< 2 Sarakuna 4 >

1 Matar wani daga ƙungiyar annabawa ta yi wa Elisha kuka ta ce, “Mijina, bawanka, ya mutu, ka kuma san yadda ya girmama Ubangiji. Amma ga shi yanzu mai binsa bashi ya zo yă kwashe’ya’yana maza biyu su zama bayinsa.”
En kvinne som var hustru til en av profetenes disipler, ropte til Elisa og sa: Din tjener, min mann, er død, og du vet at din tjener fryktet Herren; og nu kommer en som han stod i gjeld til, og vil ta begge mine sønner til træler.
2 Elisha ya amsa mata ya ce, “Me kike so in yi miki? Ki faɗa mini, me kike da shi a gidanki?” Sai ta ce, “Baiwarka ba ta da kome a can, sai ɗan tulun man zaitun.”
Elisa sa til henne: Hvad kan jeg gjøre for dig? Si mig: Hvad har du i huset? Hun svarte: Din tjenerinne har intet annet i huset enn en krukke med salve-olje.
3 Elisha ya ce, “Ki je wurin dukan maƙwabtanki, ki nemi tulunan da babu kome a ciki. Kada ki nemo kaɗan kawai.
Da sa han: Gå til alle dine naboer og be om å få låne hjem nogen tomme kar, bare ikke for få!
4 Sa’an nan ki shiga ciki, ki kulle ƙofar da ke da’ya’yanki kuke ciki. Ku ɗuɗɗura man a dukan tulunan, sa’ad da kowanne ya cika, sai ki ajiye a gefe.”
Gå så inn og lukk døren efter dig og dine sønner og hell oljen i alle karene, og efter hvert som de blir fulle, skal du sette dem bort.
5 Ta tashi ta shiga tare da’ya’yanta maza, suka kulle ƙofa.’Ya’yanta suka kawo mata tuluna, ita kuma tana ɗurawa.
Og hun gikk fra ham og lukket døren efter sig og sine sønner; de bar karene frem til henne, og hun helte i.
6 Da dukan tulunan suka cika, sai ta ce wa ɗanta, “Kawo mini wani tulu.” Amma ya amsa ya ce, “Ai, ba saura.” Sa’an nan man ya daina zuba.
Og da karene var fulle, sa hun til sin sønn: Bær ennu et kar frem til mig! Men han svarte: Det er ikke flere kar. Da stanset oljen.
7 Sai ta tafi ta faɗa wa mutumin Allah. Shi kuwa ya ce mata, “Tafi, ki sayar da man, ki biya bashinki. Ki biya bukatanki da na’ya’yanki da sauran da ya rage.”
Så kom hun og fortalte det til den Guds mann, og han sa: Gå og selg oljen og betal din gjeld; så kan du og dine sønner leve av det som blir tilovers.
8 Wata rana Elisha ya tafi Shunem. Akwai wata mai arziki a can wadda ta gayyace shi cin abinci. Sai ya zama duk lokacin da yake wucewa, yakan tsaya a can don cin abinci.
En dag gikk Elisa over til Sunem; en velstående kvinne som bodde der, nødde ham til å ete hos sig; og så ofte han siden drog der forbi, tok han inn der og fikk sig mat.
9 Ta ce wa mijinta, “Na san cewa wannan mutum da kullum yake zuwa nan mai tsarki ne na Allah.
Engang sa hun til sin mann: Hør her, jeg vet at han som jevnlig drar forbi oss, er en hellig Guds mann.
10 Bari mu yi ɗan ɗaki a rufin gida mu kuma sa masa gado da tebur da kujera da kuma fitila. Saboda a duk lokacin da ya zo wurinmu, sai yă sauka a can.”
La oss gjøre et lite tak-kammer med murvegger og sette inn der en seng for ham og et bord og en stol og en lysestake; når han så kommer til oss, kan han ta inn der.
11 Wata rana da Elisha ya zo, sai ya haura ɗakinsa ya kwanta.
Så kom han dit en dag og tok inn i tak-kammeret og la sig der.
