< 2 Sarakuna 24 >

1 A zamani Yehohiyakim, Nebukadnezzar sarkin Babilon ya kawo wa ƙasar farmaki, Yehohiyakim dai ya zama abokin tarayyarsa na tsawon shekara uku. Daga baya kuma sai ya canja ra’ayi ya yi wa Nebukadnezzar tawaye.
E ndalo loch Jehoyakim, Nebukadneza ruodh Babulon nomonjo piny kendo Jehoyakim nobedo e bwo lochne kuom higni adek. To bangʼe noloko pache mokwedo Nebukadneza.
2 Ubangiji ya aiki maharan Babiloniyawa, da na Arameyawa, da na Mowabawa, da na Ammonawa. Ya aike su su hallaka Yahuda bisa ga maganar Ubangiji wadda ya furta ta bakin bayinsa annabawa.
Jehova Nyasaye nooro jo-Babulon, jo-Aram, jo-Moab kod jo-Amon mondo omonj ruoth Jehoyakim. Ne oorogi mondo otiek Juda, kaluwore gi wach mane Jehova Nyasaye owacho kokalo kuom jotichne ma jonabi.
3 Ba shakka waɗannan abubuwa sun faru da Yahuda bisa ga umarnin Ubangiji domin yă kawar da su daga gabansa saboda zunuban Manasse da dukan abin da ya yi,
Kuom adier gigi notimore ne Juda mana kaka Jehova Nyasaye nochiko, mondo mi ogolgi e nyime nikech richo mar Manase kod gik moko duto mane osetimo,
4 haɗe da zub da jinin marasa laifi. Gama ya ƙazantar da Urushalima da jinin marasa laifi. Ubangiji kuwa bai yi niyyar yafewa ba.
kaachiel gichwero remo maonge ketho. Jehova Nyasaye ne ok oikore mar weyone richone nikech nosechwero remo maonge ketho mopongʼogo Jerusalem.
5 Game da sauran ayyukan mulkin Yehohiyakim da abubuwan da ya aikata, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
Kuom gik mamoko duto mag ndalo loch Jehoyakim kod gik moko duto mane otimo, donge ondikgi e kitepe mag weche ruodhi mag Juda?
6 Yehohiyakim ya huta da kakanninsa. Yehohiyacin ɗansa ya gāje shi.
Jehoyakim notho moyweyo gi kwerene, kendo Jehoyakin wuode nobedo ruoth kare.
7 Sarkin Masar bai sāke fita daga ƙasarsa don yaƙi ba domin sarkin Babilon ya mamaye yankin, daga Rafin Masar har zuwa Kogin Yuferites.
Ruodh Misri ne ok owuok kendo e pinye nikech ruodh Babulon nokawo tongʼ mage duto chakre Wadi manie piny Misri nyaka e Aora Yufrate.
8 Yehohiyacin yana da shekara goma sha takwas da ya zama sarki, ya kuma yi mulki wata uku a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Nehushta’yar Elnatan, mutuniyar Urushalima.
Jehoyakin ne ja-higni apar gaboro kane odoko ruoth, kendo nobedo e loch kuom dweche adek kodak Jerusalem. Min mare ne nyinge Nehushta nyar Elnathan, ma aa Jerusalem.
9 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji yadda mahaifinsa ya yi.
Notimo timbe maricho e nyim wangʼ Jehova Nyasaye, mana kaka wuon mare notimo.
10 A wannan lokaci, hafsoshin Nebukadnezzar sarkin Babilon suka kawo wa Urushalima yaƙi, suka kuma kewaye ta.
E kindeno jodong Nebukadneza ruoth Babulon nodonjo e Jerusalem mokawe,
11 Nebukadnezzar na Babilon da kansa kuwa ya zo birnin yayinda hafsoshinsa suka kewaye ta.
kendo Nebukadneza owuon nobiro nyaka dala maduongʼ ka jodonge olworo dala maduongʼno.
