< 2 Sarakuna 4 >

1 Matar wani daga ƙungiyar annabawa ta yi wa Elisha kuka ta ce, “Mijina, bawanka, ya mutu, ka kuma san yadda ya girmama Ubangiji. Amma ga shi yanzu mai binsa bashi ya zo yă kwashe’ya’yana maza biyu su zama bayinsa.”
Un viena sieva no praviešu bērnu sievām piesauca Elišu un sacīja: mans vīrs, tavs kalps, ir nomiris, un tu zini, ka tavs kalps To Kungu bijās. Un nu nāk tas parādu dzinējs, gribēdams manus divus bērnus sev ņemt par kalpiem.
2 Elisha ya amsa mata ya ce, “Me kike so in yi miki? Ki faɗa mini, me kike da shi a gidanki?” Sai ta ce, “Baiwarka ba ta da kome a can, sai ɗan tulun man zaitun.”
Un Eliša uz to sacīja: ko man tev būs darīt? Stāsti man, kas ir tavā namā? Un viņa sacīja: tavai kalponei nav it nekā namā, kā tikai krūze eļļas.
3 Elisha ya ce, “Ki je wurin dukan maƙwabtanki, ki nemi tulunan da babu kome a ciki. Kada ki nemo kaɗan kawai.
Tad viņš sacīja: ej, aizņemies traukus no citiem, no visiem saviem kaimiņiem lūdz tukšus traukus labu pulku.
4 Sa’an nan ki shiga ciki, ki kulle ƙofar da ke da’ya’yanki kuke ciki. Ku ɗuɗɗura man a dukan tulunan, sa’ad da kowanne ya cika, sai ki ajiye a gefe.”
Tad ej iekšā un aizslēdz durvis aiz sevis un aiz saviem dēliem un lej visos tanīs traukos un, kas pilni, tos liec pie malas.
5 Ta tashi ta shiga tare da’ya’yanta maza, suka kulle ƙofa.’Ya’yanta suka kawo mata tuluna, ita kuma tana ɗurawa.
Tad tā no viņa aizgāja un aizslēdza durvis aiz sevis un aiz saviem dēliem, tie viņai atnesa tos traukus, un viņa ielēja.
6 Da dukan tulunan suka cika, sai ta ce wa ɗanta, “Kawo mini wani tulu.” Amma ya amsa ya ce, “Ai, ba saura.” Sa’an nan man ya daina zuba.
Un kad tie trauki bija pilni, tad tā sacīja uz savu dēlu: nes man vēl vienu trauku Bet tas uz viņu sacīja: nav vairs trauka Tad tā eļļa nostājās.
7 Sai ta tafi ta faɗa wa mutumin Allah. Shi kuwa ya ce mata, “Tafi, ki sayar da man, ki biya bashinki. Ki biya bukatanki da na’ya’yanki da sauran da ya rage.”
Un tā gāja un to teica tam Dieva vīram. Un viņš sacīja: ej, pārdod to eļļu un maksā savu parādu, un no atlikuma uzturies pati ar saviem dēliem.
8 Wata rana Elisha ya tafi Shunem. Akwai wata mai arziki a can wadda ta gayyace shi cin abinci. Sai ya zama duk lokacin da yake wucewa, yakan tsaya a can don cin abinci.
Un notikās kādu dienu, kad Eliša gāja uz Šunemi, tad tur bija viena bagāta sieva, tā viņu uzlūdza, pie viņas ēst. Un notikās, kad viņš tur cauri staigāja, tad viņš tur iegāja, ēst maizi,
9 Ta ce wa mijinta, “Na san cewa wannan mutum da kullum yake zuwa nan mai tsarki ne na Allah.
Un tā sacīja uz savu vīru: redzi, es atzīstu, ka tas ir svēts Dieva vīrs, kas še vienmēr cauri staigā.
10 Bari mu yi ɗan ɗaki a rufin gida mu kuma sa masa gado da tebur da kujera da kuma fitila. Saboda a duk lokacin da ya zo wurinmu, sai yă sauka a can.”
Taisīsim viņam mazu augšistabiņu ar sienām un liksim viņam tur gultu un galdu un krēslu un lukturi, ka tam pie mums nākot ir, kur ieiet.
11 Wata rana da Elisha ya zo, sai ya haura ɗakinsa ya kwanta.
Un gadījās kādu dienu, kad viņš tur nonāca, tad tas gāja tai augšistabiņā, tur gulēt.
