< 2 Sarakuna 23 >
1 Sai sarki ya kira dukan dattawan Yahuda da Urushalima.
И возвестиша сия глаголы цареви: и посла царь, и собра к себе вся старейшины Иудины и Иерусалимляны,
2 Sai ya haura zuwa cikin haikalin Ubangiji tare da mutanen Yahuda, da na Urushalima, da firistoci, da annabawa, dukan mutane, manya da ƙanana. Ya karanta musu duk kalmomin Littafin Alkawari, wanda aka samu a haikalin Ubangiji.
и вниде царь в дом Господень, и вси мужие Иудины и вси живущии во Иерусалиме с ним, и жерцы, и пророцы, и вси людие от мала и до велика, и прочте во ушеса их вся словеса книги завета обретшияся в дому Господни:
3 Sarki ya tsaya dab da ginshiƙi ya kuma sabunta alkawarin a gaban Ubangiji, ya ce zai bi Ubangiji, yă kiyaye dokokinsa, da ƙa’idodinsa, da farillansa, da dukan zuciyarsa da dukan ransa, ta haka ya tabbatar da kalmomin alkawarin da yake a rubuce a cikin littafin nan. Sa’an nan dukan mutane ma suka yi alkawari yin haka.
и ста царь у столпа и завеща завет пред Господем, еже ходити вслед Господа и хранити заповеди Его и свидения Его и оправдания Его всем сердцем и всею душею, еже возставити словеса завета сего, яже писана в книзе сей. И сташа вси людие в завете.
4 Sai Yosiya ya umarci Hilkiya babban firist, tare da firistocin da suke taimakonsa, da masu tsaron ƙofa su kawar da dukan abubuwan da aka yi domin Ba’al, da domin Ashera, da kuma domin dukan rundunar taurari, daga haikalin Ubangiji. Ya ƙone su a bayan Urushalima a filayen Kwarin Kidron, ya kwashe tokan zuwa Betel.
И заповеда царь Хелкии жерцу великому и жерцем вторым и стрегущым врат изнести от храма Господня вся сосуды сотвореныя Ваалу и Дубраве и всей силе небесней, и сожже и вне Иерусалима в Садимофе Кедрсте и изверже прах их в Вефиль:
5 Ya kawar da firistocin gumakan da sarakunan Yahuda suka naɗa don su ƙona turare a masujadan kan tuddai na garuruwan Yahuda, da kuma waɗanda suke kewaye da Urushalima, masu ƙona turare wa Ba’al, rana da wata, ga rukunin taurari, da kuma ga dukan rundunan taurari.
и сожже хомаримы, ихже даша царие Иудины, и кадяху в высоких и во градех Иудиных и во окрестных Иерусалима, и кадящих Ваалу, и солнцу, и луне, и планетам и всей силе небесней:
6 Ya ɗauke ginshiƙin Ashera daga haikalin Ubangiji zuwa Kwarin Kidron can bayan Urushalima, ya ƙone shi a can. Ya niƙa shi sai da ya zama toka, sai ya watsar da ƙurar a filin kabarin talakawa.
и изнесе кумир из храма Господня вне Иерусалима на поток Кедрск, и сожже его в потоце Кедрсте, и истни в прах, и вверже прах их в гробы сынов людских:
7 Ya kuma rurrushe mazaunan karuwai mazan haikali waɗanda suke a haikalin Ubangiji, da kuma inda mata suke yi wa Ashera saƙa.
и разруши храм кадисимов, иже бе в храме Господни, идеже жены прядяху ризы кумиру:
8 Yosiya ya kawo dukan firistoci daga garuruwan Yahuda, ya kuma lalatar da masujadan kan tuddai daga Geba har zuwa Beyersheba, inda firistoci suke ƙona turare. Ya rurrushe matsafai a ƙofofi shigan gari na mashigi zuwa Ƙofar Yoshuwa, gwamnan birnin, wanda yake a hagu da ƙofar birnin.
и возведе вся жерцы от градов Иудиных, и оскверни высокая, идеже кадяху жерцы, от Гаваи да Вирсавеи: и разруши храм врат, иже бе при дверех врат Иисуса князя граднаго, иже ошуюю входящым дверми града.
