< 2 Sarakuna 25 >

1 A rana ta goma ga wata na goma, a shekara ta tara ta mulkin Zedekiya ne Nebukadnezzar sarkin Babilon tare da dukan rundunan yaƙinsa, ya tasam wa Urushalima. Ya yi sansani a bayan birnin, ya kewaye ta da shirin yaƙi.
Forsothe it was don in the nynthe yeer of his rewme, in the tenthe moneth, in the tenthe dai of the moneth, Nabugodonosor, kyng of Babiloyne, cam, he, and al his oost, in to Jerusalem; and thei cumpassiden it, and bildiden `stronge thingis in the cumpass therof.
2 Haka birnin ta kasance a kewaye har shekara ta goma sha ɗaya ta mulkin Zedekiya.
And the citee was closid, and cumpassid, `til to the eleuenthe yeer of king Sedechie,
3 A rana ta tara ta watan huɗu, lokacin da yunwa ta yi tsanani a birnin, babu kuma abinci domin mutane su ci.
in the nynthe day of the monethe; and hungur `hadde maistrie in the citee, and `breed was not to the puple of the lond.
4 Sai aka huda katanga sa’an nan dukan sojoji suka tsere da dare a ƙofa tsakanin katanga biyu da suke kusa da lambun sarki, ko da yake Babiloniyawa sun kewaye birnin. Suka tsere suka nufi Araba.
And the citee was brokun, and alle men werriours fledden in the niyt bi the weie of the yate, which is bitwixe the double wal, to the gardyn of the kyng; sotheli Caldeis bisegiden the citee `bi cumpas. Therfor Sedechie fledde bi the weie that ledith to the feeldi placis of the wildirnesse;
5 Amma sojojin Babiloniyawa suka bi sarki, suka cin masa a filayen Yeriko. Dukan sojojinsa kuwa suka rabu da shi suka watse.
and the oost of Caldeis pursuede the king, and it took him in the pleyn of Jerico; and alle the werriours, that weren with him, weren scaterid, and leften him.
6 Aka kama shi, aka kai shi gaban sarkin Babilon a Ribla, inda aka yanke masa hukunci.
Therfor thei ledden the king takun to the king of Babiloyne, in to Reblatha, which spak dom with him, `that is, with Sedechie.
7 Suka kashe’ya’yan Zedekiya a gabansa, sa’an nan aka ƙwaƙule idanunsa. Suka daure shi da sarƙar tagulla, suka kai shi Babilon.
Sotheli he killide the sones of Sedechie bifor him, and puttide out his iyen, and boond him with chaynes, and ledde him in to Babiloyne.
8 A rana ta bakwai na watan biyar, wadda ta zama shekara ta goma sha tara ta mulkin Sarki Nebukadnezzar na Babilon, Nebuzaradan, babban hafsan matsaran sarki, kuma bafadan sarkin Babilon, ya zo Urushalima
In the fifthe monethe, in the seuenthe dai of the monethe, thilke is the nyntenthe yeer of the king of Babiloyne, Nabuzardan, prince of the oost, seruaunt of the king of Babiloyne, cam in to Jerusalem;
9 Ya cinna wa haikalin Ubangiji wuta, da fadan sarki, da kuma dukan gidajen Urushalima. Ya kuma ƙone duk wani gini mai muhimmanci.
and he brente the hows of the Lord, and the hows of the king, and the housis of Jerusalem, and he brente bi fier ech hows;
10 Dukan mayaƙan Babilon a ƙarƙashin umarnin babban hafsan matsaran sarki, suka rushe katangar Urushalima.
and al the oost of Caldeis, that was with the prince of knyytis, distriede the wallis of Jerusalem `in cumpas.
11 Nebuzaradan babban hafsan matsaran, ya kwashi waɗanda suka rage a cikin birnin, tare da sauran jama’a, da waɗanda suka miƙa kansu ga sarkin Babilon, ya kai su bauta.