12 Ya ce wa bawansa Gehazi, “Kira mutuniyar Shunam nan.” Sai ya kira ta, ta zo ta tsaya a gabansa.
Un viņš sacīja uz Gehazi, savu puisi, pasauc šo Šunemieti. Un viņš to sauca un tā ienāca pie viņa.
13 Elisha ya ce masa, “Ka ce mata, ‘Kin yi duk wannan ɗawainiya saboda mu. Yanzu, me kike so a yi miki? Kina so mu yi magana a madadinki wa sarki ko babban hafsan mayaƙa?’” Sai ta ce, “A’a, ina da dukan abin da nake bukata a cikin jama’ata.”
Un viņš uz to sacīja: saki jel viņai: redzi, mūsu dēļ tev ir bijušas visas šās rūpes, ko man tev būs darīt? Vai tev kas jārunā pie ķēniņa vai pie karu lielkunga? Bet viņa sacīja: es dzīvoju starp saviem ļaudīm.
14 Sai Elisha ya tambayi Gehazi ya ce, “Me za mu yi mata?” Sai ya amsa ya ce, “Ba ta da ɗa, ga shi kuma mijinta ya tsufa.”
Tad viņš sacīja ko tad lai es viņai daru? Un Gehazis sacīja taču gan, viņai nav dēla un viņas vīrs ir vecs.
15 Sai Elisha ya ce, “Ka kira ta.” Sai ya kira ta, ta zo ta tsaya a bakin ƙofa.
Tad viņš sacīja pasauc viņu. Un tas viņu sauca, un tā ienāca durvīs.
16 Elisha ya ce mata, “War haka baɗi, za ki riƙe ɗa na kanki.” Sai ta ce masa, “A’a, ranka yă daɗe, mutumin Allah, kada ka ruɗi baiwarka!”
Un viņš sacīja: nākošā gadā ap šo laiku tu skūpstīsi dēlu. Bet tā sacīja: ne tā, mans kungs tu Dieva vīrs! Nemelo tu savai kalponei.
17 Amma matan ta yi ciki, a shekara ta biye kuwa a daidai lokacin, sai ta haifi ɗa kamar yadda Elisha ya faɗa mata.
Un tā sieva tapa grūta un dzemdēja dēlu otrā gadā ap to pašu laiku, kā Eliša uz viņu bija runājis.
18 Yaron ya yi girma, wata rana sai ya tafi wurin mahaifinsa, wanda yake tare da masu girbi.
Kad nu tas bērns paauga, tad tas kādu dienu gāja ārā pie sava tēva pie pļāvējiem.
19 Ba zato sai ya ce wa mahaifinsa, “Wayyo! Kaina yana mini ciwo! Kaina yana mini ciwo!” Sai mahaifinsa ya ce wa bawansa, “Kai shi wurin mahaifiyarsa.”
Un tas sacīja uz savu tēvu: vai mana galva, mana galva! Un viņš sacīja puisim: nes to pie viņa mātes.
20 Bayan bawan ya ɗaga shi ya kai wurin mahaifiyarsa, sai yaron ya zauna a cinyarta har tsakar rana, sa’an nan ya mutu.
Un tas to ņēma un nesa pie viņa mātes, un tā to ņēma savā klēpī līdz pusdienai, tad tas nomira.
21 Sai ta haura ta shimfiɗa shi a gadon mutumin Allah, ta rufe ƙofar, ta fita.
Un tā gāja augšām un to nolika Tā Dieva vīra gultā un to ieslēdza un izgāja,
22 Ta kira mijinta ta ce, “Ina roƙonka ka aika mini da ɗaya daga cikin bayi da kuma jaka, don in yi sauri in je wurin mutumin Allah in dawo.”
Un sauca savu vīru un sacīja: sūti man jel vienu no puišiem un vienu ēzeļa māti, es jāšu pie Tā Dieva vīra un atkal pārnākšu.
23 Sai ya ce, “Me zai kai ki wurinsa, ai, yau ba Sabon Wata ba ne ko ranar Asabbaci?” Sai ta ce, “Ba kome.”
Un viņš sacīja: kāpēc tu šodien iesi pie viņa? Jo nav nedz jauns mēnesis nedz svēta diena. Bet tā sacīja: paliec mierā!
24 Sai ta sa wa jakar sirdi ta ce wa bawanta, “Yi ta kora mini jakar, kada ka sassauta, sai na faɗa maka.”
Un viņa apsedloja ēzeļa māti un sacīja uz savu puisi: dzen steigšus, nekavē mani jājot, kā vien, kad es tev saku.
