< 2 Sarakuna 25 >

1 A rana ta goma ga wata na goma, a shekara ta tara ta mulkin Zedekiya ne Nebukadnezzar sarkin Babilon tare da dukan rundunan yaƙinsa, ya tasam wa Urushalima. Ya yi sansani a bayan birnin, ya kewaye ta da shirin yaƙi.
And it came to pass in the ninth year of his reign, in the tenth month, on the tenth of the month, that Nebuchadnezzar the king of Babylon came, he, and all his host, against Jerusalem, and encamped against it; and they built a mound all around about it.
2 Haka birnin ta kasance a kewaye har shekara ta goma sha ɗaya ta mulkin Zedekiya.
And the city was put in a state of siege until the eleventh year of king Zedekiah.
3 A rana ta tara ta watan huɗu, lokacin da yunwa ta yi tsanani a birnin, babu kuma abinci domin mutane su ci.
And on the ninth of the month, when the famine prevailed in the city, and there was no bread for the people of the land:
4 Sai aka huda katanga sa’an nan dukan sojoji suka tsere da dare a ƙofa tsakanin katanga biyu da suke kusa da lambun sarki, ko da yake Babiloniyawa sun kewaye birnin. Suka tsere suka nufi Araba.
The city was broken into, and all the men of war [fled] in the night by the way of the gate between the two walls, which was by the king's garden; [while the Chaldeans were all round about the city; ] and the people went the way toward the plain.
5 Amma sojojin Babiloniyawa suka bi sarki, suka cin masa a filayen Yeriko. Dukan sojojinsa kuwa suka rabu da shi suka watse.
And the army of the Chaldeans pursued after the king, and overtook him in the plains of Jericho: and all his army were scattered from around him.
6 Aka kama shi, aka kai shi gaban sarkin Babilon a Ribla, inda aka yanke masa hukunci.
And they seized the king, and brought him up to the king of Babylon to Riblah; and they called him to account.
7 Suka kashe’ya’yan Zedekiya a gabansa, sa’an nan aka ƙwaƙule idanunsa. Suka daure shi da sarƙar tagulla, suka kai shi Babilon.
And they slaughtered the sons of Zedekiah before his eyes, and he blinded the eyes of Zedekiah, and bound him with fetters of brass, and carried him to Babylon.
8 A rana ta bakwai na watan biyar, wadda ta zama shekara ta goma sha tara ta mulkin Sarki Nebukadnezzar na Babilon, Nebuzaradan, babban hafsan matsaran sarki, kuma bafadan sarkin Babilon, ya zo Urushalima
And in the fifth month, on the seventh day of the month, which was the nineteenth year of king Nebuchadnezzar the king of Babylon, came Nebusaradan, the chief of the guard, a servant of the king of Babylon, unto Jerusalem:
9 Ya cinna wa haikalin Ubangiji wuta, da fadan sarki, da kuma dukan gidajen Urushalima. Ya kuma ƙone duk wani gini mai muhimmanci.
And he burnt the house of the Lord, and the king's house; also, all the houses of Jerusalem, and every great man's house burnt he with fire.
10 Dukan mayaƙan Babilon a ƙarƙashin umarnin babban hafsan matsaran sarki, suka rushe katangar Urushalima.
And the walls of Jerusalem round about did all the army of the Chaldeans that were with the captain of the guard tear down.
11 Nebuzaradan babban hafsan matsaran, ya kwashi waɗanda suka rage a cikin birnin, tare da sauran jama’a, da waɗanda suka miƙa kansu ga sarkin Babilon, ya kai su bauta.
And the rest of the people that were left in the city, and the deserters that had run over to the king of Babylon, with the remnant of the multitude, did Nebusaradan the captain of the guard lead away into exile;
12 Amma hafsan ya bar waɗansu daga cikin mafiya talauci na ƙasar don su yi aiki a lambunan inabi da kuma gonaki.
But from the poorest of the land the captain of the guard left some to be vine-dressers and husbandmen.
13 Babiloniyawan kuma suka sassare ginshiƙan tagulla, da wuraren zama da za a iya matsar da su, da ƙaton kwano mai suna Teku na tagulla da yake a haikalin Ubangiji, suka kwashe tagullan zuwa Babilon.
And the pillars of copper that were in the house of the Lord, and the bases, and the copper sea that was in the house of the Lord, did the Chaldeans break up, and they carried the copper thereof to Babylon.
14 Suka ɗauke tukwane, da manyan cokula, da acibalbal, da kwanoni, da dai dukan kayan da aka yi da tagulla don hidima a haikalin Ubangiji.
And the pots, and the shovels, and the knives, and the spoons, and all the vessels of copper wherewith they ministered, took they away.
15 Babban hafsan matsaran sarkin ya kwashe har da kwanoni na kwashe garwashin wuta da sauran kwanoni, dukansu kuwa ƙeran zinariya ko azurfa tsatsa ne.
And the censers, and the bowls, the gold of the golden things, and the silver of the silver things, took the captain of the guard away.
16 Tagullar ginshiƙai biyun nan, da ta ƙaton kwanon da ake ce da shi Teku, da ta dukan amalanke masu riƙe ruwa waɗanda Sarki Solomon ya yi domin haikalin Ubangiji, sun fi gaba a auna su.
The two pillars, the one sea, and the bases which Solomon had made for the house of the Lord: the copper of all these vessels was too much to be weighed.