9 Ko da yake firistocin masujadan kan tuddai ba su yi hidima a bagaden Ubangiji a Urushalima ba, sun ci burodi marar yisti tare da sauran firistoci.
Обаче не вхождаху жерцы высоких ко олтарю Господню во Иерусалиме, но токмо ядяху опресноки посреде братии своея.
10 Ya lalatar da Tofet, wanda yake a Kwarin Ben Hinnom, don kada kowa yă iya yin amfani da wurin don yă miƙa hadayar ɗansa, ko’yarsa a wuta ga Molek.
И оскверни Тафефа, иже в дебри сынов Еномлих, еже не превести мужу сына своего и мужу дщере своея Молоху сквозе огнь:
11 Ya kawar da dawakan nan da sarakunan Yahuda suka keɓe wa gumakan nan na rana daga mashigin haikalin Ubangiji. Waɗannan dawakan suna kusa da ɗakin Natan Melek, ɗaya daga cikin dattawan sarki. Yosiya ya kuma ƙone kekunan yaƙi a yin sujada ga gumakan nan rana.
и сожже кони, ихже даша царие Иудины солнцу во входе храму Господня, при влагалищи Нафана, царева скопца во Фаруриме: и колесницу солнечную сожже огнем:
12 Ya rushe bagadan da sarakunan Yahuda suka kafa a kan ɗakin sama kusa da ɗakin sama na Ahaz, da kuma bagadai biyu da Manasse ya gina a filaye biyu na haikalin Ubangiji. Ya kawar da su daga can, ya farfashe su, ya zubar da tarkacen a Kwarin Kidron.
и олтари, яже на крове горницы Ахазовы, яже сотвориша царие Иудины и олтари, иже созда Манассиа во двою двору храма Господня, раскопа царь, и сверже оттуду, и всыпа прах их в поток Кедрск:
13 Sarkin kuma ya lalatar da masujadan kan tuddan da suke gabas da Urushalima, kudu da Tudun Hallaka, waɗanda Solomon sarkin Isra’ila ya gina don Ashtarot, ƙazantacciyar alliyar Sidoniyawa, da Kemosh ƙazantaccen allah na Mowab, da kuma Molek allahn banƙyama na mutanen Ammon.
и храм, иже пред лицем Иерусалима, одесную горы Мосфаф, егоже созда Соломон царь Израилев Астарте мерзости Сидонстей и Хамосу мерзости Моавли и Молхолу мерзости сынов Аммоних, оскверни царь:
14 Yosiya ya farfashe keɓaɓɓun duwatsu, ya rurrushe ginshiƙan Asheransu, ya baza ƙasusuwan mutane a can.
и сокруши столпы, и искорени дубравы, и наполни места их костми человеческими:
15 Har ma da bagaden Betel, masujadan kan tudun da Yerobowam ɗan Nebat ya yi, wanda ya sa Isra’ila suka yi zunubi. Wannan bagade da masujadan kan tudun ma ya kawar, ya ƙone masujadan kan tudun, ya niƙa su, ya kuma ƙone ginshiƙin Ashera.
и олтарь иже во Вефили высокий, егоже сотвори Иеровоам сын Наватов, иже в грех введе Израиля, и олтарь той высокий раскопа, и сокруши камение его, и истни в прах, и сожже кумиры.
16 Da Yosiya ya dubi kewaye da shi, ya ga kaburburan da suke can a gefen tudu, sai ya sa aka kwaso ƙasusuwan da suke cikinsu aka ƙone a kan bagade don yă lalatar da shi bisa ga maganar Ubangiji ta bakin mutumin Allah, wanda ya yi annabcin waɗannan abubuwa.
И восклонися Иосиа, и виде гробы сущыя во граде тамо, и посла, и взя кости от гроб, и сожже на олтари, и оскверни его по глаголу Господню, егоже глагола человек Божий, егда стояше Иеровоам в праздник пред олтарем: и обращься возведе очи свои на гроб человека Божия глаголавшаго словеса сия.
