< 2 Sarakuna 24 >
1 A zamani Yehohiyakim, Nebukadnezzar sarkin Babilon ya kawo wa ƙasar farmaki, Yehohiyakim dai ya zama abokin tarayyarsa na tsawon shekara uku. Daga baya kuma sai ya canja ra’ayi ya yi wa Nebukadnezzar tawaye.
Sous son règne, Nabuchodonozor, roi de Babylone, fit une invasion, et Joïakim devint son vassal pendant trois ans; ensuite il se révolta contre lui.
2 Ubangiji ya aiki maharan Babiloniyawa, da na Arameyawa, da na Mowabawa, da na Ammonawa. Ya aike su su hallaka Yahuda bisa ga maganar Ubangiji wadda ya furta ta bakin bayinsa annabawa.
Alors l’Eternel lâcha contre lui les bandes des Chaldéens, des Syriens, des Moabites et des Ammonites: tous ceux-ci, il les mit en mouvement contre Juda pour amener sa ruine, selon la parole divine qu’il avait fait annoncer par l’organe de ses serviteurs les prophètes.
3 Ba shakka waɗannan abubuwa sun faru da Yahuda bisa ga umarnin Ubangiji domin yă kawar da su daga gabansa saboda zunuban Manasse da dukan abin da ya yi,
Oui, c’était une sentence prononcée par l’Eternel contre Juda, de l’écarter de devant sa face, à cause de tous les péchés commis par Manassé,
4 haɗe da zub da jinin marasa laifi. Gama ya ƙazantar da Urushalima da jinin marasa laifi. Ubangiji kuwa bai yi niyyar yafewa ba.
et aussi à cause du sang innocent qu’il avait répandu et dont il avait inondé Jérusalem: l’Eternel ne voulut plus pardonner.
5 Game da sauran ayyukan mulkin Yehohiyakim da abubuwan da ya aikata, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
Les autres faits et gestes de Joïakim sont consignés dans le livre des annales des rois de Juda.
6 Yehohiyakim ya huta da kakanninsa. Yehohiyacin ɗansa ya gāje shi.
Joiakim s’endormit avec ses ancêtres, et son fils Joïachin régna à sa place.
7 Sarkin Masar bai sāke fita daga ƙasarsa don yaƙi ba domin sarkin Babilon ya mamaye yankin, daga Rafin Masar har zuwa Kogin Yuferites.
Dès lors, le roi d’Egypte ne continua plus à sortir de son pays, le roi de Babylone ayant conquis toutes les possessions du roi d’Egypte, depuis le torrent d’Egypte jusqu’au fleuve de l’Euphrate.
8 Yehohiyacin yana da shekara goma sha takwas da ya zama sarki, ya kuma yi mulki wata uku a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Nehushta’yar Elnatan, mutuniyar Urushalima.
Agé de dix-huit ans à son avènement, Joïachin régna trois mois à Jérusalem; le nom de sa mère était Nehouchta, fille d’Elnathan, de Jérusalem.
9 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji yadda mahaifinsa ya yi.
Il fit ce qui est mal aux yeux de l’Eternel, tout comme avait agi son père.
10 A wannan lokaci, hafsoshin Nebukadnezzar sarkin Babilon suka kawo wa Urushalima yaƙi, suka kuma kewaye ta.
En ce temps, les serviteurs de Nabuchodonozor marchèrent contre Jérusalem, et cette ville subit un siège.
11 Nebukadnezzar na Babilon da kansa kuwa ya zo birnin yayinda hafsoshinsa suka kewaye ta.
Nabuchodonozor, roi de Babylone, arriva lui-même pour attaquer la ville, pendant que ses serviteurs l’assiégeaient.
12 Yehohiyacin sarkin Yahuda, da mahaifiyarsa, da masu yi masa hidima, da hakimansa, da kuma fadawansa duk suka miƙa kansu ga Nebukadnezzar. A shekara ta takwas ta mulkin sarkin Babilon, sarkin Babilon ya mai da Yehohiyacin ɗan kurkuku.
Alors Joïachin, roi de Juda, sortit pour se rendre au roi de Babylone avec sa mère, ses serviteurs, ses grands et ses officiers; le roi de Babylone le fit prisonnier la huitième année de son règne.
13 Yadda Ubangiji ya faɗa, Nebukadnezzar ya kwashe dukan dukiyar haikalin Ubangiji, da ta fadan sarki, ya kuma kwashe dukan kayan zinariyar da Solomon sarkin Isra’ila ya ƙera domin haikalin Ubangiji.
Il emporta de Jérusalem tous les trésors de la maison de Dieu, ainsi que les trésors du palais royal, et il mit en pièces tous les vases d’or faits par Salomon pour le sanctuaire divin. C’Est ce que l’Eternel avait prédit.
14 Ya kwashi dukan mutanen Urushalima zuwa bauta, ya kwashi dukan fadawa, da mayaƙa, da masu sana’a, da maƙera, yawansu ya kai dubu goma. Ba wanda ya ragu, sai matalautan ƙasar.
Il emmena en exil tout Jérusalem, tous les grands et tous les vaillants hommes de guerre, au nombre de dix mille exilés, ainsi que tous les forgerons et serruriers; il ne resta sur place que la classe inférieure de la population du pays.
15 Nebukadnezzar ya ɗauki Yehohiyacin ya kai bauta a Babilon. Ya kuma kwashe mahaifiyar sarki, da matansa, da fadawansa, da manyan mutanen ƙasar daga Urushalima ya kai Babilon.
Il envoya aussi Joïachin captif à Babylone; de même la mère du roi, les femmes du roi, ses eunuques et les personnages d’élite du pays, il les emmena en exil de Jérusalem à Babylone.
16 Sarkin Babilon kuma ya kwashe dukan mayaƙa dubu bakwai, ƙarfafu, shiryayyu don yaƙi, da masu sana’a, da maƙera dubu ɗaya, ya kai Babilon.
En outre, tous les hommes de guerre, au nombre de sept mille, les forgerons et serruriers, au nombre de mille, tous gens vaillants, habitués à la guerre, le roi de Babylone les conduisit en captivité à Babylone.
17 Sarkin Babilon ya sa Mattaniya, ɗan’uwan mahaifin Yehohiyacin, ya zama sarki a madadinsa, ya canja masa suna zuwa Zedekiya.
Le roi de Babylone établit comme roi, à la place de Joïachin, son oncle Mathania, dont il changea le nom en celui de Sédécias.
18 Zedekiya yana da shekara ashirin da ɗaya da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekara goma sha ɗaya a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Hamutal’yar Irmiya; mutuniyar Libna.
Sédécias avait vingt et un ans à son avènement, et il régna onze ans à Jérusalem; le nom de sa mère était Hamoutal, fille de Jérémie, de Libna.
19 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji yadda Yehohiyakim ya yi.
Il fit ce qui est mal aux yeux de l’Eternel, tout comme avait agi Joïakim.
20 Saboda fushin Ubangiji ne dukan waɗannan abubuwa suka faru da Urushalima, da kuma Yahuda, a ƙarshe kuma ya kawar da su daga fuskarsa. To, sai Zedekiya ya yi wa sarkin Babilon tawaye.
C’Est ainsi que la colère de Dieu se manifesta contre Jérusalem et Juda, jusqu’à ce qu’il les eût rejetés de devant sa face. Or, Sédécias entra en révolte contre le roi de Babylone.