< 2 Sarakuna 25 >

1 A rana ta goma ga wata na goma, a shekara ta tara ta mulkin Zedekiya ne Nebukadnezzar sarkin Babilon tare da dukan rundunan yaƙinsa, ya tasam wa Urushalima. Ya yi sansani a bayan birnin, ya kewaye ta da shirin yaƙi.
Or il arriva en la neuvième année du règne de Sédécias, au dixième jour, au dixième mois, que Nabuchodonosor, roi de Babylone, vint, lui et toute son armée, contre Jérusalem; et ils l’investirent, et y construisirent tout autour des fortifications.
2 Haka birnin ta kasance a kewaye har shekara ta goma sha ɗaya ta mulkin Zedekiya.
Ainsi la ville fut enfermée et fortifiée jusqu’à la onzième année du roi Sédécias,
3 A rana ta tara ta watan huɗu, lokacin da yunwa ta yi tsanani a birnin, babu kuma abinci domin mutane su ci.
Au neuvième jour du mois, et la famine régna dans la ville; et il n’y avait pas de pain pour le peuple du pays.
4 Sai aka huda katanga sa’an nan dukan sojoji suka tsere da dare a ƙofa tsakanin katanga biyu da suke kusa da lambun sarki, ko da yake Babiloniyawa sun kewaye birnin. Suka tsere suka nufi Araba.
Et une brèche fut faite à la ville, et tous les hommes de guerre s’enfuirent durant la nuit, par la voie de la porte qui est entre le double mur près de la porte du jardin du roi (or les Chaldéens assiégeaient tout autour la ville): c’est pourquoi Sédécias s’enfuit par la voie qui conduit aux plaines du désert.
5 Amma sojojin Babiloniyawa suka bi sarki, suka cin masa a filayen Yeriko. Dukan sojojinsa kuwa suka rabu da shi suka watse.
Et l’armée des Chaldéens poursuivit le roi, et le prit dans la plaine de Jéricho; et tous les combattants qui étaient avec lui furent dispersés et l’abandonnèrent.
6 Aka kama shi, aka kai shi gaban sarkin Babilon a Ribla, inda aka yanke masa hukunci.
Ayant donc pris le roi, ils l’amenèrent au roi de Babylone à Réblatha, lequel prononça contre lui un arrêt.
7 Suka kashe’ya’yan Zedekiya a gabansa, sa’an nan aka ƙwaƙule idanunsa. Suka daure shi da sarƙar tagulla, suka kai shi Babilon.
Quant aux fils de Sédécias, il les tua devant lui, puis il lui creva les yeux, le chargea de chaînes et l’emmena à Babylone.
8 A rana ta bakwai na watan biyar, wadda ta zama shekara ta goma sha tara ta mulkin Sarki Nebukadnezzar na Babilon, Nebuzaradan, babban hafsan matsaran sarki, kuma bafadan sarkin Babilon, ya zo Urushalima
Au cinquième mois, au septième jour du mois, c’est la dix-neuvième année même du roi de Babylone, Nabuzardan, chef d’armée, serviteur du roi de Babylone, vint à Jérusalem.
9 Ya cinna wa haikalin Ubangiji wuta, da fadan sarki, da kuma dukan gidajen Urushalima. Ya kuma ƙone duk wani gini mai muhimmanci.
Et il brûla la maison du Seigneur et la maison du roi, et il consuma les maisons de Jérusalem, et toute espèce de maison.
10 Dukan mayaƙan Babilon a ƙarƙashin umarnin babban hafsan matsaran sarki, suka rushe katangar Urushalima.
Toute l’armée des Chaldéens, qui était avec ce chef de soldats, détruisit les murs de Jérusalem tout autour.
11 Nebuzaradan babban hafsan matsaran, ya kwashi waɗanda suka rage a cikin birnin, tare da sauran jama’a, da waɗanda suka miƙa kansu ga sarkin Babilon, ya kai su bauta.
Quant à l’autre partie du peuple qui était restée dans la ville, et aux transfuges qui avaient passé au roi de Babylone, et au reste du bas peuple, Nabuzardan, prince de la milice, les transporta à Babylone.