12 Yehohiyacin sarkin Yahuda, da mahaifiyarsa, da masu yi masa hidima, da hakimansa, da kuma fadawansa duk suka miƙa kansu ga Nebukadnezzar. A shekara ta takwas ta mulkin sarkin Babilon, sarkin Babilon ya mai da Yehohiyacin ɗan kurkuku.
Jehoyakin ruodh Juda, min mare, jotende jodonge kod jongʼadne rieko duto nochiwore e lwet ruodh Babulon. Jehoyakin noket e twech e higa mar aboro mar Loch ruodh Babulon.
13 Yadda Ubangiji ya faɗa, Nebukadnezzar ya kwashe dukan dukiyar haikalin Ubangiji, da ta fadan sarki, ya kuma kwashe dukan kayan zinariyar da Solomon sarkin Isra’ila ya ƙera domin haikalin Ubangiji.
Mana kaka Jehova Nyasaye nosewacho, Nebukadneza nogolo mwandu duto mane ni e hekalu mar Jehova Nyasaye kendo e kar dak ruoth, mi okawo gik molos gi dhahabu duto mane ruoth Solomon ruodh Israel olosone hekalu mar Jehova Nyasaye.
14 Ya kwashi dukan mutanen Urushalima zuwa bauta, ya kwashi dukan fadawa, da mayaƙa, da masu sana’a, da maƙera, yawansu ya kai dubu goma. Ba wanda ya ragu, sai matalautan ƙasar.
Ruoth Nebukadneza notero jo-Jerusalem alufu apar e twech mane gin jodongo duto kod jolweny, gi joma olony e tich lwedo kod jogoro. Onge ngʼato mane odongʼ makmana joma odhier.
15 Nebukadnezzar ya ɗauki Yehohiyacin ya kai bauta a Babilon. Ya kuma kwashe mahaifiyar sarki, da matansa, da fadawansa, da manyan mutanen ƙasar daga Urushalima ya kai Babilon.
Nebukadneza notero Jehoyakin e twech Babulon, kaachiel gi min ruoth, monde, jodonge kod jodong gwengʼ kogologi Jerusalem.
16 Sarkin Babilon kuma ya kwashe dukan mayaƙa dubu bakwai, ƙarfafu, shiryayyu don yaƙi, da masu sana’a, da maƙera dubu ɗaya, ya kai Babilon.
Bende ruodh Babulon notero e twech jolweny duto madirom ji alufu abiriyo, kaachiel gi joma olony kuom tich lwedo kod jogoro alufu achiel; giduto ne gin roteke moromo kedo.
17 Sarkin Babilon ya sa Mattaniya, ɗan’uwan mahaifin Yehohiyacin, ya zama sarki a madadinsa, ya canja masa suna zuwa Zedekiya.
Ne oketo Matania, ma owadgi Jehoyakin mondo obed ruoth kare kendo noloko nyinge ni Zedekia.
18 Zedekiya yana da shekara ashirin da ɗaya da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekara goma sha ɗaya a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Hamutal’yar Irmiya; mutuniyar Libna.
Zedekia ne ja-higni piero ariyo gachiel kane obedo ruoth, kendo nobedo e loch kodak Jerusalem kuom higni apar gachiel. Min mare ne nyinge Hamutal nyar Jeremia; ma aa Libna.
19 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji yadda Yehohiyakim ya yi.
Ne otimo richo e nyim Jehova Nyasaye mana kaka Jehoyakim notimo.
20 Saboda fushin Ubangiji ne dukan waɗannan abubuwa suka faru da Urushalima, da kuma Yahuda, a ƙarshe kuma ya kawar da su daga fuskarsa. To, sai Zedekiya ya yi wa sarkin Babilon tawaye.
Magi duto notimore ne Jerusalem kod Juda nikech mirimb Jehova Nyasaye kendo giko to ne oriembogi oko e nyime. Koro Zedekia nongʼanyone ruodh Babulon modagi lochne.

< 2 Sarakuna 24 >