< 2 Sarakuna 3 >
1 Yoram, ɗan Ahab ya zama sarki Isra’ila, a Samariya, a shekara ta goma sha takwas ta mulkin Yehoshafat, sarkin Yahuda, ya kuma yi mulki shekara goma sha biyu.
Joram, hijo de Acab, se convirtió en rey de Israel en Samaria en el año dieciocho del gobierno de Josafat, rey de Judá; y fue rey por doce años.
2 Yoram ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, amma ba kamar yadda mahaifinsa da mahaifiyarsa suka yi ba. Ya kawar da dutsen tsarkin Ba’al wanda mahaifinsa ya yi.
Hizo lo malo ante los ojos del Señor; pero no como su padre y su madre, porque quitó la columna de piedra de Baal que su padre había hecho.
3 Duk da haka ya manne wa zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta aikata, bai rabu da su ba.
Pero aún así él cometió los mismos pecados que Jeroboam, el hijo de Nebat, e hizo que Israel pecara y no se apartó de ellos.
4 Mesha, sarkin Mowab yana kiwon tumaki, ya kuma zama tilas yă biya haraji ga sarkin Isra’ila. Saboda haka yakan ba da’yan tumaki dubu ɗari, da kuma gashin raguna dubu ɗari.
Mesa, rey de Moab, era un criador de ovejas; y pagaba regularmente al rey de Israel la lana de cien mil corderos y cien mil ovejas.
5 Amma bayan mutuwar Ahab, sai sarkin Mowab ya yi wa sarkin Isra’ila tawaye.
Pero cuando Acab murió, el rey de Moab se rebeló contra la autoridad del rey de Israel.
6 To, a lokacin, Sarki Yoram ya tashi daga Samariya, ya tattara sojoji daga dukan Isra’ila.
En ese momento, el rey Joram salió de Samaria y reunió a todo Israel en orden de combate.
7 Ya kuma aika da wannan saƙo ga Yehoshafat sarkin Yahuda cewa, “Sarkin Mowab ya yi mini tawaye. Za ka tafi tare da ni mu yaƙi Mowab?” Sai sarkin Yahuda ya ce, “I, ina shirye mu tafi. Ai, sojojina sojojinka ne, dawakaina kuma dawakanka ne.”
Entonces envió a Josafat, rey de Judá, diciendo: El rey de Moab se ha rebelado contra mi autoridad: ¿irás conmigo a hacer la guerra a Moab? Y él dijo: Iré contigo; yo soy como tú, mi pueblo como tu pueblo y mis caballos como tus caballos.
8 Ya ƙara da cewa, “Wace hanya za mu bi?” Sai Yoram ya amsa ya ce, “Ta hanyar jejin Edom.”
Y él dijo: ¿Por dónde vamos? Y él respondió en respuesta: Por el desierto de Edom.
9 Saboda haka sarkin Isra’ila ya fita tare da sarkin Yahuda, da kuma sarkin Edom. Da suka yi kwana bakwai suna ta zagawa, sai sojoji da dabbobi suka rasa ruwan sha.
Entonces el rey de Israel fue con el rey de Judá y con el rey de Edom durante siete días, y no había agua para el ejército ni para las bestias que tenían con ellos.
10 Sai sarkin Isra’ila ya ce, “Mene! Ubangiji ya kira mu sarakunan nan uku don kawai yă ba da mu ga Mowab ne?”
Y el rey de Israel dijo: Aquí hay problemas: porque el Señor ha reunido a estos tres reyes para entregarlos en las manos de Moab.
11 Amma Yehoshafat ya yi tambaya ya ce, “Babu wani annabin Ubangiji a nan da za mu nemi nufin Ubangiji ta wurinsa?” Wani hafsan sarkin Isra’ila ya amsa ya ce, “Ai, akwai Elisha ɗan Shafat, wanda dā ya yi wa Iliya hidima.”
Pero Josafat dijo: ¿No hay profeta del Señor aquí, a través de quien podamos obtener instrucciones del Señor? Y uno de los hombres del rey de Israel dijo en respuesta: Eliseo, hijo de Safat, está aquí y fue el siervo de Elías.
12 Yehoshafat ya ce, “Maganar Ubangiji tana tare da shi.” Saboda haka sarkin Isra’ila da Yehoshafat da kuma sarkin Edom suka tafi wurin Elisha.
Y Josafat dijo: La palabra del Señor está con él. Entonces el rey de Israel y Josafat y el rey de Edom fueron adonde estaba él.
13 Elisha ya ce wa sarkin Isra’ila, “Ina ruwana da kai? Tafi wurin annabawan mahaifinka da annabawa mahaifiyarka.” Sai sarkin Isra’ila ya ce, “A’a, ai Ubangiji ne ya kira mu, mu sarakunan nan uku don yă bashe mu ga Mowab.”
Pero Eliseo dijo al rey de Israel: ¿Qué tengo que hacer contigo? Ve a los profetas de tu padre y de tu madre. Y el rey de Israel dijo: No; porque el Señor ha reunido a estos tres reyes para entregarlos en las manos de Moab.
14 Sai Elisha ya ce, “Muddin Ubangiji Maɗaukaki yana a raye, wanda nake bauta, da ba don ina ganin girman Yehoshafat Sarkin Yahuda ba, da ko kallonka ba zan yi ba.
