Adi giadofabela: ?”
22 Gehazi ya amsa ya ce, “Lafiya ƙalau. Maigidana ne ya aiko ni cewa, ‘Samari biyu daga ƙungiyar annabawa sun ziyarce ni daga ƙasa mai duwatsu na yankin Efraim. Ina roƙonka ka ba su talenti na azurfa da tufafi kashi biyu.’”
Gihaisai da bu adole i, “Giadofai hame! Be na hina da dima amane sia: sima: ne, na asunasi. ‘Ifala: ime agolo soge amogai, balofede gilisisu amoga, balofede dunu aduna da wahawane doaga: i dagoi. E da dia amo dunuma silifa fage 3,000 agoane amola ga: su abula noga: idafa aduna, elama ima: ne sia: sa.”
23 Na’aman ya ce, “Ba damuwa, karɓi talenti biyu.” Ya roƙi Gehazi yă karɓa, sa’an nan ya ƙunsa masa talentin biyu na azurfa ya sa masa a kan jakankuna biyu, ya haɗa da tufafi kashi biyu, ya ba bayinsa biyu suka ɗauka, ya ce su sha gaban Gehazi.
Na: ima: ne da bu adole i, “Defeadafa! Be di silifa fage 6,000 agoane lama!” E da amo lama: ne ouwalei. Na: ima: ne da silifa fage esa aduna ganodini sanawene lala: gi. Amola e da esa amola ga: su abula noga: idafa aduna amo ea hawa: hamosu dunu aduna elama ianu, ela Gihaisai bisili masa: ne asunasi.
24 Da Gehazi ya isa wani tudu, sai ya karɓi kayan daga wurin bayin ya shiga da su a ɓoye a cikin gida. Sa’an nan ya sallami mutanen suka tafi.
Ilia da agolo amoga Ilaisia da esalu, amoga doaga: loba, Gihaisai da esa aduna elama lale, hi diasu ganodini gaguli asili, ligisi. Amalalu, e da Na: ima: ne ea hawa: hamosu dunu buhagima: ne asunasi.
25 Sa’an nan ya shiga ya tsaya a gaban maigidansa Elisha. Sai Elisha ya tambaye shi ya ce, “Ina ka je, Gehazi?” Sai Gehazi ya amsa ya ce, “Bawanka bai je ko’ina ba.”
Gihaisai da diasua buhagilaloba, Ilaisia da ema amane adole ba: i, “Di da habidili asibala: ?” E bu adole i, “Hina! Na da enodini hame asi!”
26 Amma Elisha ya ce masa, “Ashe, ba ina tare da kai a ruhu ba sa’ad da mutumin ya sauko daga keken yaƙinsa ya tarye ka. Kana gani wannan lokaci ne da za a karɓi kuɗi, da riguna, da gonar inabi, da tumaki, da bijimai, da bayi maza da mata?
Be Ilaisia da amane sia: i, “Na: ima: ne da ea ‘sa: liode’ fila heda: lu, di gousa: musa: gudu aliagudusia, na a: silibu da amogawi esalebeba: le, hou huluane ba: i dagoi. Wewaba amo muni amola abula amola olife sagai, waini sagai, sibi, bulamagau amola hawa: hamosu dunu bidi agoane lamu da defea hame gala.
27 Kuturtar Na’aman zai manne maka da zuriyarka har abada.” Sai Gehazi ya fita daga gaban Elisha a kuturce, fari fat kamar dusar ƙanƙara.
Wali, Na: ima: ne ea oloi da dima madelamu. Amola di amola digaga fi da eso huluane amo olo madelale esalumu.” Gihaisai da fisili asili, Na: ima: ne ea musa: lebelosi olo amo madelai dagoi ba: i. Ea da: i gadofo da anegagi ofo defele, ahea: iyaidafa ba: i.

< 2 Sarakuna 5 >