< 2 Sarakuna 3 >

1 Yoram, ɗan Ahab ya zama sarki Isra’ila, a Samariya, a shekara ta goma sha takwas ta mulkin Yehoshafat, sarkin Yahuda, ya kuma yi mulki shekara goma sha biyu.
Joram, Achabs son, vardt Konung öfver Israel i Samarien, uti adertonde årena Josaphats, Juda Konungs; och regerade i tolf år;
2 Yoram ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, amma ba kamar yadda mahaifinsa da mahaifiyarsa suka yi ba. Ya kawar da dutsen tsarkin Ba’al wanda mahaifinsa ya yi.
Och gjorde det ondt varför Herranom, dock icke såsom hans fader och hans moder; ty han kastade bort Baals stöder, som hans fader hade göra låtit.
3 Duk da haka ya manne wa zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta aikata, bai rabu da su ba.
Men han blef vid Jerobeams, Nebats sons, synder, hvilken kom Israel till att synda; och trädde intet derifrå.
4 Mesha, sarkin Mowab yana kiwon tumaki, ya kuma zama tilas yă biya haraji ga sarkin Isra’ila. Saboda haka yakan ba da’yan tumaki dubu ɗari, da kuma gashin raguna dubu ɗari.
Men Mesa, de Moabiters Konung, hade mång får, och han skattade Israels Konunge ull af hundradetusend lamb, och af hundradetusend vädrar.
5 Amma bayan mutuwar Ahab, sai sarkin Mowab ya yi wa sarkin Isra’ila tawaye.
Då nu Achab var död, föll de Moabiters Konung af ifrån Israels Konung.
6 To, a lokacin, Sarki Yoram ya tashi daga Samariya, ya tattara sojoji daga dukan Isra’ila.
Då drog ut på den tiden Konung Joram af Samarien, och skickade hela Israel;
7 Ya kuma aika da wannan saƙo ga Yehoshafat sarkin Yahuda cewa, “Sarkin Mowab ya yi mini tawaye. Za ka tafi tare da ni mu yaƙi Mowab?” Sai sarkin Yahuda ya ce, “I, ina shirye mu tafi. Ai, sojojina sojojinka ne, dawakaina kuma dawakanka ne.”
Och sände bort till Josaphat, Juda Konung, och lät säga honom: De Moabiters Konung är affallen ifrå mig. Kom med mig till att strida emot de Moabiter. Han sade: Jag vill uppkomma; jag är såsom du, och mitt folk såsom ditt folk, och mine hästar såsom dine hästar;
8 Ya ƙara da cewa, “Wace hanya za mu bi?” Sai Yoram ya amsa ya ce, “Ta hanyar jejin Edom.”
Och sade: Hvilken vägen vilje vi draga ditupp? Han sade: Den vägen igenom Edoms öken.
9 Saboda haka sarkin Isra’ila ya fita tare da sarkin Yahuda, da kuma sarkin Edom. Da suka yi kwana bakwai suna ta zagawa, sai sojoji da dabbobi suka rasa ruwan sha.
Alltså drogo åstad Israels Konung, Juda Konung, och Edoms Konung. Och som de omkringdragit hade sju dagsresor, hade hären, och de öker, som med dem voro, intet vatten.
10 Sai sarkin Isra’ila ya ce, “Mene! Ubangiji ya kira mu sarakunan nan uku don kawai yă ba da mu ga Mowab ne?”
Då sade Israels Konung: Ack, ve! Herren hafver dessa tre Konungar församlat, på det han skall gifva dem uti de Moabiters händer.
11 Amma Yehoshafat ya yi tambaya ya ce, “Babu wani annabin Ubangiji a nan da za mu nemi nufin Ubangiji ta wurinsa?” Wani hafsan sarkin Isra’ila ya amsa ya ce, “Ai, akwai Elisha ɗan Shafat, wanda dā ya yi wa Iliya hidima.”
Men Josaphat sade: Är här ingen Herrans Prophet, att vi måge genom honom fråga Herran? Då svarade en ibland Israels Konungs tjenare, och sade: Här är Elisa, Saphats son, hvilken göt vatten på Elia händer.
12 Yehoshafat ya ce, “Maganar Ubangiji tana tare da shi.” Saboda haka sarkin Isra’ila da Yehoshafat da kuma sarkin Edom suka tafi wurin Elisha.
Josaphat sade: Herrans ord är när honom. Alltså drogo neder till honom Israels Konung, och Josaphat, och Edoms Konung.
13 Elisha ya ce wa sarkin Isra’ila, “Ina ruwana da kai? Tafi wurin annabawan mahaifinka da annabawa mahaifiyarka.” Sai sarkin Isra’ila ya ce, “A’a, ai Ubangiji ne ya kira mu, mu sarakunan nan uku don yă bashe mu ga Mowab.”
Då sade Elisa till Israels Konung: Hvad hafver du med mig skaffa? Gack bort till dins faders Propheter, och till dine moders Propheter. Israels Konung sade till honom: Nej; ty Herren hafver församlat dessa tre Konungar, på det han skall gifva dem uti de Moabiters händer.
14 Sai Elisha ya ce, “Muddin Ubangiji Maɗaukaki yana a raye, wanda nake bauta, da ba don ina ganin girman Yehoshafat Sarkin Yahuda ba, da ko kallonka ba zan yi ba.