12 Ya ce wa bawansa Gehazi, “Kira mutuniyar Shunam nan.” Sai ya kira ta, ta zo ta tsaya a gabansa.
Og han sa til sin dreng Gehasi: Kall på den sunamittiske kone som bor her! Så kalte han på henne, og hun trådte frem for ham.
13 Elisha ya ce masa, “Ka ce mata, ‘Kin yi duk wannan ɗawainiya saboda mu. Yanzu, me kike so a yi miki? Kina so mu yi magana a madadinki wa sarki ko babban hafsan mayaƙa?’” Sai ta ce, “A’a, ina da dukan abin da nake bukata a cikin jama’ata.”
Han hadde sagt til ham: Si til henne: Nu har du hatt all denne uro for vår skyld; hvad kan jeg gjøre for dig? Er det noget jeg kan tale til kongen om for dig eller til hærføreren? Hun svarte: Jeg bor jo her midt iblandt mitt folk.
14 Sai Elisha ya tambayi Gehazi ya ce, “Me za mu yi mata?” Sai ya amsa ya ce, “Ba ta da ɗa, ga shi kuma mijinta ya tsufa.”
Så sa han: Hvad kan jeg da gjøre for henne? Gehasi svarte: Jo, hun har ingen sønn, og hennes mann er gammel.
15 Sai Elisha ya ce, “Ka kira ta.” Sai ya kira ta, ta zo ta tsaya a bakin ƙofa.
Da sa han: Kall på henne! Så kalte han på henne, og hun trådte frem i døren.
16 Elisha ya ce mata, “War haka baɗi, za ki riƙe ɗa na kanki.” Sai ta ce masa, “A’a, ranka yă daɗe, mutumin Allah, kada ka ruɗi baiwarka!”
Da sa han: Til næste år ved denne tid skal du holde en sønn i dine armer. Men hun sa: Nei, min herre, du som er en Guds mann! Lyv ikke for din tjenerinne!
17 Amma matan ta yi ciki, a shekara ta biye kuwa a daidai lokacin, sai ta haifi ɗa kamar yadda Elisha ya faɗa mata.
Og kvinnen blev fruktsommelig og fødte en sønn det følgende år nettop på den tid som Elisa hadde sagt henne.
18 Yaron ya yi girma, wata rana sai ya tafi wurin mahaifinsa, wanda yake tare da masu girbi.
Da barnet blev større, hendte det en dag at han gikk ut til sin far, som var ute hos høstfolkene.
19 Ba zato sai ya ce wa mahaifinsa, “Wayyo! Kaina yana mini ciwo! Kaina yana mini ciwo!” Sai mahaifinsa ya ce wa bawansa, “Kai shi wurin mahaifiyarsa.”
Og han sa til sin far: Mitt hode! Mitt hode! Da sa faren til sin dreng: Bær ham hjem til hans mor!
20 Bayan bawan ya ɗaga shi ya kai wurin mahaifiyarsa, sai yaron ya zauna a cinyarta har tsakar rana, sa’an nan ya mutu.
Og han tok ham og bar ham hjem til hans mor, og han satt på hennes kne til om middagen; da døde han.
21 Sai ta haura ta shimfiɗa shi a gadon mutumin Allah, ta rufe ƙofar, ta fita.
Hun gikk op og la ham på den Guds manns seng og lukket efter ham og gikk ut.
22 Ta kira mijinta ta ce, “Ina roƙonka ka aika mini da ɗaya daga cikin bayi da kuma jaka, don in yi sauri in je wurin mutumin Allah in dawo.”
Så kalte hun på sin mann og sa: Send en av drengene til mig med en aseninne! Så vil jeg skynde mig avsted til den Guds mann og så komme tilbake.
23 Sai ya ce, “Me zai kai ki wurinsa, ai, yau ba Sabon Wata ba ne ko ranar Asabbaci?” Sai ta ce, “Ba kome.”
Han sa: Hvorfor vil du gå til ham idag? Det er jo hverken nymåne eller sabbat. Men hun sa: La mig bare gå!
24 Sai ta sa wa jakar sirdi ta ce wa bawanta, “Yi ta kora mini jakar, kada ka sassauta, sai na faɗa maka.”
Så lot hun aseninnen sale og sa til sin dreng: Led den og gå avsted, stans mig ikke mens jeg rider, uten jeg sier dig til!
