< 2 Sarakuna 24 >

1 A zamani Yehohiyakim, Nebukadnezzar sarkin Babilon ya kawo wa ƙasar farmaki, Yehohiyakim dai ya zama abokin tarayyarsa na tsawon shekara uku. Daga baya kuma sai ya canja ra’ayi ya yi wa Nebukadnezzar tawaye.
Viņa laikā Nebukadnecars, Bābeles ķēniņš, cēlās, un Jojaķims viņam bija par kalpu trīs gadus, tad viņš no tā atkal atkrita.
2 Ubangiji ya aiki maharan Babiloniyawa, da na Arameyawa, da na Mowabawa, da na Ammonawa. Ya aike su su hallaka Yahuda bisa ga maganar Ubangiji wadda ya furta ta bakin bayinsa annabawa.
Un Tas Kungs sūtīja pret viņu Kaldeju pulkus un Sīriešu pulkus un Moaba pulkus un Amona bērnu pulkus un tos sūtīja pret Jūdu, to izdeldēt, pēc Tā Kunga vārda, ko Viņš bija runājis caur Saviem kalpiem, tiem praviešiem.
3 Ba shakka waɗannan abubuwa sun faru da Yahuda bisa ga umarnin Ubangiji domin yă kawar da su daga gabansa saboda zunuban Manasse da dukan abin da ya yi,
Tiešām, pēc Tā Kunga vārda Jūdam tā notika, ka Viņš to atmeta nost no Sava vaiga Manasus grēku dēļ ko šis bija darījis,
4 haɗe da zub da jinin marasa laifi. Gama ya ƙazantar da Urushalima da jinin marasa laifi. Ubangiji kuwa bai yi niyyar yafewa ba.
Un to nenoziedzīgo asiņu dēļ, ko tas bija izlējis un Jeruzālemi piepildījis ar nenoziedzīgām asinīm; tāpēc Tas Kungs negribēja piedot.
5 Game da sauran ayyukan mulkin Yehohiyakim da abubuwan da ya aikata, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
Un kas vēl par Jojaķimu stāstāms, un viss, ko viņš darījis, tas ir rakstīts Jūda ķēniņu laiku grāmatā.
6 Yehohiyakim ya huta da kakanninsa. Yehohiyacin ɗansa ya gāje shi.
Un Jojaķims aizmiga saviem tēviem pakaļ, un viņa dēls Jojaķins palika par ķēniņu viņa vietā.
7 Sarkin Masar bai sāke fita daga ƙasarsa don yaƙi ba domin sarkin Babilon ya mamaye yankin, daga Rafin Masar har zuwa Kogin Yuferites.
Un Ēģiptes ķēniņš neizgāja vairs no savas zemes, jo Bābeles ķēniņš bija visu uzņēmis, kas Ēģiptes ķēniņam piederēja no Ēģiptes upes līdz Eifrat upei.
8 Yehohiyacin yana da shekara goma sha takwas da ya zama sarki, ya kuma yi mulki wata uku a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Nehushta’yar Elnatan, mutuniyar Urushalima.
Jojaķins bija astoņpadsmit gadus vecs, kad palika par ķēniņu, un valdīja trīs mēnešus Jeruzālemē. Un viņa mātei bija vārds Neūsta, Elnatana meita, no Jeruzālemes.
9 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji yadda mahaifinsa ya yi.
Un viņš darīja, kas Tam Kungam nepatika, tā kā viņa tēvs bija darījis.
10 A wannan lokaci, hafsoshin Nebukadnezzar sarkin Babilon suka kawo wa Urushalima yaƙi, suka kuma kewaye ta.
Tanī laikā Nebukadnecara, Bābeles ķēniņa, kalpi cēlās pret Jeruzālemi un apsēda to pilsētu.
11 Nebukadnezzar na Babilon da kansa kuwa ya zo birnin yayinda hafsoshinsa suka kewaye ta.
Un Nebukadnecars, Bābeles ķēniņš, pats nāca pret to pilsētu, kad viņa kalpi to spaidīja.