Elisa sade: Så sant som Herren Zebaoth lefver, för hvilkom jag står, om jag icke ansåge Josaphat, Juda Konung, jag ville icke anse dig eller akta dig.
15 Amma yanzu, a kawo mini makaɗin garaya.” Yayinda makaɗin garayan yake kiɗa, ikon Ubangiji ya sauko a kan Elisha
Så låter nu en spelman komma hit. Och då spelmannen spelade på strängerna, kom Herrans hand öfver honom;
16 ya kuma ce, “Ga abin da Ubangiji ya ce, zan cika kwarin nan da tafkunan ruwa.
Och han sade: Detta säger Herren: Görer grafver vid denna bäcken här och der.
17 Gama ga abin da Ubangiji ya ce, ko da yake babu iska, ko ruwan sama, duk da haka kwarin nan zai cika da ruwa, har ku da dabbobinku da kuma sauran dabbobi ku sha.
Förty så säger Herren: I skolen intet väder eller regn se; likväl skall bäcken varda full med vatten, så att I, och edart folk, och edra öker skola få dricka.
18 Wannan abu mai sauƙi ne a wurin Ubangiji; zai kuma ba da Mowab a gare ku.
Dertill är detta en ringa ting för Herranom; han skall ock gifva de Moabiter i edra händer;
19 Za ku ci kowane birni mai katanga, da kowane babban gari. Za ku sare kowane itace mai kyau, ku kuma tattoshe maɓuɓɓugan ruwa. Za ku kuma yi amfani da duwatsu ku lalatar da kowace gona mai kyau.”
Så att I skolen slå alla fasta städer, och alla utvalda städer, och skolen omkullhugga all god trä, och skolen förstoppa alla vattubrunnar, och skolen förderfva alla goda åkrar med stenar.
20 Kashegari, daidai lokacin hadaya, sai ga ruwa yana gangarowa daga gefen Edom! Ƙasar kuwa ta cika da ruwa.
Om morgonen, då man spisoffer offrade, si, då kom ett vatten på den vägen ifrån Edom, och fyllde landet med vatten.
21 To, dukan Mowabawa suka ji cewa sarakuna suna tafe don su yaƙe su; saboda haka aka kira kowane namiji, babba da yaro, wanda ya isa ɗaukan makami, aka jera su a bakin iyaka.
Då nu de Moabiter hörde, att Konungarna drogo upp till att strida emot dem, kallade de tillhopa alla, som vuxne voro att bära vapen, och derutöfver, och drogo intill gränson.
22 Da suka tashi da sassafe, rana tana haska ruwa. Sai ruwan ya yi ja kamar jini a idanun Mowabawan da suke a ƙetare.
Och som de om morgonen bittida uppstode, och solen uppgick öfver vattnet, tyckte de Moabiter, att vattnet emot dem var rödt såsom blod;
23 Sai suka ce, “Jini ne! Ba shakka sarakunan nan sun yaƙe juna, suka karkashe juna. Ya Mowabawa, mu tafi mu kwashi ganima!”
Och de sade: Det är blod; Konungarna hafva slagits inbördes med svärd, och den ene hafver slagit den andra. Nu Moab, statt upp, och tag byte.
24 Amma da Mowabawa suka isa sansanin Isra’ila, sai Isra’ilawa suka taso suka auka musu har sai da suka gudu. Isra’ilawa kuwa suka kai musu hari, suka karkashe Mowabawa.
Men då de kommo till Israels lägre, reste Israel upp, och slog de Moabiter, och de flydde för dem; men de kommo in, och slogo Moab;
25 Suka ragargaza garuruwa, kowane mutum kuwa ya jefa dutse a kowane gona mai kyau har sai da aka rufe gonakin gaba ɗaya. Suka tattoshe duk maɓulɓulan ruwa, suka kuma sare duk itace mai kyau. Kir Hareset ne kaɗai aka bari tare da duwatsunsa yadda suke, amma mutanen da suke da majajjawa suka yi wa birnin zobe, suka kai masa hari shi ma.
Bröto städerna neder, och hvar och en kastade sin sten på alla goda åkrar, och uppfyllde dem, och förstoppade alla vattubrunnar, och fällde all god trä, tilldess att allenast stenarna i tegelmuren qvare blefvo; och de kringhvärfde staden med slungor, och slogo honom.
26 Da sarkin Mowab ya ga yaƙi ya rinjaye shi, sai ya ɗauki mutane masu takobi ɗari bakwai, ya ratsa zuwa wajen sarkin Edom, amma ba su yi nasara ba.
Då de Moabiters Konung såg att striden vardt honom för stark, tog han sjuhundrade män till sig, som svärd utdrogo, till att slå ut emot Edoms Konung; men de kunde icke.
27 Sa’an nan ya ɗauki ɗansa na fari, wanda zai gāje shi, ya yi hadaya da shi a bisa katangan birnin. Isra’ilawa suka firgita ƙwarai; sai suka janye suka koma ƙasarsu.
Då tog han sin första son, som i hans stad skulle Konung vordit, och offrade honom till ett bränneoffer på muren. Då kom en stor vrede öfver Israel; så att de drogo ifrå honom, och vände till landet igen.

< 2 Sarakuna 3 >