< 2 Sarakuna 25 >
1 A rana ta goma ga wata na goma, a shekara ta tara ta mulkin Zedekiya ne Nebukadnezzar sarkin Babilon tare da dukan rundunan yaƙinsa, ya tasam wa Urushalima. Ya yi sansani a bayan birnin, ya kewaye ta da shirin yaƙi.
Un notikās viņa valdības devītajā gadā desmitā mēnesi, desmitā mēneša dienā, tad Nebukadnecars, Bābeles ķēniņš, nāca ar visu savu karaspēku pret Jeruzālemi un apmeta lēģeri pret to un uztaisīja valni ap to.
2 Haka birnin ta kasance a kewaye har shekara ta goma sha ɗaya ta mulkin Zedekiya.
Un tā pilsēta palika apstāta līdz ķēniņa Cedeķijas vienpadsmitam gadam.
3 A rana ta tara ta watan huɗu, lokacin da yunwa ta yi tsanani a birnin, babu kuma abinci domin mutane su ci.
Un (ceturtā) mēneša devītā (dienā), kad bads pilsētu pārvarēja un iedzīvotājiem vairs nebija maizes,
4 Sai aka huda katanga sa’an nan dukan sojoji suka tsere da dare a ƙofa tsakanin katanga biyu da suke kusa da lambun sarki, ko da yake Babiloniyawa sun kewaye birnin. Suka tsere suka nufi Araba.
Tad ielauzās pilsētā, un visi karavīri bēga naktī pa vārtu ceļu starp abiem mūriem pie ķēniņa dārza, (bet Kaldeji bija pilsētai visapkārt) un ķēniņš bēga pa klajuma ceļu.
5 Amma sojojin Babiloniyawa suka bi sarki, suka cin masa a filayen Yeriko. Dukan sojojinsa kuwa suka rabu da shi suka watse.
Un Kaldeju spēks ķēniņam dzinās pakaļ un to panāca Jērikus klajumā, un viss viņa spēks no viņa izklīda.
6 Aka kama shi, aka kai shi gaban sarkin Babilon a Ribla, inda aka yanke masa hukunci.
Un tie sagrāba ķēniņu un to noveda pie Bābeles ķēniņa uz Riblatu, un turēja tiesu pār viņu.
7 Suka kashe’ya’yan Zedekiya a gabansa, sa’an nan aka ƙwaƙule idanunsa. Suka daure shi da sarƙar tagulla, suka kai shi Babilon.
Un tie nokāva Cedeķijas dēlus priekš viņa acīm un izdūra Cedeķijam acis un to saistīja ar divām vara ķēdēm un to noveda uz Bābeli.
8 A rana ta bakwai na watan biyar, wadda ta zama shekara ta goma sha tara ta mulkin Sarki Nebukadnezzar na Babilon, Nebuzaradan, babban hafsan matsaran sarki, kuma bafadan sarkin Babilon, ya zo Urushalima
Un piektā mēneša septītā dienā (tas bija ķēniņa Nebukadnecara, Bābeles ķēniņa, deviņpadsmitais gads, ) NebuzarAdans, pils karavīru virsnieks, Bābeles ķēniņa kalps, nāca uz Jeruzālemi
9 Ya cinna wa haikalin Ubangiji wuta, da fadan sarki, da kuma dukan gidajen Urushalima. Ya kuma ƙone duk wani gini mai muhimmanci.
Un sadedzināja Tā Kunga namu un ķēniņa namu un visus Jeruzālemes namus, visus lielos namus viņš sadedzināja ar uguni.
10 Dukan mayaƙan Babilon a ƙarƙashin umarnin babban hafsan matsaran sarki, suka rushe katangar Urushalima.
Un viss Kaldeju spēks, kas bija pie pils karavīru virsnieka, noplēsa Jeruzālemes mūrus visapkārt.
11 Nebuzaradan babban hafsan matsaran, ya kwashi waɗanda suka rage a cikin birnin, tare da sauran jama’a, da waɗanda suka miƙa kansu ga sarkin Babilon, ya kai su bauta.
Un tos atlikušos ļaudis, kas bija atlikuši pilsētā, un tos bēgļus, kas bija aizbēguši pie Bābeles ķēniņa, un tautas atlikumu NebuzarAdans, pils karavīru virsnieks, aizveda.