12 Yehohiyacin sarkin Yahuda, da mahaifiyarsa, da masu yi masa hidima, da hakimansa, da kuma fadawansa duk suka miƙa kansu ga Nebukadnezzar. A shekara ta takwas ta mulkin sarkin Babilon, sarkin Babilon ya mai da Yehohiyacin ɗan kurkuku.
Tad Jojaķins, Jūda ķēniņš, izgāja pie Bābeles ķēniņa ar savu māti un saviem kalpiem un saviem virsniekiem un kambarjunkuriem, un Bābeles ķēniņš to saņēma gūstā savas valdības astotā gadā.
13 Yadda Ubangiji ya faɗa, Nebukadnezzar ya kwashe dukan dukiyar haikalin Ubangiji, da ta fadan sarki, ya kuma kwashe dukan kayan zinariyar da Solomon sarkin Isra’ila ya ƙera domin haikalin Ubangiji.
Un viņš no turienes paņēma visas Tā Kunga nama mantas un visas ķēniņa nama mantas, un nolauzīja zeltu no visiem rīkiem, ko Salamans, Israēla ķēniņš, bija taisījis Tā Kunga namā, kā Tas Kungs bija runājis.
14 Ya kwashi dukan mutanen Urushalima zuwa bauta, ya kwashi dukan fadawa, da mayaƙa, da masu sana’a, da maƙera, yawansu ya kai dubu goma. Ba wanda ya ragu, sai matalautan ƙasar.
Un viņš aizveda cietumā visu Jeruzālemi, visus virsniekus un visus varenos, desmit tūkstošus, un visus būvmeistarus un kalējus, nekas neatlika, kā tikai zemes nabaga ļaudis.
15 Nebukadnezzar ya ɗauki Yehohiyacin ya kai bauta a Babilon. Ya kuma kwashe mahaifiyar sarki, da matansa, da fadawansa, da manyan mutanen ƙasar daga Urushalima ya kai Babilon.
Un viņš aizveda Jojaķinu uz Bābeli līdz ar ķēniņa māti un ķēniņa sievām un viņa kambarjunkuriem un zemes vareniem, tos viņš no Jeruzālemes noveda cietumā uz Bābeli.
16 Sarkin Babilon kuma ya kwashe dukan mayaƙa dubu bakwai, ƙarfafu, shiryayyu don yaƙi, da masu sana’a, da maƙera dubu ɗaya, ya kai Babilon.
Un visus stipros vīrus, septiņus tūkstošus, un amatniekus un kalējus, kādu tūkstoti, kas visi bija stipri vīri karā, tos Bābeles ķēniņš noveda uz Bābeli cietumā.
17 Sarkin Babilon ya sa Mattaniya, ɗan’uwan mahaifin Yehohiyacin, ya zama sarki a madadinsa, ya canja masa suna zuwa Zedekiya.
Un Bābeles ķēniņš cēla par ķēniņu viņa vietā Mataniju, viņa tēva brāli, un viņam deva vārdu Cedeķija.
18 Zedekiya yana da shekara ashirin da ɗaya da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekara goma sha ɗaya a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Hamutal’yar Irmiya; mutuniyar Libna.
Cedeķija bija divdesmit vienu gadu vecs, kad palika par ķēniņu, un valdīja vienpadsmit gadus Jeruzālemē, un viņa mātei bija vārds Amitala, Jeremijas meita, no Libnas.
19 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji yadda Yehohiyakim ya yi.
Un viņš darīja, kas Tam Kungam nepatika, tāpat, kā Jojaķims bija darījis.
20 Saboda fushin Ubangiji ne dukan waɗannan abubuwa suka faru da Urushalima, da kuma Yahuda, a ƙarshe kuma ya kawar da su daga fuskarsa. To, sai Zedekiya ya yi wa sarkin Babilon tawaye.
Bet tā notika caur Tā Kunga dusmību pret Jeruzālemi un Jūdu, tiekams Viņš tos bija atmetis nost no Sava vaiga. Un Cedeķija atkrita no Bābeles ķēniņa.

< 2 Sarakuna 24 >