< 2 Sarakuna 25 >

1 A rana ta goma ga wata na goma, a shekara ta tara ta mulkin Zedekiya ne Nebukadnezzar sarkin Babilon tare da dukan rundunan yaƙinsa, ya tasam wa Urushalima. Ya yi sansani a bayan birnin, ya kewaye ta da shirin yaƙi.
Et il arriva, en la neuvième année de son règne, au dixième mois, le dixième [jour] du mois, que Nebucadnetsar, roi de Babylone, vint contre Jérusalem, lui et toute son armée, et campa contre elle; et ils bâtirent contre elle une circonvallation tout à l’entour.
2 Haka birnin ta kasance a kewaye har shekara ta goma sha ɗaya ta mulkin Zedekiya.
Et la ville fut assiégée jusqu’à la onzième année du roi Sédécias.
3 A rana ta tara ta watan huɗu, lokacin da yunwa ta yi tsanani a birnin, babu kuma abinci domin mutane su ci.
Le neuvième jour du [quatrième] mois, la famine se renforça dans la ville, et il n’y avait point de pain pour le peuple du pays.
4 Sai aka huda katanga sa’an nan dukan sojoji suka tsere da dare a ƙofa tsakanin katanga biyu da suke kusa da lambun sarki, ko da yake Babiloniyawa sun kewaye birnin. Suka tsere suka nufi Araba.
Et la brèche fut faite à la ville; et tous les hommes de guerre [s’enfuirent] de nuit par le chemin de la porte qui était entre les deux murailles près du jardin du roi; (et les Chaldéens étaient près de la ville tout à l’entour); et on s’en alla par le chemin de la plaine.
5 Amma sojojin Babiloniyawa suka bi sarki, suka cin masa a filayen Yeriko. Dukan sojojinsa kuwa suka rabu da shi suka watse.
Et l’armée des Chaldéens poursuivit le roi; et ils l’atteignirent dans les plaines de Jéricho, et toute son armée se dispersa d’avec lui.
6 Aka kama shi, aka kai shi gaban sarkin Babilon a Ribla, inda aka yanke masa hukunci.
Et ils prirent le roi, et le firent monter vers le roi de Babylone à Ribla, et on prononça son jugement.
7 Suka kashe’ya’yan Zedekiya a gabansa, sa’an nan aka ƙwaƙule idanunsa. Suka daure shi da sarƙar tagulla, suka kai shi Babilon.
Et on égorgea les fils de Sédécias devant ses yeux; et on creva les yeux à Sédécias, et on le lia avec des chaînes d’airain, et on l’amena à Babylone.
8 A rana ta bakwai na watan biyar, wadda ta zama shekara ta goma sha tara ta mulkin Sarki Nebukadnezzar na Babilon, Nebuzaradan, babban hafsan matsaran sarki, kuma bafadan sarkin Babilon, ya zo Urushalima
Et au cinquième mois, le septième [jour] du mois (c’était la dix -neuvième année du roi Nebucadnetsar, roi de Babylone, ) Nebuzaradan, chef des gardes, serviteur du roi de Babylone, vint à Jérusalem.
9 Ya cinna wa haikalin Ubangiji wuta, da fadan sarki, da kuma dukan gidajen Urushalima. Ya kuma ƙone duk wani gini mai muhimmanci.
Et il brûla la maison de l’Éternel, et la maison du roi, et toutes les maisons de Jérusalem; et il brûla par le feu toutes les grandes maisons.
10 Dukan mayaƙan Babilon a ƙarƙashin umarnin babban hafsan matsaran sarki, suka rushe katangar Urushalima.
Et toute l’armée des Chaldéens qui était avec le chef des gardes abattit les murailles [qui étaient] autour de Jérusalem.
11 Nebuzaradan babban hafsan matsaran, ya kwashi waɗanda suka rage a cikin birnin, tare da sauran jama’a, da waɗanda suka miƙa kansu ga sarkin Babilon, ya kai su bauta.