12 Amma hafsan ya bar waɗansu daga cikin mafiya talauci na ƙasar don su yi aiki a lambunan inabi da kuma gonaki.
Bet no zemniekiem pils karavīru virsnieks citus atlicināja par vīna dārzniekiem un arājiem.
13 Babiloniyawan kuma suka sassare ginshiƙan tagulla, da wuraren zama da za a iya matsar da su, da ƙaton kwano mai suna Teku na tagulla da yake a haikalin Ubangiji, suka kwashe tagullan zuwa Babilon.
Un Kaldeji salauzīja tos vara stabus Tā Kunga namā un tos krēslus un to vara jūru Tā Kunga nama, un noveda to varu uz Bābeli.
14 Suka ɗauke tukwane, da manyan cokula, da acibalbal, da kwanoni, da dai dukan kayan da aka yi da tagulla don hidima a haikalin Ubangiji.
Tie paņēma arī tos podus un tās lāpstas un dakšas un kausus un visus vara rīkus pie Dieva nama kalpošanas.
15 Babban hafsan matsaran sarkin ya kwashe har da kwanoni na kwashe garwashin wuta da sauran kwanoni, dukansu kuwa ƙeran zinariya ko azurfa tsatsa ne.
Un pils karavīru virsnieks paņēma tos ogļu traukus un tās bļodas, kas bija tīra zelta un tīra sudraba,
16 Tagullar ginshiƙai biyun nan, da ta ƙaton kwanon da ake ce da shi Teku, da ta dukan amalanke masu riƙe ruwa waɗanda Sarki Solomon ya yi domin haikalin Ubangiji, sun fi gaba a auna su.
Tos divus stabus, to vienu jūru un tos krēslus, ko Salamans bija taisījis Tā Kunga namam. Visu šo trauku varš bija nesverams.
17 Tsawon kowane ginshiƙi, ƙafa ashirin da bakwai ne. Hulunan tagullan da suke ƙwalƙwalin kowane ginshiƙi kuma yana da tsawon ƙafa huɗu da rabi. Kuma aka yi masa ado da saƙa da’ya’yan itace kewaye da shi. Bayan ginshiƙin ma haka yake.
Astoņpadsmit olektis augsts bija viens stabs un uz tā vara kronis un tas kronis bija trīs olektis augsts, un tīkli un granātāboli apkārt kronim bija visi no vara. Un tāpat bija arī tas otrs stabs ar tiem tīkliem.
18 Babban hafsan ya kwashi Serahiya babban firist, da Zefaniya na biye da shi a girma, da matsara ƙofofi uku.
Un pils karavīru virsnieks paņēma augsto priesteri Seraju un otru priesteri Cefaniju un trīs sliekšņa sargus.
19 Daga cikin waɗanda suka rage a birnin, ya ɗauki hafsa mai kula da dakaru, da kuma mashawartan sarki guda biyar. Ya kuma tafi da magatakarda wanda yake babban jami’in soja mai ɗaukan dukan jama’an ƙasar, tare da mutanensa guda sittin waɗanda aka samu a birnin.
Un no pilsētas viņš paņēma vienu kambarjunkuri, kas bija pār karavīriem, un piecus vīrus no tiem, kas vienmēr bija ķēniņa priekšā un kas pilsētā atradās, un karavirsnieka skrīveri, kas zemes ļaudis rīkoja uz karu, un sešdesmit vīrus no zemes ļaudīm, kas pilsētā atradās.
20 Nebuzaradan, babban hafsan, ya kwashe su duka ya kawo su wurin sarkin Babilon a Ribla.
Un NebuzarAdans, pils karavīru virsnieks, tos ņēmis noveda pie Bābeles ķēniņa uz Riblatu.
21 A can Ribla, a ƙasar Hamat, sarkin Babilon ya sa aka kashe su. Haka Yahuda ta tafi bauta daga ƙasarta.
Un Bābeles ķēniņš tos kāva un nokāva Riblatā Hamatas zemē. Tā Jūda tapa aizvests no savas zemes.
22 Nebukadnezzar sarkin Babilon ya zaɓi Gedaliya ɗan Ahikam, ɗan Shafan yă zama shugaban sauran mutanen da suka rage a Yahuda.