Forsothe Nabuzardan, prince of the chyyualrie, translatide the tother part of the puple, that dwellide in the citee, and the fleeris, that hadden fled ouer to the king of Babiloyne, and the residue comyn puple;
12 Amma hafsan ya bar waɗansu daga cikin mafiya talauci na ƙasar don su yi aiki a lambunan inabi da kuma gonaki.
and he lefte of the pore men of the lond vyntilieris, and erthe tilieris.
13 Babiloniyawan kuma suka sassare ginshiƙan tagulla, da wuraren zama da za a iya matsar da su, da ƙaton kwano mai suna Teku na tagulla da yake a haikalin Ubangiji, suka kwashe tagullan zuwa Babilon.
Sotheli Caldeis braken the brasun pilers, that weren in the temple, and the foundementis, and the see of bras, that was in the hous of the Lord; and thei translatiden al the metal in to Babiloyne.
14 Suka ɗauke tukwane, da manyan cokula, da acibalbal, da kwanoni, da dai dukan kayan da aka yi da tagulla don hidima a haikalin Ubangiji.
And thei token the pottis of bras, and trullis, and fleisch hokis, and cuppis, and morteris, and alle brasun vessels, in whiche thei mynystriden;
15 Babban hafsan matsaran sarkin ya kwashe har da kwanoni na kwashe garwashin wuta da sauran kwanoni, dukansu kuwa ƙeran zinariya ko azurfa tsatsa ne.
also and censeris, and violis. The prince of the chyualrie took tho that weren of gold, and tho that weren of siluer,
16 Tagullar ginshiƙai biyun nan, da ta ƙaton kwanon da ake ce da shi Teku, da ta dukan amalanke masu riƙe ruwa waɗanda Sarki Solomon ya yi domin haikalin Ubangiji, sun fi gaba a auna su.
that is, twei pileris, o see, and the foundementis, whiche king Salomon hadde maad `in to the temple of the Lord; and no weiyte was of metal of alle the vessels.
17 Tsawon kowane ginshiƙi, ƙafa ashirin da bakwai ne. Hulunan tagullan da suke ƙwalƙwalin kowane ginshiƙi kuma yana da tsawon ƙafa huɗu da rabi. Kuma aka yi masa ado da saƙa da’ya’yan itace kewaye da shi. Bayan ginshiƙin ma haka yake.
O piler hadde eiyten cubitis of hiyte, and a brasun pomel on it of the heiyte of thre cubitis, and a werk lijk a net, and pomgarnadis on the pomel of the piler, alle thingis of bras; and the secounde piler hadde lijk ournyng.
18 Babban hafsan ya kwashi Serahiya babban firist, da Zefaniya na biye da shi a girma, da matsara ƙofofi uku.
Also the prince of the chyualrie took Saraie, the firste preest, and Sophony, the secunde prest,
19 Daga cikin waɗanda suka rage a birnin, ya ɗauki hafsa mai kula da dakaru, da kuma mashawartan sarki guda biyar. Ya kuma tafi da magatakarda wanda yake babban jami’in soja mai ɗaukan dukan jama’an ƙasar, tare da mutanensa guda sittin waɗanda aka samu a birnin.
and thre porteris, and oon onest seruaunt of the citee, that was a souereyn ouer men werriours, and fyue men `of hem that stoden bifor the king, whiche he foond in the citee; and he took Sopher, the prince of the oost, that preuide yonge knyytis, `ether men able to batel, of the puple of the lond, and sixe men of the comyns, that weren foundyn in the citee;
20 Nebuzaradan, babban hafsan, ya kwashe su duka ya kawo su wurin sarkin Babilon a Ribla.
whiche Nabuzardan, prince of the chyualrie, took, and ledde to the king of Babiloyne, in to Reblatha.
21 A can Ribla, a ƙasar Hamat, sarkin Babilon ya sa aka kashe su. Haka Yahuda ta tafi bauta daga ƙasarta.
And the kyng of Babiloyne smoot hem, and killide hem in Reblatha, in the lond of Emath; and Juda was translatid fro his lond.
22 Nebukadnezzar sarkin Babilon ya zaɓi Gedaliya ɗan Ahikam, ɗan Shafan yă zama shugaban sauran mutanen da suka rage a Yahuda.