Entonces Eliseo dijo: Por la vida del Señor de los ejércitos cuyo siervo soy, si no fuera por el respeto que tengo por Josafat, rey de Judá, no te miraría ni te vería.
15 Amma yanzu, a kawo mini makaɗin garaya.” Yayinda makaɗin garayan yake kiɗa, ikon Ubangiji ya sauko a kan Elisha
Pero ahora, consígame músico, y sucederá que mientras el hombre está tocando, la mano del Señor vendrá sobre mí y le daré la palabra del Señor: y obtuvieron un músico, y mientras el hombre tocaba, la mano del Señor estaba sobre él.
16 ya kuma ce, “Ga abin da Ubangiji ya ce, zan cika kwarin nan da tafkunan ruwa.
Y él dijo: Él Señor dice: Haré este valle lleno de pozos de agua.
17 Gama ga abin da Ubangiji ya ce, ko da yake babu iska, ko ruwan sama, duk da haka kwarin nan zai cika da ruwa, har ku da dabbobinku da kuma sauran dabbobi ku sha.
Porque el Señor dice: Aunque no veas viento ni lluvia, el valle estará lleno de agua, y tú y tus ejércitos y tus bestias beberán.
18 Wannan abu mai sauƙi ne a wurin Ubangiji; zai kuma ba da Mowab a gare ku.
Y esto será solo una pequeña cosa para el Señor: además él entregará a los moabitas en tus manos.
19 Za ku ci kowane birni mai katanga, da kowane babban gari. Za ku sare kowane itace mai kyau, ku kuma tattoshe maɓuɓɓugan ruwa. Za ku kuma yi amfani da duwatsu ku lalatar da kowace gona mai kyau.”
Y debes destruir cada pueblo amurallado, talar cada árbol frutal, y tapar cada manantial de agua, y hacer que toda la tierra de cultivo sea áspera con piedras.
20 Kashegari, daidai lokacin hadaya, sai ga ruwa yana gangarowa daga gefen Edom! Ƙasar kuwa ta cika da ruwa.
Ahora, en la mañana, aproximadamente cuando se hizo la ofrenda, vieron que el agua fluía desde la dirección de Edom hasta que el país estaba lleno de agua.
21 To, dukan Mowabawa suka ji cewa sarakuna suna tafe don su yaƙe su; saboda haka aka kira kowane namiji, babba da yaro, wanda ya isa ɗaukan makami, aka jera su a bakin iyaka.
Y todo Moab, oyendo que los reyes habían venido a hacerles la guerra, reunieron a todos los que podían tomar las armas y avanzaron hasta el borde del país.
22 Da suka tashi da sassafe, rana tana haska ruwa. Sai ruwan ya yi ja kamar jini a idanun Mowabawan da suke a ƙetare.
Y temprano en la mañana se levantaron, cuando el sol brillaba sobre el agua, y vieron que el agua estaba frente a ellos tan roja como la sangre.
23 Sai suka ce, “Jini ne! Ba shakka sarakunan nan sun yaƙe juna, suka karkashe juna. Ya Mowabawa, mu tafi mu kwashi ganima!”
Entonces ellos dijeron: Esto es sangre: está claro que la destrucción ha venido sobre los reyes; han estado luchando entre sí: ahora ven, Moab, tomemos sus bienes.
24 Amma da Mowabawa suka isa sansanin Isra’ila, sai Isra’ilawa suka taso suka auka musu har sai da suka gudu. Isra’ilawa kuwa suka kai musu hari, suka karkashe Mowabawa.
Pero cuando llegaron a los campamentos de Israel, los israelitas salieron e hicieron un violento ataque a los moabitas, para que huyeran delante de ellos; los persiguieron y los mataron;
25 Suka ragargaza garuruwa, kowane mutum kuwa ya jefa dutse a kowane gona mai kyau har sai da aka rufe gonakin gaba ɗaya. Suka tattoshe duk maɓulɓulan ruwa, suka kuma sare duk itace mai kyau. Kir Hareset ne kaɗai aka bari tare da duwatsunsa yadda suke, amma mutanen da suke da majajjawa suka yi wa birnin zobe, suka kai masa hari shi ma.
Destruyendo los pueblos, cubriendo cada campo de cultivo con piedras, tapando todos los manantiales de agua y cortando todos los árboles frutales; siguieron conduciendo Moab delante de ellos hasta que solo quedó en pie en Kir-hareset pero los honderos hicieron llover piedras sobre ella y la destruyeron.
26 Da sarkin Mowab ya ga yaƙi ya rinjaye shi, sai ya ɗauki mutane masu takobi ɗari bakwai, ya ratsa zuwa wajen sarkin Edom, amma ba su yi nasara ba.
Y cuando el rey de Moab vio que la lucha iba contra él, llevó consigo a setecientos hombres armados con espadas, con la idea de forzar el camino hacia el rey de Edom, pero no pudieron hacerlo.
27 Sa’an nan ya ɗauki ɗansa na fari, wanda zai gāje shi, ya yi hadaya da shi a bisa katangan birnin. Isra’ilawa suka firgita ƙwarai; sai suka janye suka koma ƙasarsu.
Luego tomó a su hijo mayor, que habría sido rey después de él, ofreciéndolo como ofrenda quemada en la pared. Y hubo gran ira contra Israel; Y se fueron de allí, de vuelta a su país.