12 Amma hafsan ya bar waɗansu daga cikin mafiya talauci na ƙasar don su yi aiki a lambunan inabi da kuma gonaki.
Et il laissa d’entre les pauvres les vignerons et les laboureurs.
13 Babiloniyawan kuma suka sassare ginshiƙan tagulla, da wuraren zama da za a iya matsar da su, da ƙaton kwano mai suna Teku na tagulla da yake a haikalin Ubangiji, suka kwashe tagullan zuwa Babilon.
Mais les colonnes d’airain qui étaient dans le temple du Seigneur, et les bases, et la mer d’airain qui était dans la maison du Seigneur, les Chaldéens les brisèrent, et ils transportèrent tout l’airain à Babylone.
14 Suka ɗauke tukwane, da manyan cokula, da acibalbal, da kwanoni, da dai dukan kayan da aka yi da tagulla don hidima a haikalin Ubangiji.
Les marmites d’airain aussi, de même que les pelles, les tridents, les coupes, les petits mortiers, et tous les vases d’airain avec lesquels on faisait le service dans le temple, ils les emportèrent.
15 Babban hafsan matsaran sarkin ya kwashe har da kwanoni na kwashe garwashin wuta da sauran kwanoni, dukansu kuwa ƙeran zinariya ko azurfa tsatsa ne.
Le prince de la milice emporta également les encensoirs et les patères, ce qui était d’or, à part, et ce qui était d’argent, à part.
16 Tagullar ginshiƙai biyun nan, da ta ƙaton kwanon da ake ce da shi Teku, da ta dukan amalanke masu riƙe ruwa waɗanda Sarki Solomon ya yi domin haikalin Ubangiji, sun fi gaba a auna su.
C’est-à-dire les deux colonnes, la mer et les bases qu’avait faites Salomon dans le temple du Seigneur; il n’y avait pas de poids pour l’airain de tous ces vases.
17 Tsawon kowane ginshiƙi, ƙafa ashirin da bakwai ne. Hulunan tagullan da suke ƙwalƙwalin kowane ginshiƙi kuma yana da tsawon ƙafa huɗu da rabi. Kuma aka yi masa ado da saƙa da’ya’yan itace kewaye da shi. Bayan ginshiƙin ma haka yake.
L’une des colonnes avait dix-huit coudées de hauteur, et le chapiteau d’airain de dessus, était de trois coudées de hauteur: et il y avait un réseau et des grenades sur le chapiteau de la colonne; le tout était d’airain: la seconde colonne aussi avait un semblable ornement.
18 Babban hafsan ya kwashi Serahiya babban firist, da Zefaniya na biye da shi a girma, da matsara ƙofofi uku.
Le prince de la milice emmena aussi Saraïas, le premier prêtre, et Sophonias, second prêtre, et les trois portiers.
19 Daga cikin waɗanda suka rage a birnin, ya ɗauki hafsa mai kula da dakaru, da kuma mashawartan sarki guda biyar. Ya kuma tafi da magatakarda wanda yake babban jami’in soja mai ɗaukan dukan jama’an ƙasar, tare da mutanensa guda sittin waɗanda aka samu a birnin.
Et un eunuque de la ville qui commandait aux hommes de guerre, et cinq hommes qui étaient toujours devant le roi, qu’il trouva dans la ville, et Sopher, le prince de l’armée, qui exerçait les jeunes soldats pris d’entre le peuple du pays, et soixante hommes du bas peuple, qui avaient été trouvés dans la ville.
20 Nebuzaradan, babban hafsan, ya kwashe su duka ya kawo su wurin sarkin Babilon a Ribla.
Nabuzardan, chef des soldats, les ayant pris, les amena au roi de Babylone à Réblatha.
21 A can Ribla, a ƙasar Hamat, sarkin Babilon ya sa aka kashe su. Haka Yahuda ta tafi bauta daga ƙasarta.
Et le roi de Babylone les frappa et les tua à Réblatha, dans la terre d’Emath; ainsi Juda fut transféré hors de son pays,
22 Nebukadnezzar sarkin Babilon ya zaɓi Gedaliya ɗan Ahikam, ɗan Shafan yă zama shugaban sauran mutanen da suka rage a Yahuda.