17 Sarkin ya yi tambaya, ya ce, “Wane kabari ke nan nake gani?” Mutanen birnin suka ce, “Ai, kabarin annabin Allah ne wanda ya fito daga Yahuda, shi ne ya yi annabcin waɗannan abubuwan da ka aikata gāba da bagaden Betel.”
И рече: что могила сия, юже аз вижду? И реша ему мужие града: гроб сей человека Божия есть, иже прииде от Иуды и проглагола словеса сия, яже сотворил еси ныне над олтарем, иже в Вефили.
18 Sai ya ce, “Ku rabu da shi, kada wani yă dami ƙasusuwansa.” Saboda haka suka bar kasusuwansa, da na annabin da ya fito Samariya.
И рече: оставите его, да не подвижет ни един муж костей его. И оставиша кости его с костьми пророка пришедшаго от Самарии.
19 Kamar yadda ya yi a Betel, Yosiya ya kawar da dukan ɗakunan gumaka a kan tuddan da sarakunan Isra’ila suka gina a garuruwan Samariya, waɗanda suka tozarta Ubangiji.
Еще и вся храмы высоких сущих во градех Самарийских, яже сотвориша царие Израилевы прогневляюще Господа, отверже Иосиа, и сотвори им вся дела, яже сотвори в Вефили,
20 Yosiya ya yayyanka dukan firistoci na waɗannan masujadan kan tuddai, ya kuma ƙone ƙasusuwan mutane a kansu. Sa’an nan ya koma Urushalima.
и закла вся жерцы высоких сущыя тамо пред олтарми, и сожже на них кости человечи, и возвратися во Иерусалим.
21 Sarkin ya ba da umarnin nan ga dukan mutane, cewa, “Ku yi Bikin Ƙetarewa ga Ubangiji Allahnku, yadda aka rubuta a Littafin Alkawari.”
И заповеда царь всем людем, глаголя: сотворите пасху Господеви Богу нашему, якоже писано в книзе завета сего:
22 Ba a taɓa yin irin Bikin Ƙetarewa haka ba, tun zamanin da masu shari’a suke aiki a matsayin sarakuna, ko a kwanakin sarakunan Isra’ila, ko na Yahuda.
яко не бысть пасха сия от дний судий, иже судиша Израилеви, и во всех днех царей Израилевых и царей Иудиных:
23 Amma a shekara ta goma sha takwas ta mulkin sarki Yosiya, aka yi Bikin Ƙetarewan nan ga Ubangiji a Urushalima.
но токмо во осмоенадесять лето царя Иосии бысть пасха Господу во Иерусалиме.
24 Ban da haka, Yosiya ya kawar da masu duba, da masu maita, da allolin gidaje, da gumaka, da duk wani abin banƙyaman da ya gani a Yahuda da Urushalima. Ya yi wannan domin yă cika wa’adodin shari’a yadda suke a littafin da Hilkiya firist ya samu a haikalin Ubangiji.
Еще и волшебники, и вражбиты, и ферафимы, и кумиры, и вся мерзости бывшыя в земли Иудине и во Иерусалиме, искорени царь Иосиа, да утвердит словеса законная писанная в книзе, юже обрете Хелкиа жрец в храме Господни.
25 Babu wani sarki kafin Yosiya, ko kuma a bayansa, wanda ya juya ga Ubangiji da dukan zuciyarsa, da dukan ransa, da dukan ƙarfinsa bisa ga shari’ar Musa, kamar yadda ya yi.
Подобен ему не бысть пред ним царь, иже обратися к Господеви всем сердцем своим и всею душею своею и всею силою своею по всему закону Моисеову, и по нем не воста подобен ему.
26 Duk da haka, Ubangiji bai huce daga zafin fushinsa wanda ya ƙuna game da Yahuda saboda abin da Manasse ya aikata don yă tozarta shi ba.
Обаче не отвратися Господь от ярости гнева Своего великаго, имже возярися гневом на Иуду, на прогневания, имиже прогнева Его Манассиа,
27 Saboda haka Ubangiji ya ce, “Zan shafe Yahuda ma kamar yadda na shafe Isra’ila, daga gabana, zan ƙi Urushalima birnin da na zaɓa, da wannan haikali wanda na ce, ‘A can Sunana zai kasance.’”