Et le reste du peuple, qui était demeuré de reste dans la ville, et les transfuges qui s’étaient rendus au roi de Babylone, et le reste de la multitude, Nebuzaradan, chef des gardes, les transporta;
12 Amma hafsan ya bar waɗansu daga cikin mafiya talauci na ƙasar don su yi aiki a lambunan inabi da kuma gonaki.
mais des pauvres du pays, le chef des gardes en laissa pour être vignerons et laboureurs.
13 Babiloniyawan kuma suka sassare ginshiƙan tagulla, da wuraren zama da za a iya matsar da su, da ƙaton kwano mai suna Teku na tagulla da yake a haikalin Ubangiji, suka kwashe tagullan zuwa Babilon.
Et les Chaldéens brisèrent les colonnes d’airain qui étaient devant la maison de l’Éternel, et les bases, et la mer d’airain qui était dans la maison de l’Éternel, et en emportèrent l’airain à Babylone.
14 Suka ɗauke tukwane, da manyan cokula, da acibalbal, da kwanoni, da dai dukan kayan da aka yi da tagulla don hidima a haikalin Ubangiji.
Ils prirent aussi les vases [à cendre], et les pelles, et les couteaux, et les coupes, et tous les ustensiles d’airain avec lesquels on faisait le service.
15 Babban hafsan matsaran sarkin ya kwashe har da kwanoni na kwashe garwashin wuta da sauran kwanoni, dukansu kuwa ƙeran zinariya ko azurfa tsatsa ne.
Et le chef des gardes prit les brasiers et les bassins, ce qui était d’or, en or, et ce qui était d’argent, en argent.
16 Tagullar ginshiƙai biyun nan, da ta ƙaton kwanon da ake ce da shi Teku, da ta dukan amalanke masu riƙe ruwa waɗanda Sarki Solomon ya yi domin haikalin Ubangiji, sun fi gaba a auna su.
Les deux colonnes, la mer unique, et les socles que Salomon avait faits pour la maison de l’Éternel: pour l’airain de tous ces objets il n’y avait point de poids.
17 Tsawon kowane ginshiƙi, ƙafa ashirin da bakwai ne. Hulunan tagullan da suke ƙwalƙwalin kowane ginshiƙi kuma yana da tsawon ƙafa huɗu da rabi. Kuma aka yi masa ado da saƙa da’ya’yan itace kewaye da shi. Bayan ginshiƙin ma haka yake.
La hauteur d’une colonne était de 18 coudées; et il y avait dessus un chapiteau d’airain, et la hauteur du chapiteau était de trois coudées; et il y avait un réseau et des grenades tout autour du chapiteau, le tout d’airain: et de même pour la seconde colonne, avec le réseau.
18 Babban hafsan ya kwashi Serahiya babban firist, da Zefaniya na biye da shi a girma, da matsara ƙofofi uku.
Et le chef des gardes prit Seraïa, le premier sacrificateur, et Sophonie, le second sacrificateur, et les trois gardiens du seuil;
19 Daga cikin waɗanda suka rage a birnin, ya ɗauki hafsa mai kula da dakaru, da kuma mashawartan sarki guda biyar. Ya kuma tafi da magatakarda wanda yake babban jami’in soja mai ɗaukan dukan jama’an ƙasar, tare da mutanensa guda sittin waɗanda aka samu a birnin.
et il prit de la ville un eunuque qui était inspecteur des hommes de guerre, et cinq hommes de ceux qui voyaient la face du roi, lesquels furent trouvés dans la ville, et le scribe du chef de l’armée, qui enrôlait le peuple du pays, et 60 hommes du peuple du pays, qui furent trouvés dans la ville.
20 Nebuzaradan, babban hafsan, ya kwashe su duka ya kawo su wurin sarkin Babilon a Ribla.
Et Nebuzaradan, chef des gardes, les prit et les mena vers le roi de Babylone à Ribla.
21 A can Ribla, a ƙasar Hamat, sarkin Babilon ya sa aka kashe su. Haka Yahuda ta tafi bauta daga ƙasarta.
Et le roi de Babylone les frappa et les fit mourir à Ribla, dans le pays de Hamath. Et Juda fut transporté de dessus sa terre.