Quant au peuple qui était resté dans la terre de Juda, qu’avait laissé Nabuchodonosor, roi de Babylone, il mit à sa tête Godolias, fils d’Ahicam, fils de Saphan.
23 Sa’ad da dukan hafsoshin soja tare da mutanensu suka ji cewa sarkin Babilon ya naɗa Gedaliya a matsayin gwamna, sai suka zo wurin Gedaliya a Mizfa. Mutanen da suka zo su ne, Ishmayel ɗan Netaniya, Yohanan ɗan Kareya, Serahiya ɗan Tanhumet mutumin Netofa, Ya’azaniya ɗan mutumin Ma’aka, tare da mutanensu.
Ce qu’ayant appris tous les chefs des soldats, eux et les hommes qui étaient avec eux, à savoir que le roi de Babylone avait établi Godolias pour gouverneur, Ismaël, fils de Nathanias, Johanan, fils de Carée, et Saraïa, fils de Thanéhumeth, le Nétophathite, et Jézonias, fils de Maachathi, vinrent vers Godolias à Maspha, eux et tous les leurs.
24 Gedaliya ya tabbatar musu da rantsuwa cewa, “Kada ku ji tsoron jama’ar Babiloniyawa, muddin kun zauna lafiya, kun kuma bauta wa sarkin Babilon, kome zai yi muku kyau.”
Et Godolias leur jura, à eux et aux leurs, disant: Ne craignez point de servir les Chaldéens; demeurez dans cette terre, et servez le roi de Babylone, et vous serez bien.
25 Amma a wata na bakwai, sai Ishmayel, ɗan Netaniya, ɗan Elishama, wanda yake daga gidan sarauta, ya zo tare da mutane goma, suka kashe Gedaliya duk da mutanen Yahuda, da na Babilon da suke tare da shi na Mizfa.
Or il arriva, au septième mois après, qu’Ismaël, fils de Nathanias, fils d’Elisama, de la race royale, vint à Maspha, et dix hommes avec lui; et ils frappèrent Godolias, qui mourut, et aussi les Juifs et les Chaldéens qui étaient avec lui.
26 Ganin haka sai dukan mutane, babba da ƙarami, tare da shugabannin sojoji, suka tashi suka gudu zuwa ƙasar Masar, gama suna tsoron mutanen Babilon.
Et se levant, tout le peuple, depuis le petit jusqu’au grand, et les chefs des soldats, vinrent en Egypte, craignant les Chaldéens.
27 A shekara ta talatin da bakwai ta bautar Yehohiyacin sarkin Yahuda, a shekaran da Ewil-Merodak ya ci sarautan Babilon, sai ya saki Yehohiyacin daga jaru, ya sake shi a rana ashirin da bakwai ga watan goma sha biyu.
Mais il arriva qu’en la trente-septième année de la captivité de Joachin, roi de Juda, au douzième mois, au vingt-septième jour du mois, Evilmérodach, roi de Babylone, en l’année même qu’il commença à régner tira Joachin, roi de Juda, de prison.
28 Ya yi wa Yehohiyacin maganar alheri, ya kuma ɗaukaka shi sama da sauran sarakunan da suke tare da shi a Babilon.
Et il lui parla avec bonté, et il mit son trône au-dessus du trône des rois qui étaient auprès de lui à Babylone.
29 Don haka Yehohiyacin ya tuɓe kayan fursuna. Kowace rana kuwa yakan ci abinci a teburin sarki har iyakar ransa.
Et il changea ses vêtements qu’il avait eus dans la prison; et Joachin mangea toujours du pain en sa présence tous les jour? de sa vie.
30 Sarki kuma ya yanka masa kuɗin da za a dinga ba shi, kowace rana muddin ransa.
Il lui assigna aussi sans interruption des vivres, qui même lui étaient donnés chaque jour par le roi, tous les jours de sa vie.

< 2 Sarakuna 25 >