25 Ta haka ta kama hanya ta tafi wurin mutumin Allah a Dutsen Karmel. Da ya hange ta daga nesa, sai mutumin Allah ya ce wa bawansa Gehazi, “Duba! Ga mutuniyar Shunam nan can!
Så drog hun avsted og kom til den Guds mann på Karmel-fjellet. Da den Guds mann så henne et stykke borte, sa han til sin dreng Gehasi: Se, der kommer konen fra Sunem.
26 Ka yi gudu ka tarye ta ka tambaye ta, ‘Lafiyarki? Mijinki yana nan lafiya? Yaronki yana nan lafiya?’” Ta amsa ta ce, “Kome lafiya yake.”
Spring henne nu i møte og si til henne: Står det vel til med dig og med din mann og med barnet? Hun svarte: Ja, det står vel til.
27 Da ta isa wurin mutumin Allah a dutsen, sai ta kama ƙafafunsa. Sai Gehazi ya zo don yă ture ta, amma mutumin Allah ya ce, “Ka bar ta! Tana cikin baƙin ciki ƙwarai, amma Ubangiji ya ɓoye mini, bai kuma faɗa mini me ya sa ba.”
Men da hun kom op på fjellet til den Guds mann, omfavnet hun hans føtter; da gikk Gehasi frem og vilde støte henne bort, men den Guds mann sa: La henne være! For hun har en stor hjertesorg; men Herren har skjult det for mig og ikke latt mig få vite det.
28 Sai ta tambaya shi ta ce, “Na roƙe ka ɗa ne, ranka yă daɗe? Ba na ce maka, ‘Kada ka sa in fara bege ba’?”
Hun sa: Har jeg vel bedt min herre om en sønn? Sa jeg ikke: Du må ikke narre mig?
29 Elisha ya ce wa Gehazi, “Ka yi ɗamara, ka ɗauki sandana ka ruga a guje. Idan ka sadu da wani, kada ka gaishe shi, idan kuma wani ya gaishe ka, kada ka amsa. Ka shimfiɗa sandana a fuskar yaron.”
Da sa han til Gehasi: Omgjord dine lender og ta min stav i hånden og gå avsted! Møter du nogen, så hils ikke på ham, og hilser nogen på dig, så svar ham ikke, og legg min stav på guttens ansikt.
30 Amma mahaifiyar yaron ta ce, “Muddin Ubangiji yana raye, kai kuma kana a raye, ba zan bar ka ba.” Saboda haka ya tashi ya bi ta.
Men guttens mor sa: Så sant Herren lever, og så sant du selv lever: Jeg forlater dig ikke. Da stod han op og fulgte med henne.
31 Gehazi ya yi gaba, ya shimfiɗa sandan a fuskar yaron, amma babu motsi, babu alamar rai. Saboda haka Gehazi ya koma ya taryi Elisha, ya faɗa masa, “Yaron bai tashi ba.”
Gehasi gikk i forveien og la staven på guttens ansikt; men det hørtes ikke en lyd og viste sig ikke noget tegn til at han merket noget. Så vendte han tilbake og gikk Elisa i møte og fortalte ham det og sa: Gutten våknet ikke.
32 Da Elisha ya isa gidan, sai ga gawar yaron kwance a kan gadonsa.
Og da Elisa kom til huset, fikk han se at gutten lå død på hans seng.
33 Sai ya shiga, ya rufe ƙofa, daga shi sai yaron, ya kuma yi addu’a ga Ubangiji.
Så gikk han inn og lukket døren til og bad til Herren.
34 Sa’an nan ya hau gadon yă kwanta a bisa yaron, ya miƙe a kansa, baki da baki, ido da ido, hannu da hannu. Yayinda ya miƙe kansa a kan yaron, sai jikin yaron ya ɗau ɗumi.
Derefter steg han op og la sig over barnet med sin munn mot dets munn og sine øine mot dets øine og sine hender på dets hender, og da han således bøide sig over barnet, blev dets legeme varmt.