22 Nebukadnezzar sarkin Babilon ya zaɓi Gedaliya ɗan Ahikam, ɗan Shafan yă zama shugaban sauran mutanen da suka rage a Yahuda.
Et quant au peuple qui était demeuré de reste dans le pays de Juda, que Nebucadnetsar, roi de Babylone, avait laissé, il établit sur eux Guedalia, fils d’Akhikam, fils de Shaphan.
23 Sa’ad da dukan hafsoshin soja tare da mutanensu suka ji cewa sarkin Babilon ya naɗa Gedaliya a matsayin gwamna, sai suka zo wurin Gedaliya a Mizfa. Mutanen da suka zo su ne, Ishmayel ɗan Netaniya, Yohanan ɗan Kareya, Serahiya ɗan Tanhumet mutumin Netofa, Ya’azaniya ɗan mutumin Ma’aka, tare da mutanensu.
Et tous les chefs des forces, eux et leurs hommes, apprirent que le roi de Babylone avait établi [chef] Guedalia; et ils vinrent vers Guedalia à Mitspa, savoir Ismaël, fils de Nethania, et Jokhanan, fils de Karéakh, et Seraïa, fils de Thanhumeth, le Netophathite, et Jaazania, fils d’un Maacathien, eux et leurs hommes.
24 Gedaliya ya tabbatar musu da rantsuwa cewa, “Kada ku ji tsoron jama’ar Babiloniyawa, muddin kun zauna lafiya, kun kuma bauta wa sarkin Babilon, kome zai yi muku kyau.”
Et Guedalia leur jura, à eux et à leurs hommes, et leur dit: Ne craignez pas de devenir les serviteurs des Chaldéens; habitez dans le pays, et servez le roi de Babylone, et vous vous en trouverez bien.
25 Amma a wata na bakwai, sai Ishmayel, ɗan Netaniya, ɗan Elishama, wanda yake daga gidan sarauta, ya zo tare da mutane goma, suka kashe Gedaliya duk da mutanen Yahuda, da na Babilon da suke tare da shi na Mizfa.
Et il arriva, au septième mois, qu’Ismaël, fils de Nethania, fils d’Élishama, de la semence royale, et dix hommes avec lui, vinrent et frappèrent Guedalia, (et il mourut), et les Juifs et les Chaldéens qui étaient avec lui à Mitspa.
26 Ganin haka sai dukan mutane, babba da ƙarami, tare da shugabannin sojoji, suka tashi suka gudu zuwa ƙasar Masar, gama suna tsoron mutanen Babilon.
Et tout le peuple, depuis le petit jusqu’au grand, et les chefs des forces, se levèrent et allèrent en Égypte, car ils craignaient les Chaldéens.
27 A shekara ta talatin da bakwai ta bautar Yehohiyacin sarkin Yahuda, a shekaran da Ewil-Merodak ya ci sarautan Babilon, sai ya saki Yehohiyacin daga jaru, ya sake shi a rana ashirin da bakwai ga watan goma sha biyu.
Et il arriva, en la trente-septième année de la transportation de Jehoïakin, roi de Juda, au douzième mois, le vingt-septième [jour] du mois, qu’Évil-Merodac, roi de Babylone, l’année où il commença de régner, éleva la tête de Jehoïakin, roi de Juda, [et le tira] de prison.
28 Ya yi wa Yehohiyacin maganar alheri, ya kuma ɗaukaka shi sama da sauran sarakunan da suke tare da shi a Babilon.
Et il lui parla avec bonté, et mit son trône au-dessus du trône des rois qui étaient avec lui à Babylone.
29 Don haka Yehohiyacin ya tuɓe kayan fursuna. Kowace rana kuwa yakan ci abinci a teburin sarki har iyakar ransa.
Et il lui changea ses vêtements de prison, et [Jehoïakin] mangea le pain devant lui constamment, tous les jours de sa vie;
30 Sarki kuma ya yanka masa kuɗin da za a dinga ba shi, kowace rana muddin ransa.
et quant à son entretien régulier, un entretien continuel lui fut donné de la part du roi, jour par jour, tous les jours de sa vie.

< 2 Sarakuna 25 >