< 2 Sarakuna 3 >

1 Yoram, ɗan Ahab ya zama sarki Isra’ila, a Samariya, a shekara ta goma sha takwas ta mulkin Yehoshafat, sarkin Yahuda, ya kuma yi mulki shekara goma sha biyu.
И Иорам сын Ахаавов воцарися над Израилем в Самарии, в лето осмоенадесять Иосафата царя Иудина, и царствова лет дванадесять,
2 Yoram ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, amma ba kamar yadda mahaifinsa da mahaifiyarsa suka yi ba. Ya kawar da dutsen tsarkin Ba’al wanda mahaifinsa ya yi.
и сотвори лукавое пред очима Господнима: обаче не якоже отец его и не якоже мати его: и разруши капища Ваалова, яже сотвори отец его:
3 Duk da haka ya manne wa zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta aikata, bai rabu da su ba.
обаче ко греху Иеровоама сына Наватова, иже введе во грех Израиля, прилепися и не отступи от него.
4 Mesha, sarkin Mowab yana kiwon tumaki, ya kuma zama tilas yă biya haraji ga sarkin Isra’ila. Saboda haka yakan ba da’yan tumaki dubu ɗari, da kuma gashin raguna dubu ɗari.
И Моса царь Моавль бе нокид и даяше дань царю Израилеву, сто тысящ агнцев и сто тысящ овнов с рунами.
5 Amma bayan mutuwar Ahab, sai sarkin Mowab ya yi wa sarkin Isra’ila tawaye.
И бысть по умертвии Ахаавли и отвержеся царь Моавль царя Израилева.
6 To, a lokacin, Sarki Yoram ya tashi daga Samariya, ya tattara sojoji daga dukan Isra’ila.
И изыде царь Иорам во дни оны от Самарии и согляда Израиля,
7 Ya kuma aika da wannan saƙo ga Yehoshafat sarkin Yahuda cewa, “Sarkin Mowab ya yi mini tawaye. Za ka tafi tare da ni mu yaƙi Mowab?” Sai sarkin Yahuda ya ce, “I, ina shirye mu tafi. Ai, sojojina sojojinka ne, dawakaina kuma dawakanka ne.”
и иде, и посла ко Иосафату царю Иудину, глаголя: царь Моавль отвержеся мене: идеши ли со мною на брань на Моава? И рече: взыду: сице мне, якоже и тебе: якоже людие мои, людие твои: якоже кони мои, кони твои.
8 Ya ƙara da cewa, “Wace hanya za mu bi?” Sai Yoram ya amsa ya ce, “Ta hanyar jejin Edom.”
И рече: киим путем взыдем? И рече: путем пустыни Едомския.
9 Saboda haka sarkin Isra’ila ya fita tare da sarkin Yahuda, da kuma sarkin Edom. Da suka yi kwana bakwai suna ta zagawa, sai sojoji da dabbobi suka rasa ruwan sha.
И иде царь Израилев и царь Иудин и царь Едомль, и идоша путем седмь дний: и не бе полку воды и скотом сущым с ними.
10 Sai sarkin Isra’ila ya ce, “Mene! Ubangiji ya kira mu sarakunan nan uku don kawai yă ba da mu ga Mowab ne?”
И рече отроком своим царь Израилев: о, яко созва Господь три сия цари идущыя предати их в руце Моавли.
11 Amma Yehoshafat ya yi tambaya ya ce, “Babu wani annabin Ubangiji a nan da za mu nemi nufin Ubangiji ta wurinsa?” Wani hafsan sarkin Isra’ila ya amsa ya ce, “Ai, akwai Elisha ɗan Shafat, wanda dā ya yi wa Iliya hidima.”
И рече Иосафат к нему царь Иудин: есть ли зде пророк Господень, и вопросим Господа им? И отвеща един отрок царя Израилева и рече: зде есть Елиссей сын Сафатов, иже возливаше воду на руце Илиине.
12 Yehoshafat ya ce, “Maganar Ubangiji tana tare da shi.” Saboda haka sarkin Isra’ila da Yehoshafat da kuma sarkin Edom suka tafi wurin Elisha.
И рече Иосафат: есть с ним глагол Господень. И сниде к нему царь Израилев и Иосафат царь Иудин и царь Едомль.
13 Elisha ya ce wa sarkin Isra’ila, “Ina ruwana da kai? Tafi wurin annabawan mahaifinka da annabawa mahaifiyarka.” Sai sarkin Isra’ila ya ce, “A’a, ai Ubangiji ne ya kira mu, mu sarakunan nan uku don yă bashe mu ga Mowab.”
И рече Елиссей ко царю Израилеву: что мне и тебе? Иди ко пророком отца твоего и ко пророком матере твоея. И рече ему царь Израилев: еда созва Господь три цари, еже предати я в руце Моавли?
14 Sai Elisha ya ce, “Muddin Ubangiji Maɗaukaki yana a raye, wanda nake bauta, da ba don ina ganin girman Yehoshafat Sarkin Yahuda ba, da ko kallonka ba zan yi ba.
