< 2 Sarakuna 3 >

1 Yoram, ɗan Ahab ya zama sarki Isra’ila, a Samariya, a shekara ta goma sha takwas ta mulkin Yehoshafat, sarkin Yahuda, ya kuma yi mulki shekara goma sha biyu.
Joram, son of Ahab, became king of Israel in the eighteenth year of the reign of King Jehoshaphat of Judah. He reigned in Samaria for twelve years.
2 Yoram ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, amma ba kamar yadda mahaifinsa da mahaifiyarsa suka yi ba. Ya kawar da dutsen tsarkin Ba’al wanda mahaifinsa ya yi.
He did evil in the Lord's sight, but not like his father and mother had done, for he got rid of the stone image of Baal that his father had made.
3 Duk da haka ya manne wa zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta aikata, bai rabu da su ba.
However, he still held on to the sins that Jeroboam, son of Nebat, had made Israel commit—he did not give them up.
4 Mesha, sarkin Mowab yana kiwon tumaki, ya kuma zama tilas yă biya haraji ga sarkin Isra’ila. Saboda haka yakan ba da’yan tumaki dubu ɗari, da kuma gashin raguna dubu ɗari.
Mesha, king of Moab, was a sheep breeder. He used to provide a tribute to the king of Israel of one hundred thousand lambs and the wool of one hundred thousand rams.
5 Amma bayan mutuwar Ahab, sai sarkin Mowab ya yi wa sarkin Isra’ila tawaye.
But after Ahab died, the king of Moab rebelled against the king of Israel.
6 To, a lokacin, Sarki Yoram ya tashi daga Samariya, ya tattara sojoji daga dukan Isra’ila.
Immediately King Joram called up the whole Israelite army and left Samaria.
7 Ya kuma aika da wannan saƙo ga Yehoshafat sarkin Yahuda cewa, “Sarkin Mowab ya yi mini tawaye. Za ka tafi tare da ni mu yaƙi Mowab?” Sai sarkin Yahuda ya ce, “I, ina shirye mu tafi. Ai, sojojina sojojinka ne, dawakaina kuma dawakanka ne.”
On his way he sent a message to Jehoshaphat, king of Judah, saying, “The king of Moab has rebelled against me. Will you join me in an attack on Moab?” Jehoshaphat replied, “Yes, I will join you. You and I are as one, my men and your men are as one, and my horses and your horses are as one.”
8 Ya ƙara da cewa, “Wace hanya za mu bi?” Sai Yoram ya amsa ya ce, “Ta hanyar jejin Edom.”
Then he asked, “Which way shall we go?” “We'll take the road through the desert of Edom,” he replied.
9 Saboda haka sarkin Isra’ila ya fita tare da sarkin Yahuda, da kuma sarkin Edom. Da suka yi kwana bakwai suna ta zagawa, sai sojoji da dabbobi suka rasa ruwan sha.
So the king of Israel, the king of Judah, and the king of Edom set off. Having followed an indirect route for seven days, they ran out of water for their army and for their animals.
10 Sai sarkin Isra’ila ya ce, “Mene! Ubangiji ya kira mu sarakunan nan uku don kawai yă ba da mu ga Mowab ne?”
“What are we doing?” complained the king of Israel. “The Lord has brought us three kings here to hand us over to the Moabites!”
11 Amma Yehoshafat ya yi tambaya ya ce, “Babu wani annabin Ubangiji a nan da za mu nemi nufin Ubangiji ta wurinsa?” Wani hafsan sarkin Isra’ila ya amsa ya ce, “Ai, akwai Elisha ɗan Shafat, wanda dā ya yi wa Iliya hidima.”
But Jehoshaphat asked, “Isn't there a prophet of the Lord here with us? Let us consult the Lord through him.” One of the king of Israel's officers answered, “Elisha, son of Shaphat, is here. He was Elijah's assistant.”
12 Yehoshafat ya ce, “Maganar Ubangiji tana tare da shi.” Saboda haka sarkin Isra’ila da Yehoshafat da kuma sarkin Edom suka tafi wurin Elisha.
Jehoshaphat agreed, “The Lord communicates by him.” So the king of Israel, Jehoshaphat, and the king of Edom went to see him.
13 Elisha ya ce wa sarkin Isra’ila, “Ina ruwana da kai? Tafi wurin annabawan mahaifinka da annabawa mahaifiyarka.” Sai sarkin Isra’ila ya ce, “A’a, ai Ubangiji ne ya kira mu, mu sarakunan nan uku don yă bashe mu ga Mowab.”
Elisha said to the king of Israel, “What have I got to do with you? Go to your own prophets, those of your father and your mother.” But the king of Israel said to him, “No—because it's the Lord who has brought these three kings here to hand them over to the Moabites!”