Sotheli he made souereyn Godolie, sone of Aicham, sone of Saphan, to the puple that was left in the lond of Juda; which puple Nabugodonosor, king of Babiloyne, hadde left.
23 Sa’ad da dukan hafsoshin soja tare da mutanensu suka ji cewa sarkin Babilon ya naɗa Gedaliya a matsayin gwamna, sai suka zo wurin Gedaliya a Mizfa. Mutanen da suka zo su ne, Ishmayel ɗan Netaniya, Yohanan ɗan Kareya, Serahiya ɗan Tanhumet mutumin Netofa, Ya’azaniya ɗan mutumin Ma’aka, tare da mutanensu.
And whanne alle the duykis of knyytis hadde herd these thingis, thei, and the men that weren with hem, that is, that the king of Babiloyne hadde ordeyned Godolie, thei camen `to Godolie, in Maspha, Ismael, sone of Nathanye, and Johannan, sone of Charee, and Saraie, sone of Thenameth of Nechophat, and Jeconye, sone of Machati, thei, and Machat, and the felowis of hem.
24 Gedaliya ya tabbatar musu da rantsuwa cewa, “Kada ku ji tsoron jama’ar Babiloniyawa, muddin kun zauna lafiya, kun kuma bauta wa sarkin Babilon, kome zai yi muku kyau.”
And Godolie swoor to hem, and to the felowis of hem, and seide, Nyle ye drede to serue the Caldeis; dwelle ye in the lond, and serue ye the king of Babiloyne, and it schal be wel to you.
25 Amma a wata na bakwai, sai Ishmayel, ɗan Netaniya, ɗan Elishama, wanda yake daga gidan sarauta, ya zo tare da mutane goma, suka kashe Gedaliya duk da mutanen Yahuda, da na Babilon da suke tare da shi na Mizfa.
Forsothe it was don in the seuenthe monethe, `that is, sithen Godolie was maad souereyn, Hismael, the sone of Nathanye, sone of Elysama, of the `kyngis seed, cam, and ten men with hym, and thei smytiden Godolie, which diede; but also thei smytiden Jewis and Caldeis, that weren with hym in Maspha.
26 Ganin haka sai dukan mutane, babba da ƙarami, tare da shugabannin sojoji, suka tashi suka gudu zuwa ƙasar Masar, gama suna tsoron mutanen Babilon.
And al the puple roos fro litil `til to greet, and the prynces of knyytis, and camen in to Egipt, and dredden Caldeis.
27 A shekara ta talatin da bakwai ta bautar Yehohiyacin sarkin Yahuda, a shekaran da Ewil-Merodak ya ci sarautan Babilon, sai ya saki Yehohiyacin daga jaru, ya sake shi a rana ashirin da bakwai ga watan goma sha biyu.
Therfor it was doon in the seuenthe and threttithe yeer of transmigracioun, `ether passyng ouer, of Joakyn, kyng of Juda, in the tweluethe monethe, in the seuene and twentithe dai of the monethe, Euylmeradach, kyng of Babiloyne, in the yeer in which he bigan to regne, reiside the heed of Joakyn, kyng of Juda,
28 Ya yi wa Yehohiyacin maganar alheri, ya kuma ɗaukaka shi sama da sauran sarakunan da suke tare da shi a Babilon.
fro prisoun, and spak to hym benygneli; and he settide the trone of Joakyn aboue the trone of kyngis, that weren with hym in Babilonye.
29 Don haka Yehohiyacin ya tuɓe kayan fursuna. Kowace rana kuwa yakan ci abinci a teburin sarki har iyakar ransa.
And he chaungide `hise clothis, whiche he hadde in prisoun; and he eet breed euer in the siyt of Euylmeradach, in alle the daies of his lijf.
30 Sarki kuma ya yanka masa kuɗin da za a dinga ba shi, kowace rana muddin ransa.
Also Euylmeradach ordeynede sustenaunce `to hym with out ceessyng; which sustenaunce also was youun of the kyng to hym bi alle daies, and in alle the daies of his lijf.

< 2 Sarakuna 25 >