Bet pār tiem ļaudīm, kas bija atlikuši Jūda zemē, ko Nebukadnecars, Bābeles ķēniņš, bija atlicinājis, viņš iecēla Ģedaliju, Aikama dēlu, Safana dēla dēlu.
23 Sa’ad da dukan hafsoshin soja tare da mutanensu suka ji cewa sarkin Babilon ya naɗa Gedaliya a matsayin gwamna, sai suka zo wurin Gedaliya a Mizfa. Mutanen da suka zo su ne, Ishmayel ɗan Netaniya, Yohanan ɗan Kareya, Serahiya ɗan Tanhumet mutumin Netofa, Ya’azaniya ɗan mutumin Ma’aka, tare da mutanensu.
Kad nu visi kara virsnieki ar saviem vīriem dzirdēja, ka Bābeles ķēniņš Ģedaliju bija iecēlis par valdnieku, tad tie nāca pie Ģedalijas uz Micpu, ar vārdu: Ismaēls, Netanijas dēls, un Johanans, Kareūs dēls, un Seraja, Tanumeta dēls, no Netofas, un Jaēzanija, Maēkata dēls, ar saviem vīriem.
24 Gedaliya ya tabbatar musu da rantsuwa cewa, “Kada ku ji tsoron jama’ar Babiloniyawa, muddin kun zauna lafiya, kun kuma bauta wa sarkin Babilon, kome zai yi muku kyau.”
Un Ģedalija tiem un viņu vīriem zvērēja un uz tiem sacīja: nebīstaties no Kaldeju kalpiem, paliekat zemē un kalpojiet Bābeles ķēniņam, tad jums labi klāsies.
25 Amma a wata na bakwai, sai Ishmayel, ɗan Netaniya, ɗan Elishama, wanda yake daga gidan sarauta, ya zo tare da mutane goma, suka kashe Gedaliya duk da mutanen Yahuda, da na Babilon da suke tare da shi na Mizfa.
Bet septītā mēnesī nāca Ismaēls, Netanijas dēls, Elišama dēla dēls, no ķēniņa dzimuma, un desmit vīri ar viņu, un tie kāva Ģedaliju, ka tas nomira, līdz ar tiem Jūdiem un Kaldejiem, kas pie viņa bija Micpā.
26 Ganin haka sai dukan mutane, babba da ƙarami, tare da shugabannin sojoji, suka tashi suka gudu zuwa ƙasar Masar, gama suna tsoron mutanen Babilon.
Tad visi ļaudis cēlās, ir mazi, ir lieli līdz ar kara virsniekiem, un gāja uz Ēģipti; jo tie bijās no Kaldejiem. -
27 A shekara ta talatin da bakwai ta bautar Yehohiyacin sarkin Yahuda, a shekaran da Ewil-Merodak ya ci sarautan Babilon, sai ya saki Yehohiyacin daga jaru, ya sake shi a rana ashirin da bakwai ga watan goma sha biyu.
Un trīsdesmit septītā gadā pēc tam, kad Jojaķins, Jūda ķēniņš, bija aizvests, divpadsmitā mēnesī, divdesmit septītā mēneša dienā, Evil-Merodaks, Bābeles ķēniņš, tai gadā, kad palika par ķēniņu, paaugstināja Jojaķina, Jūda ķēniņa, galvu no cietuma nama.
28 Ya yi wa Yehohiyacin maganar alheri, ya kuma ɗaukaka shi sama da sauran sarakunan da suke tare da shi a Babilon.
Un viņš runāja laipnīgi ar to un lika viņa krēslu pār visiem ķēniņu krēsliem, kas pie viņa bija Bābelē.
29 Don haka Yehohiyacin ya tuɓe kayan fursuna. Kowace rana kuwa yakan ci abinci a teburin sarki har iyakar ransa.
Un viņš pārmija viņa cietuma drēbes, un tas ēda vienmēr viņa priekšā, kamēr dzīvoja.
30 Sarki kuma ya yanka masa kuɗin da za a dinga ba shi, kowace rana muddin ransa.
Un viņš tam nosprieda uzturam dienišķu daļu, ko tas ikdienas dabūja no ķēniņa, kamēr dzīvoja.