И рече Елиссей: жив Господь Сил емуже предстою пред Ним, яко аще бых не лице Иосафата царя Иудина аз приял, то воззрел ли бых на тя, и видел ли бых тя?
15 Amma yanzu, a kawo mini makaɗin garaya.” Yayinda makaɗin garayan yake kiɗa, ikon Ubangiji ya sauko a kan Elisha
И ныне приведи ми певца. И бысть егда воспеваше певец, и бысть на нем рука Господня,
16 ya kuma ce, “Ga abin da Ubangiji ya ce, zan cika kwarin nan da tafkunan ruwa.
и рече: тако глаголет Господь: сотворите поток сей рвами рвами,
17 Gama ga abin da Ubangiji ya ce, ko da yake babu iska, ko ruwan sama, duk da haka kwarin nan zai cika da ruwa, har ku da dabbobinku da kuma sauran dabbobi ku sha.
яко тако глаголет Господь: не узрите духа, и ниже увидите дождя: и поток сей наполнится воды, и пиете вы и стяжания ваша и скоти ваши:
18 Wannan abu mai sauƙi ne a wurin Ubangiji; zai kuma ba da Mowab a gare ku.
и легко сие пред очима Господнима, и предам Моава в руки вашя,
19 Za ku ci kowane birni mai katanga, da kowane babban gari. Za ku sare kowane itace mai kyau, ku kuma tattoshe maɓuɓɓugan ruwa. Za ku kuma yi amfani da duwatsu ku lalatar da kowace gona mai kyau.”
и поразите всяк град тверд, и всяко древо благо низложите, и всяк источник воды заградите, и всяку часть благу разбиете камением.
20 Kashegari, daidai lokacin hadaya, sai ga ruwa yana gangarowa daga gefen Edom! Ƙasar kuwa ta cika da ruwa.
И бысть заутра восходящей жертве, и се, воды идяху путем Едомским, и исполнися воды земля.
21 To, dukan Mowabawa suka ji cewa sarakuna suna tafe don su yaƙe su; saboda haka aka kira kowane namiji, babba da yaro, wanda ya isa ɗaukan makami, aka jera su a bakin iyaka.
И вси Моавитяне услышаша, яко взыдоша тридесяти царя братися с ними. И возопиша отвсюду препоясаннии оружием и реша: ох: и сташа у предела.
22 Da suka tashi da sassafe, rana tana haska ruwa. Sai ruwan ya yi ja kamar jini a idanun Mowabawan da suke a ƙetare.
И ураниша заутра, и солнце возсия на воды: и виде Моав сопротив воды чермны яко кровь,
23 Sai suka ce, “Jini ne! Ba shakka sarakunan nan sun yaƙe juna, suka karkashe juna. Ya Mowabawa, mu tafi mu kwashi ganima!”
и рече: кровь сия есть от оружия: и бишася царие, и уби муж искренняго своего: и ныне (гряди) на корысти, Моаве.
24 Amma da Mowabawa suka isa sansanin Isra’ila, sai Isra’ilawa suka taso suka auka musu har sai da suka gudu. Isra’ilawa kuwa suka kai musu hari, suka karkashe Mowabawa.
И внидоша в полк Израилев, Израилтяне же восташа. И избиша Моавлян: и побегоша от лица их: и внидоша входяще и биюще Моава,
25 Suka ragargaza garuruwa, kowane mutum kuwa ya jefa dutse a kowane gona mai kyau har sai da aka rufe gonakin gaba ɗaya. Suka tattoshe duk maɓulɓulan ruwa, suka kuma sare duk itace mai kyau. Kir Hareset ne kaɗai aka bari tare da duwatsunsa yadda suke, amma mutanen da suke da majajjawa suka yi wa birnin zobe, suka kai masa hari shi ma.
и грады разбиша, и всяку часть благу навергоша мужие камением, и наполниша ю, и всяк источник заградиша, и всяко древо благо изсекоша, донележе оставиша камение стен разбиено: и обступиша пращницы и разбиша его.
26 Da sarkin Mowab ya ga yaƙi ya rinjaye shi, sai ya ɗauki mutane masu takobi ɗari bakwai, ya ratsa zuwa wajen sarkin Edom, amma ba su yi nasara ba.
И виде царь Моавль, яко укрепися над ним брань, и взя с собою седмь сот мужей со обнаженным оружием, еже просещися ко царю Едомску: и не возмогоша.
27 Sa’an nan ya ɗauki ɗansa na fari, wanda zai gāje shi, ya yi hadaya da shi a bisa katangan birnin. Isra’ilawa suka firgita ƙwarai; sai suka janye suka koma ƙasarsu.
И поят сына своего первенца, егоже воцари вместо себе, и вознесе его во всесожжение на стене: и бысть раскаяние великое во Израили: и отступиша от него и возвратишася в землю свою.

< 2 Sarakuna 3 >