14 Sai Elisha ya ce, “Muddin Ubangiji Maɗaukaki yana a raye, wanda nake bauta, da ba don ina ganin girman Yehoshafat Sarkin Yahuda ba, da ko kallonka ba zan yi ba.
Elisha replied, “As the Lord Almighty lives, the one I serve, if I didn't respect the fact that Jehoshaphat, king of Judah, is here, I wouldn't even look in your direction or acknowledge you.
15 Amma yanzu, a kawo mini makaɗin garaya.” Yayinda makaɗin garayan yake kiɗa, ikon Ubangiji ya sauko a kan Elisha
Now bring me a musician.” While the musician played, the Lord's power came upon Elisha,
16 ya kuma ce, “Ga abin da Ubangiji ya ce, zan cika kwarin nan da tafkunan ruwa.
and he announced, “This is what the Lord says: This valley will be filled with pools of water. For the Lord says:
17 Gama ga abin da Ubangiji ya ce, ko da yake babu iska, ko ruwan sama, duk da haka kwarin nan zai cika da ruwa, har ku da dabbobinku da kuma sauran dabbobi ku sha.
You won't see any wind, you won't see any rain, but even so this valley will be filled with water. You will drink, and your cattle, and your animals.
18 Wannan abu mai sauƙi ne a wurin Ubangiji; zai kuma ba da Mowab a gare ku.
The Lord views this as something trivial to do; and he will also make you victorious over the Moabites.
19 Za ku ci kowane birni mai katanga, da kowane babban gari. Za ku sare kowane itace mai kyau, ku kuma tattoshe maɓuɓɓugan ruwa. Za ku kuma yi amfani da duwatsu ku lalatar da kowace gona mai kyau.”
You will conquer every fortified town, and every important town. You will chop down every good tree, block up every spring, and spoil every good field by throwing stones on them.”
20 Kashegari, daidai lokacin hadaya, sai ga ruwa yana gangarowa daga gefen Edom! Ƙasar kuwa ta cika da ruwa.
The next day, around the time of the morning sacrifice, water suddenly flowed from the direction of Edom, filling the whole countryside with water.
21 To, dukan Mowabawa suka ji cewa sarakuna suna tafe don su yaƙe su; saboda haka aka kira kowane namiji, babba da yaro, wanda ya isa ɗaukan makami, aka jera su a bakin iyaka.
All the Moabites had heard that the kings had come to attack them. So everyone who could wear a sword, young and old, was called up and went to guard the border.
22 Da suka tashi da sassafe, rana tana haska ruwa. Sai ruwan ya yi ja kamar jini a idanun Mowabawan da suke a ƙetare.
But the next morning when they got up the sun was shining on the water, and to the Moabites on the other side it looked blood red.
23 Sai suka ce, “Jini ne! Ba shakka sarakunan nan sun yaƙe juna, suka karkashe juna. Ya Mowabawa, mu tafi mu kwashi ganima!”
“This is blood!” they said. “The kings and their armies must have attacked and killed each other! Moabites, let's grab the plunder!”
24 Amma da Mowabawa suka isa sansanin Isra’ila, sai Isra’ilawa suka taso suka auka musu har sai da suka gudu. Isra’ilawa kuwa suka kai musu hari, suka karkashe Mowabawa.
But when the Moabites arrived at the Israelite camp, the Israelites ran out and attacked them, and they ran away from them. So the Israelites invaded their country and killed the Moabites.
25 Suka ragargaza garuruwa, kowane mutum kuwa ya jefa dutse a kowane gona mai kyau har sai da aka rufe gonakin gaba ɗaya. Suka tattoshe duk maɓulɓulan ruwa, suka kuma sare duk itace mai kyau. Kir Hareset ne kaɗai aka bari tare da duwatsunsa yadda suke, amma mutanen da suke da majajjawa suka yi wa birnin zobe, suka kai masa hari shi ma.
They destroyed the towns, and each soldier threw stones on every good field until it was covered. They blocked up every spring and chopped down every good tree. Only Kir-haraseth still had its walls, but soldiers using slingshots surrounded it and attacked it as well.
26 Da sarkin Mowab ya ga yaƙi ya rinjaye shi, sai ya ɗauki mutane masu takobi ɗari bakwai, ya ratsa zuwa wajen sarkin Edom, amma ba su yi nasara ba.
When the king of Moab realized he'd lost the battle, he led seven hundred swordsmen in an attempt to break through and attack the king of Edom, but they weren't able to do so.
27 Sa’an nan ya ɗauki ɗansa na fari, wanda zai gāje shi, ya yi hadaya da shi a bisa katangan birnin. Isra’ilawa suka firgita ƙwarai; sai suka janye suka koma ƙasarsu.
So the king of Moab took his firstborn son, who was meant to succeed him, and sacrificed him as a burnt offering on the town wall. Great anger came upon the Israelites, so they left and went back to their own country.

< 2 Sarakuna 3 >