и рече Господь: еще и Иуду отрину от лица Моего, якоже отринух Израиля, и град сей отвергу, егоже избрах, Иерусалима, и храм, о немже рех: будет имя Мое ту.
28 Game da sauran ayyukan mulkin Yosiya, da duk abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
И прочая словес Иосиевых, и вся елика сотвори, не сия ли написана в книзе словес дний царей Иудиных?
29 Yayinda Yosiya yake sarki, Fir’auna Neko, sarkin Masar ya haura zuwa Kogin Yuferites don yă taimaki sarkin Assuriya da yaƙi. Sarki Yosiya kuwa ya yi ƙoƙari ya hana shi wucewa, sa’ad da Fir’auna Neko ya gan shi, sai ya kashe shi a filin yaƙi a Megiddo.
Во днех же его взыде фараон Нехао царь Египетск на царя Ассирийска на реку Евфрат: и изыде царь Иосиа на сретение ему, и уби его Нехао царь в Магеддоне, егда его узре.
30 Bayin Yosiya suka ɗauko gawarsa daga Megiddo suka kai Urushalima, suka binne shi a kabarinsa. Sai mutanen ƙasar suka ɗauki Yehoyahaz ɗan Yosiya suka naɗa shi sarki a madadin mahaifinsa.
И взяша его отроцы его мертва из Магеддона и принесоша его во Иерусалим, и погребоша его во гробе его во граде Давидове. И пояша людие земли тоя Иоахаза сына Иосиина и помазаша его, и воцариша его вместо отца его.
31 Yehoyahaz yana da shekara ashirin da uku sa’ad da ya zama sarki. Ya yi mulki na wata uku a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Hamutal’yar Irmiya; mutuniyar Libna.
Сын двадесяти и триех лет бе Иоахаз, внегда нача царствовати и три месяцы царствова во Иерусалиме. Имя же матери его Амитала, дщи Иеремии из Ловны.
32 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, yadda kakanninsa suka yi.
И сотвори лукавое пред очима Господнима, по всем елика сотвориша отцы его.
33 Fir’auna Neko ya sa shi a sarƙa a Ribla a ƙasar Hamat don kada yă yi mulki a Urushalima, sa’an nan ya sa wa Yahuda harajin talenti ɗari na azurfa, da talenti ɗaya na zinariya.
И пресели его фараон Нехао в Ревлаам в землю Емаф, да не царствует во Иерусалиме, и возложи дань на землю ту сто талант сребра и сто талант злата.
34 Fir’auna Neko ya naɗa Eliyakim ɗan Yosiya sarki a maimakon mahaifinsa, ya kuma canja masa suna zuwa Yehohiyakim. Ya ɗauki Yehoyahaz ya kai Masar, a can ya mutu.
И постави царем фараон Нехао над ними Елиакима, сына Иосии царя Иудина, вместо Иосии отца его, и премени имя ему Иоаким: Иоахаза же взя и введе во Египет и умре тамо.
35 Yehohiyakim ya riƙa biyan Fir’auna Neko azurfa da zinariyar da ya umarta. Don yă yi haka sai ya riƙa karɓar azurfa da zinariya daga mutanen ƙasar, kowa bisa ga ƙarfinsa.
И сребро и злато даде Иоаким фараону, обаче написа землю даяти сребро по словеси фараоню: муж по оценению своему даяше сребро и злато от людий земли тоя даяти фараону Нехао.
36 Yehohiyakim yana da shekara ashirin da biyar sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekara goma sha ɗaya a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Zebuda’yar Fedahiya, mutuniyar Ruma.
Сын бе двадесяти и пяти лет Иоаким, егда нача царствовати, и единонадесять лет царствова во Иерусалиме. Имя же матери его Иелдаф, дщи Фадаиля, от Румы.
37 Ya kuma aika mugunta a gaban Ubangiji yadda kakanninsa suka yi.
И сотвори лукавое пред очима Господнима, по всем елика сотвориша отцы его.