25 Ta haka ta kama hanya ta tafi wurin mutumin Allah a Dutsen Karmel. Da ya hange ta daga nesa, sai mutumin Allah ya ce wa bawansa Gehazi, “Duba! Ga mutuniyar Shunam nan can!
Tā viņa jāja un nāca pie Tā Dieva vīra uz Karmeļa kalnu. Un kad tas Dieva vīrs no tālienes to redzēja, tad viņš sacīja uz savu puisi Gehazi: redzi, tur ir tā Šunemiete.
26 Ka yi gudu ka tarye ta ka tambaye ta, ‘Lafiyarki? Mijinki yana nan lafiya? Yaronki yana nan lafiya?’” Ta amsa ta ce, “Kome lafiya yake.”
Steidzies jel viņai pretī un saki uz to: vai tev labi klājās, un tavam vīram, un tavam dēlam? Un viņa sacīja: labi gan.
27 Da ta isa wurin mutumin Allah a dutsen, sai ta kama ƙafafunsa. Sai Gehazi ya zo don yă ture ta, amma mutumin Allah ya ce, “Ka bar ta! Tana cikin baƙin ciki ƙwarai, amma Ubangiji ya ɓoye mini, bai kuma faɗa mini me ya sa ba.”
Un tā nāca kalnā pie Tā Dieva vīra un apkampa viņa kājas. Bet Gehazis piegāja to atstumt. Bet tas Dieva vīrs sacīja: liec to mierā, jo viņas dvēsele ir noskumusi, un Tas Kungs man to apslēpis un man nav darījis zināmu.
28 Sai ta tambaya shi ta ce, “Na roƙe ka ɗa ne, ranka yă daɗe? Ba na ce maka, ‘Kada ka sa in fara bege ba’?”
Un viņa sacīja: vai es esmu lūgusi dēlu no sava kunga? Vai es nesacīju: nevil mani?
29 Elisha ya ce wa Gehazi, “Ka yi ɗamara, ka ɗauki sandana ka ruga a guje. Idan ka sadu da wani, kada ka gaishe shi, idan kuma wani ya gaishe ka, kada ka amsa. Ka shimfiɗa sandana a fuskar yaron.”
Tad viņš sacīja uz Gehazi: apjoz savus gurnus un ņem manu zizli savā rokā un ej. Ja tevi kas sastop, tad nesveicini to, un ja kas tevi sveicina, tad neatbildi tam, un liec manu zizli uz tā bērna vaigu.
30 Amma mahaifiyar yaron ta ce, “Muddin Ubangiji yana raye, kai kuma kana a raye, ba zan bar ka ba.” Saboda haka ya tashi ya bi ta.
Bet tā bērna māte sacīja: tik tiešām kā Tas Kungs dzīvs un tava dvēsele dzīva, es tevi neatstāšu. Tad viņš cēlās un tai gāja līdz.
31 Gehazi ya yi gaba, ya shimfiɗa sandan a fuskar yaron, amma babu motsi, babu alamar rai. Saboda haka Gehazi ya koma ya taryi Elisha, ya faɗa masa, “Yaron bai tashi ba.”
Gehazis viņu priekšā bija nogājis un licis to zizli uz tā bērna vaigu, bet tur nebija ne balss nedz samaņas. Tad viņš griezās atpakaļ tam pretī un teica un sacīja: tas bērns nav uzmodies.
32 Da Elisha ya isa gidan, sai ga gawar yaron kwance a kan gadonsa.
Kad nu Eliša ienāca namā, redzi, tad tas bērns gulēja nomiris viņa gultā.
33 Sai ya shiga, ya rufe ƙofa, daga shi sai yaron, ya kuma yi addu’a ga Ubangiji.
Un viņš gāja iekšā un aizslēdza durvis aiz abiem un pielūdza To Kungu.
34 Sa’an nan ya hau gadon yă kwanta a bisa yaron, ya miƙe a kansa, baki da baki, ido da ido, hannu da hannu. Yayinda ya miƙe kansa a kan yaron, sai jikin yaron ya ɗau ɗumi.
Un viņš uzkāpa un nolikās uz to bērnu un lika savu muti un savas acis uz viņa acīm un savas rokas uz viņa rokām, un nogūlās tā pār tā bērna miesām, kamēr tās sasila.