35 Elisha ya tashi, ya yi ta kai komo a cikin ɗakin. Sa’an nan ya sāke koma kan gadon yă miƙe a kan yaron, sai yaron ya yi atishawa sau bakwai, ya kuma buɗe idanunsa.
Så stod han op igjen og gikk en gang frem og tilbake i kammeret; derefter steg han atter op og bøide sig over gutten; da nøs gutten syv ganger og slo øinene op.
36 Elisha ya kira Gehazi ya ce, “Kirawo mutuniyar Shunam.” Ya kuwa kira ta. Sa’ad da ta zo, sai Elisha ya ce mata, “Ɗauki ɗanki.”
Da kalte han på Gehasi og sa: Kall på den sunamittiske kone! Han kalte på henne, og da hun kom inn til ham, sa han: Ta din sønn!
37 Sai ta shiga, ta fāɗi a ƙafafunsa ta rusuna har ƙasa. Sa’an nan ta ɗauki ɗanta ta fita.
Og hun kom og falt ned for hans føtter og bøide sig til jorden; så tok hun sin sønn og gikk ut.
38 Sai Elisha ya koma Gilgal, a can kuwa ana yunwa a yankin. Yayinda ƙungiyar annabawa suke tattaunawa da shi, sai ya ce wa Gehazi bawansa, “Ka sa babban tukunya a wuta, ka yi wa mutanen nan fate.”
Elisa vendte tilbake til Gilgal; det var dengang hungersnød i landet, og da profetenes disipler engang satt der hos ham, sa han til sin dreng: Sett den store gryte over og kok en rett mat for profetenes disipler!
39 Ɗaya daga cikin mutanen ya shiga gona don neman ganyaye, ya kuwa sami kabewar jeji. Ya tsinko’ya’yanta cike da shafin rigarsa. Da ya dawo, sai ya yayyanka su ya zuba a cikin tukunyar faten, ko da yake ba wanda ya san ko mene ne.
Da gikk en av dem ut på marken for å sanke urter, og han fant en vill slyngplante og sanket av den ville gresskar, sin kappe full, og da han kom inn, skar han dem op i matgryten; for de kjente ikke til dem.
40 Sai aka zuba wa mutanen faten, amma da suka fara ci, sai suka yi ihu suna cewa, “Ya mutumin Allah, akwai dafi a cikin tukunyan nan!” Suka kuwa kāsa ci.
Så øste de op for mennene forat de skulde ete; men da de begynte å ete av retten, skrek de op og ropte: Det er død i gryten, du Guds mann! Og de kunde ikke ete.
41 Elisha ya ce, “Samo mini ɗan gari.” Aka kawo masa ya kuma sa a cikin tukunyan ya ce, “Raba wa mutanen su ci.” Ya kasance kuwa babu wani abin damuwa a tukunyar.
Da sa han: Hent noget mel! Og han kastet det i gryten og sa: Øs op for folket, så de kan få ete! Og da var det ikke mere noget skadelig i gryten.
42 Sai ga wani mutum ya zo daga Ba’al-Shalisha, ya kawo wa Elisha dunƙulen burodi guda ashirin na sha’ir da aka gasa daga nunan fari na hatsi, tare da kawunan sababbin hatsi. Sai Elisha ya ce, “Ka ba mutanen su ci.”
Engang kom det en mann fra Ba'al-Salisa og han hadde med til den Guds mann brød som var bakt av førstegrøden, tyve byggbrød, og nyhøstet korn i sin pose. Da sa Elisa: Gi det til folket, så de kan få ete!
43 Sai bawansa ya ce, “Yaya zan raba wa mutane ɗari wannan?” Amma Elisha ya amsa ya ce, “Ka raba wa mutane su ci, gama haka Ubangiji ya ce, ‘Za su ci har su bar saura.’”
Men hans tjener sa: Hvorledes kan jeg sette dette frem for hundre mann? Han svarte: Gi det til folket, så de kan få ete! For så sier Herren: De skal ete og få tilovers.
44 Sa’an nan ya ajiye a gabansu, suka kuwa ci har suka bar saura, bisa ga maganar Ubangiji.
Så satte han det frem for dem, og de åt og fikk tilovers efter Herrens ord.

< 2 Sarakuna 4 >