< 2 Sarakuna 24 >
1 A zamani Yehohiyakim, Nebukadnezzar sarkin Babilon ya kawo wa ƙasar farmaki, Yehohiyakim dai ya zama abokin tarayyarsa na tsawon shekara uku. Daga baya kuma sai ya canja ra’ayi ya yi wa Nebukadnezzar tawaye.
In his days Nabuchodonosor king of Babylon came up, and Joakim became his servant three years: then again he rebelled against him.
2 Ubangiji ya aiki maharan Babiloniyawa, da na Arameyawa, da na Mowabawa, da na Ammonawa. Ya aike su su hallaka Yahuda bisa ga maganar Ubangiji wadda ya furta ta bakin bayinsa annabawa.
And the Lord sent against him the rovers of the Chaldees, and the rovers of Syria, and the rovers of Moab, and the rovers of the children of Ammon: and he sent them against Juda, to destroy it, according to the word of the Lord, which he had spoken by his servants the prophets.
3 Ba shakka waɗannan abubuwa sun faru da Yahuda bisa ga umarnin Ubangiji domin yă kawar da su daga gabansa saboda zunuban Manasse da dukan abin da ya yi,
And this came by the word of the Lord against Juda, to remove them from before him for all the sins of Manasses which he did.
4 haɗe da zub da jinin marasa laifi. Gama ya ƙazantar da Urushalima da jinin marasa laifi. Ubangiji kuwa bai yi niyyar yafewa ba.
And for the innocent blood that he shed, filling Jerusalem with innocent blood: and therefore the Lord would not be appeased.
5 Game da sauran ayyukan mulkin Yehohiyakim da abubuwan da ya aikata, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
But the rest of the acts of Joakim, and all that he did, are they not written in the book of the words of the days of the kings of Juda? And Joakim slept with his fathers:
6 Yehohiyakim ya huta da kakanninsa. Yehohiyacin ɗansa ya gāje shi.
And Joachin his son reigned in his stead.
7 Sarkin Masar bai sāke fita daga ƙasarsa don yaƙi ba domin sarkin Babilon ya mamaye yankin, daga Rafin Masar har zuwa Kogin Yuferites.
And the king of Egypt came not again any more out of his own country: for the king of Babylon had taken all that had belonged to the king of Egypt, from the river of Egypt, unto the river Euphrates.
8 Yehohiyacin yana da shekara goma sha takwas da ya zama sarki, ya kuma yi mulki wata uku a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Nehushta’yar Elnatan, mutuniyar Urushalima.
Joachin was eighteen years old when he began to reign, a and he reigned three months in Jerusalem: the name of his mother was Nohesta the daughter of Elnathan of Jerusalem.
9 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji yadda mahaifinsa ya yi.
And he did evil before the Lord, according to all that his father had done.
10 A wannan lokaci, hafsoshin Nebukadnezzar sarkin Babilon suka kawo wa Urushalima yaƙi, suka kuma kewaye ta.
At that time the servants of Nabuchodonosor king of Babylon came up against Jerusalem, and the city was surrounded with their forts.
11 Nebukadnezzar na Babilon da kansa kuwa ya zo birnin yayinda hafsoshinsa suka kewaye ta.
And Nabuchodonosor king of Babylon came to the city with his servants to assault it.
12 Yehohiyacin sarkin Yahuda, da mahaifiyarsa, da masu yi masa hidima, da hakimansa, da kuma fadawansa duk suka miƙa kansu ga Nebukadnezzar. A shekara ta takwas ta mulkin sarkin Babilon, sarkin Babilon ya mai da Yehohiyacin ɗan kurkuku.
And Joachin king of Juda went out to the king of Babylon, he and his mother, and his servants, and his nobles, and his eunuchs: and the king of Babylon received him in the eighth year of his reign.
13 Yadda Ubangiji ya faɗa, Nebukadnezzar ya kwashe dukan dukiyar haikalin Ubangiji, da ta fadan sarki, ya kuma kwashe dukan kayan zinariyar da Solomon sarkin Isra’ila ya ƙera domin haikalin Ubangiji.
And he brought out from thence all the treasures of the house of the Lord, and the treasures of the king’s house: and he cut in pieces all the vessels of gold which Solomon king of Israel had made in the temple of the Lord, according to the word of the Lord.
14 Ya kwashi dukan mutanen Urushalima zuwa bauta, ya kwashi dukan fadawa, da mayaƙa, da masu sana’a, da maƙera, yawansu ya kai dubu goma. Ba wanda ya ragu, sai matalautan ƙasar.
And he carried away all Jerusalem, and all the princes, and all the valiant men of the army, to the number of ten thousand into captivity: and every artificer and smith: and none were left, but the poor sort of the people of the land.
15 Nebukadnezzar ya ɗauki Yehohiyacin ya kai bauta a Babilon. Ya kuma kwashe mahaifiyar sarki, da matansa, da fadawansa, da manyan mutanen ƙasar daga Urushalima ya kai Babilon.
And he carried away Joachin into Babylon, and the king’s mother, and the king’s wives, and his eunuchs: and the judges of the land he carried into captivity from Jerusalem into Babylon.
16 Sarkin Babilon kuma ya kwashe dukan mayaƙa dubu bakwai, ƙarfafu, shiryayyu don yaƙi, da masu sana’a, da maƙera dubu ɗaya, ya kai Babilon.
And all the strong men, seven thousand, and the artificers, and the smiths a thousand, all that were valiant men and fit for war: and the king of Babylon led them captives into Babylon.
17 Sarkin Babilon ya sa Mattaniya, ɗan’uwan mahaifin Yehohiyacin, ya zama sarki a madadinsa, ya canja masa suna zuwa Zedekiya.
And he appointed Matthanias his uncle in his stead: and called his name Sedecias.
18 Zedekiya yana da shekara ashirin da ɗaya da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekara goma sha ɗaya a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Hamutal’yar Irmiya; mutuniyar Libna.
Sedecias was one and twenty years old when he began to reign, and he reigned eleven years in Jerusalem: the name of his mother was Amital, the daughter of Jeremias of Lobna.
19 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji yadda Yehohiyakim ya yi.
And he did evil before the Lord, according to all that Joakim had done.
20 Saboda fushin Ubangiji ne dukan waɗannan abubuwa suka faru da Urushalima, da kuma Yahuda, a ƙarshe kuma ya kawar da su daga fuskarsa. To, sai Zedekiya ya yi wa sarkin Babilon tawaye.
For the Lord was angry against Jerusalem and against Juda, till he cast them out from his face: and Sedecias revolted from the king of Babylon.