17 Tsawon kowane ginshiƙi, ƙafa ashirin da bakwai ne. Hulunan tagullan da suke ƙwalƙwalin kowane ginshiƙi kuma yana da tsawon ƙafa huɗu da rabi. Kuma aka yi masa ado da saƙa da’ya’yan itace kewaye da shi. Bayan ginshiƙin ma haka yake.
Eighteen cubits was the height of the one pillar, and the capital upon it was copper; and the height of the capital was three cubits; and the wreathed work, and the pomegranates upon the capitals round about, were all of copper: and the same had the second pillar together with the wreathed work.
18 Babban hafsan ya kwashi Serahiya babban firist, da Zefaniya na biye da shi a girma, da matsara ƙofofi uku.
And the captain of the guard took Serayah the chief-priest, and Zephanyahu the second priest, and the three door-keepers;
19 Daga cikin waɗanda suka rage a birnin, ya ɗauki hafsa mai kula da dakaru, da kuma mashawartan sarki guda biyar. Ya kuma tafi da magatakarda wanda yake babban jami’in soja mai ɗaukan dukan jama’an ƙasar, tare da mutanensa guda sittin waɗanda aka samu a birnin.
And out of the city he took one court-officer that was appointed over the men of war, and five men of those that could come into the king's presence, who were found in the city, and the scribe of the chief of the army, who ordered to the army the people of the land, and sixty men of the people of the land that were found in the city:
20 Nebuzaradan, babban hafsan, ya kwashe su duka ya kawo su wurin sarkin Babilon a Ribla.
And Nebusaradan the captain of the guard took these, and conducted them to the king of Babylon to Riblah;
21 A can Ribla, a ƙasar Hamat, sarkin Babilon ya sa aka kashe su. Haka Yahuda ta tafi bauta daga ƙasarta.
And the king of Babylon smote them, and put them to death at Riblah in the land of Chamath. So did Judah wander away into exile out of their land.
22 Nebukadnezzar sarkin Babilon ya zaɓi Gedaliya ɗan Ahikam, ɗan Shafan yă zama shugaban sauran mutanen da suka rage a Yahuda.
And as for the people that were left in the land of Judah, whom Nebuchadnezzar the king of Babylon had left, he appointed over them Gedalyahu the son of Achikam, the son of Shaphan.
23 Sa’ad da dukan hafsoshin soja tare da mutanensu suka ji cewa sarkin Babilon ya naɗa Gedaliya a matsayin gwamna, sai suka zo wurin Gedaliya a Mizfa. Mutanen da suka zo su ne, Ishmayel ɗan Netaniya, Yohanan ɗan Kareya, Serahiya ɗan Tanhumet mutumin Netofa, Ya’azaniya ɗan mutumin Ma’aka, tare da mutanensu.
And when all the captains of the armies, they and their men, heard that the king of Babylon had appointed Gedalyahu, they came to Gedalyahu to Mizpah; even Ishma'el the son of Nethanyah, and Jochanan the son of Kareach, and Serayah the son of Tanchumeth the Netophathite, and Jaazanyahu the son of a Ma'achathite, they and their men.
24 Gedaliya ya tabbatar musu da rantsuwa cewa, “Kada ku ji tsoron jama’ar Babiloniyawa, muddin kun zauna lafiya, kun kuma bauta wa sarkin Babilon, kome zai yi muku kyau.”
And Gedalyahu swore to them, and to their men, and said unto them, Be not afraid of the servants of the Chaldeans: remain in the land, and serve the king of Babylon; and it will be well with you.
25 Amma a wata na bakwai, sai Ishmayel, ɗan Netaniya, ɗan Elishama, wanda yake daga gidan sarauta, ya zo tare da mutane goma, suka kashe Gedaliya duk da mutanen Yahuda, da na Babilon da suke tare da shi na Mizfa.
But it happened in the seventh month, that there came Ishma'el the son of Nethanyah, the son of Elishama', of the seed royal, and ten men with him, and they smote Gedalyahu, so that he died, also the Jews and the Chaldeans that were with him at Mizpah.
26 Ganin haka sai dukan mutane, babba da ƙarami, tare da shugabannin sojoji, suka tashi suka gudu zuwa ƙasar Masar, gama suna tsoron mutanen Babilon.
And then arose all the people, from small to great, and the captains of the armies, and went to Egypt; for they were afraid of the Chaldeans.
27 A shekara ta talatin da bakwai ta bautar Yehohiyacin sarkin Yahuda, a shekaran da Ewil-Merodak ya ci sarautan Babilon, sai ya saki Yehohiyacin daga jaru, ya sake shi a rana ashirin da bakwai ga watan goma sha biyu.
And it came to pass in the seven and thirtieth year of the captivity of Jehoyachin the king of Judah, in the twelfth month, on the seven and twentieth [day] of the month, that Evil-merodach the king of Babylon in the year that he became king did lift up the head of Jehoyachin the king of Judah out of the prison;
28 Ya yi wa Yehohiyacin maganar alheri, ya kuma ɗaukaka shi sama da sauran sarakunan da suke tare da shi a Babilon.
And he spoke kindly to him, and set his chair above the chair of the kings that were with him in Babylon:
29 Don haka Yehohiyacin ya tuɓe kayan fursuna. Kowace rana kuwa yakan ci abinci a teburin sarki har iyakar ransa.
And changed his prison garments: and he ate bread continually before him all the days of his life.
30 Sarki kuma ya yanka masa kuɗin da za a dinga ba shi, kowace rana muddin ransa.
And his allowance was a continual allowance given him by the king, the necessary ration for the day on its day, all the days of his life.

< 2 Sarakuna 25 >