35 Elisha ya tashi, ya yi ta kai komo a cikin ɗakin. Sa’an nan ya sāke koma kan gadon yă miƙe a kan yaron, sai yaron ya yi atishawa sau bakwai, ya kuma buɗe idanunsa.
Un viņš atkal cēlās un gāja istabā reiz šurp un reiz turp un uzkāpa atkal un nogūlās pār to. Tad tas bērns šķaudīja septiņas reizes, pēc tas atdarīja savas acis.
36 Elisha ya kira Gehazi ya ce, “Kirawo mutuniyar Shunam.” Ya kuwa kira ta. Sa’ad da ta zo, sai Elisha ya ce mata, “Ɗauki ɗanki.”
Un viņš sauca Gehazi un sacīja: pasauc to Šunemieti. Un viņš to sauca un tā nāca; tad viņš sacīja: ņem savu bērnu.
37 Sai ta shiga, ta fāɗi a ƙafafunsa ta rusuna har ƙasa. Sa’an nan ta ɗauki ɗanta ta fita.
Tad tā nāca un metās viņam pie kājām un nometās zemē un ņēma savu dēlu un izgāja ārā.
38 Sai Elisha ya koma Gilgal, a can kuwa ana yunwa a yankin. Yayinda ƙungiyar annabawa suke tattaunawa da shi, sai ya ce wa Gehazi bawansa, “Ka sa babban tukunya a wuta, ka yi wa mutanen nan fate.”
Un Eliša gāja atkal uz Gilgalu; un zemē bija bads, un praviešu bērni sēdēja viņa priekšā, un viņš sacīja uz savu puisi: liec to lielo podu pie uguns un vāri ēdienu praviešu bērniem.
39 Ɗaya daga cikin mutanen ya shiga gona don neman ganyaye, ya kuwa sami kabewar jeji. Ya tsinko’ya’yanta cike da shafin rigarsa. Da ya dawo, sai ya yayyanka su ya zuba a cikin tukunyar faten, ko da yake ba wanda ya san ko mene ne.
Tad viens izgāja laukā, zāles lasīt un atrada meža gurķu stīgas un no tām salasīja pilnu klēpi meža gurķu un nāca un tos iegrieza tai ēdiena podā, jo tie tos nepazina.
40 Sai aka zuba wa mutanen faten, amma da suka fara ci, sai suka yi ihu suna cewa, “Ya mutumin Allah, akwai dafi a cikin tukunyan nan!” Suka kuwa kāsa ci.
Un tie ielēja tiem vīriem ēst, un kad tie no tā ēdiena ēda, tad tie brēca un sacīja: nāve podā, tu Dieva vīrs! Un nevarēja to ēst.
41 Elisha ya ce, “Samo mini ɗan gari.” Aka kawo masa ya kuma sa a cikin tukunyan ya ce, “Raba wa mutanen su ci.” Ya kasance kuwa babu wani abin damuwa a tukunyar.
Bet viņš sacīja: atnesiet miltus. Un viņš tos iemeta tai podā un sacīja: lej tiem ļaudīm, lai tie ēd. Tad tur vairs nekā nelaba nebija podā.
42 Sai ga wani mutum ya zo daga Ba’al-Shalisha, ya kawo wa Elisha dunƙulen burodi guda ashirin na sha’ir da aka gasa daga nunan fari na hatsi, tare da kawunan sababbin hatsi. Sai Elisha ya ce, “Ka ba mutanen su ci.”
Un viens vīrs nāca no BaālBalizas un atnesa tam Dieva vīram jaunu maizi, divdesmit miežu maizes un taukšētas vārpas savā kulē. Un viņš sacīja: dodi tiem ļaudīm, lai ēd.
43 Sai bawansa ya ce, “Yaya zan raba wa mutane ɗari wannan?” Amma Elisha ya amsa ya ce, “Ka raba wa mutane su ci, gama haka Ubangiji ya ce, ‘Za su ci har su bar saura.’”
Bet viņa sulainis sacīja: ko es došu simts vīriem? Un viņš sacīja: dod tiem ļaudīm, lai ēd; jo tā saka Tas Kungs: tie ēdīs un vēl atliks.
44 Sa’an nan ya ajiye a gabansu, suka kuwa ci har suka bar saura, bisa ga maganar Ubangiji.
Tad viņš tiem lika priekšā, ka tie ēda, un tur vēl atlika pēc Tā Kunga vārda.

< 2 Sarakuna 4 >