< 2 Sarakuna 24 >

1 A zamani Yehohiyakim, Nebukadnezzar sarkin Babilon ya kawo wa ƙasar farmaki, Yehohiyakim dai ya zama abokin tarayyarsa na tsawon shekara uku. Daga baya kuma sai ya canja ra’ayi ya yi wa Nebukadnezzar tawaye.
En sus días, subió Nabucodonosor, rey de Babilonia, y Joacim fue su siervo por tres años; luego se rebeló contra él.
2 Ubangiji ya aiki maharan Babiloniyawa, da na Arameyawa, da na Mowabawa, da na Ammonawa. Ya aike su su hallaka Yahuda bisa ga maganar Ubangiji wadda ya furta ta bakin bayinsa annabawa.
Y el Señor envió contra él bandas de los caldeos y de los sirios y de los moabitas y de los hijos de Amón; enviándolos contra Judá para su destrucción, como había dicho por sus siervos los profetas.
3 Ba shakka waɗannan abubuwa sun faru da Yahuda bisa ga umarnin Ubangiji domin yă kawar da su daga gabansa saboda zunuban Manasse da dukan abin da ya yi,
Sólo por la palabra del Señor vino este destino a Judá, para apartarla de su rostro; por los pecados de Manasés y todo el mal que hizo;
4 haɗe da zub da jinin marasa laifi. Gama ya ƙazantar da Urushalima da jinin marasa laifi. Ubangiji kuwa bai yi niyyar yafewa ba.
Y por la muerte de los que no hicieron nada malo, porque llenó a Jerusalén de la sangre de los rectos; y el Señor no tenía perdón por ello.
5 Game da sauran ayyukan mulkin Yehohiyakim da abubuwan da ya aikata, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
Los demás hechos de Joacim, y todo lo que hizo, ¿no están registrados en el libro de las crónicas de los reyes de Judá?
6 Yehohiyakim ya huta da kakanninsa. Yehohiyacin ɗansa ya gāje shi.
Y Joacim durmió con sus padres; y Joaquín su hijo se convirtió en rey en su lugar.
7 Sarkin Masar bai sāke fita daga ƙasarsa don yaƙi ba domin sarkin Babilon ya mamaye yankin, daga Rafin Masar har zuwa Kogin Yuferites.
Y el rey de Egipto no volvió a salir de su tierra, porque el rey de Babilonia había tomado toda su tierra, desde la corriente de Egipto hasta el río Eufrates.
8 Yehohiyacin yana da shekara goma sha takwas da ya zama sarki, ya kuma yi mulki wata uku a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Nehushta’yar Elnatan, mutuniyar Urushalima.
Joaquín tenía dieciocho años cuando se convirtió en rey, gobernó en Jerusalén durante tres meses, y el nombre de su madre era Neusta, la hija de Elnatan de Jerusalén.
9 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji yadda mahaifinsa ya yi.
E hizo lo malo ante los ojos del Señor, como había hecho su padre.
10 A wannan lokaci, hafsoshin Nebukadnezzar sarkin Babilon suka kawo wa Urushalima yaƙi, suka kuma kewaye ta.
En ese momento, los ejércitos de Nabucodonosor llegaron a Jerusalén y la ciudad estaba cerrada por todos lados.
11 Nebukadnezzar na Babilon da kansa kuwa ya zo birnin yayinda hafsoshinsa suka kewaye ta.
Y llegó allí Nabucodonosor, rey de Babilonia, mientras sus siervos la tenían sitiada;
12 Yehohiyacin sarkin Yahuda, da mahaifiyarsa, da masu yi masa hidima, da hakimansa, da kuma fadawansa duk suka miƙa kansu ga Nebukadnezzar. A shekara ta takwas ta mulkin sarkin Babilon, sarkin Babilon ya mai da Yehohiyacin ɗan kurkuku.
Entonces Joaquín, rey de Judá, salió al rey de Babilonia y se rindieron, con su madre y sus siervos y sus jefes y sus oficiales y hombres de confianza; y en el octavo año del gobierno de Nabucodonosor.
13 Yadda Ubangiji ya faɗa, Nebukadnezzar ya kwashe dukan dukiyar haikalin Ubangiji, da ta fadan sarki, ya kuma kwashe dukan kayan zinariyar da Solomon sarkin Isra’ila ya ƙera domin haikalin Ubangiji.
Luego se llevó todas las riquezas almacenadas de la casa del Señor y los bienes de la casa del rey, cortando todas las vasijas de oro que Salomón, rey de Israel, había hecho en la casa del Señor, como el Señor había dicho.
14 Ya kwashi dukan mutanen Urushalima zuwa bauta, ya kwashi dukan fadawa, da mayaƙa, da masu sana’a, da maƙera, yawansu ya kai dubu goma. Ba wanda ya ragu, sai matalautan ƙasar.
Y se llevó a todos los habitantes de Jerusalén, a todos los jefes y a todos los hombres de guerra, diez mil prisioneros; y todos los trabajadores expertos y los trabajadores del metal; sólo el tipo más pobre de la gente de la tierra no fue quitado.
15 Nebukadnezzar ya ɗauki Yehohiyacin ya kai bauta a Babilon. Ya kuma kwashe mahaifiyar sarki, da matansa, da fadawansa, da manyan mutanen ƙasar daga Urushalima ya kai Babilon.
Tomó a Joaquín prisionero en Babilonia, con su madre y sus esposas, sus oficiales de confianza y los hombres importantes de la tierra; los tomó a todos como prisioneros de Jerusalén a Babilonia.
16 Sarkin Babilon kuma ya kwashe dukan mayaƙa dubu bakwai, ƙarfafu, shiryayyu don yaƙi, da masu sana’a, da maƙera dubu ɗaya, ya kai Babilon.
Y todos los hombres de guerra, siete mil de ellos, y mil trabajadores expertos y herreros, todos ellos fuertes, y aptos para la guerra, el rey de Babilonia se los llevó a Babilonia como prisioneros.
17 Sarkin Babilon ya sa Mattaniya, ɗan’uwan mahaifin Yehohiyacin, ya zama sarki a madadinsa, ya canja masa suna zuwa Zedekiya.
Y el rey de Babilonia hizo a Matanías, hermano de su padre, rey en lugar de Joaquín, cambiando su nombre a Sedequías.
18 Zedekiya yana da shekara ashirin da ɗaya da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekara goma sha ɗaya a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Hamutal’yar Irmiya; mutuniyar Libna.
Sedequías tenía veintiún años cuando comenzó a reinar, y fue rey en Jerusalén durante once años; El nombre de su madre era Hamutal, hija de Jeremías de Libna.
19 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji yadda Yehohiyakim ya yi.
E hizo lo malo ante los ojos del Señor, conforme a todo como lo había hecho Joacim.
20 Saboda fushin Ubangiji ne dukan waɗannan abubuwa suka faru da Urushalima, da kuma Yahuda, a ƙarshe kuma ya kawar da su daga fuskarsa. To, sai Zedekiya ya yi wa sarkin Babilon tawaye.
Y a causa de la ira del Señor, esto sucedió en Jerusalén y en Judá, hasta que los echó de su presencia; y Sedequías tomó las armas contra el rey de Babilonia.

< 2 Sarakuna 24 >