< 2 Sarakuna 23 >

1 Sai sarki ya kira dukan dattawan Yahuda da Urushalima.
Inkosi yasithumela, basebebuthanisa kuye bonke abadala bakoJuda labeJerusalema.
2 Sai ya haura zuwa cikin haikalin Ubangiji tare da mutanen Yahuda, da na Urushalima, da firistoci, da annabawa, dukan mutane, manya da ƙanana. Ya karanta musu duk kalmomin Littafin Alkawari, wanda aka samu a haikalin Ubangiji.
Inkosi yasisenyukela endlini kaJehova, lawo wonke amadoda akoJuda labo bonke abahlali beJerusalema kanye laye, labapristi labaprofethi, labo bonke abantu kusukela komncinyane kusiya komkhulu, yasifunda endlebeni zabo wonke amazwi ogwalo lwesivumelwano olwaficwa endlini yeNkosi.
3 Sarki ya tsaya dab da ginshiƙi ya kuma sabunta alkawarin a gaban Ubangiji, ya ce zai bi Ubangiji, yă kiyaye dokokinsa, da ƙa’idodinsa, da farillansa, da dukan zuciyarsa da dukan ransa, ta haka ya tabbatar da kalmomin alkawarin da yake a rubuce a cikin littafin nan. Sa’an nan dukan mutane ma suka yi alkawari yin haka.
Inkosi yema-ke ngasensikeni, yenza isivumelwano phambi kweNkosi, sokuhamba emva kweNkosi, lokugcina imilayo yayo lemithetho yayo lezimiso zayo ngenhliziyo yonke langomphefumulo wonke, ukuqinisa amazwi alesisivumelwano abhaliweyo kulolugwalo. Bonke abantu basebesima esivumelwaneni.
4 Sai Yosiya ya umarci Hilkiya babban firist, tare da firistocin da suke taimakonsa, da masu tsaron ƙofa su kawar da dukan abubuwan da aka yi domin Ba’al, da domin Ashera, da kuma domin dukan rundunar taurari, daga haikalin Ubangiji. Ya ƙone su a bayan Urushalima a filayen Kwarin Kidron, ya kwashe tokan zuwa Betel.
Inkosi yasilaya uHilikhiya umpristi omkhulu labapristi besigaba sesibili labalindi bombundu womnyango ukuthi bakhuphe ethempelini leNkosi zonke izitsha ezazenzelwe uBhali lesixuku lebutho lonke lamazulu, wazitshisela ngaphandle kweJerusalema eziqintini zeKidroni, wathwalela umlotha wazo eBhetheli.
5 Ya kawar da firistocin gumakan da sarakunan Yahuda suka naɗa don su ƙona turare a masujadan kan tuddai na garuruwan Yahuda, da kuma waɗanda suke kewaye da Urushalima, masu ƙona turare wa Ba’al, rana da wata, ga rukunin taurari, da kuma ga dukan rundunan taurari.
Wasesusa abapristi bezithombe amakhosi akoJuda ayebabekile ukuthi batshise impepha endaweni eziphakemeyo, emizini yakoJuda, lendawo ezizingelezele iJerusalema, lalabo ababetshisa impepha kuBhali, elangeni, lenyangeni, lezinkanyezini, lebuthweni lonke lamazulu.
6 Ya ɗauke ginshiƙin Ashera daga haikalin Ubangiji zuwa Kwarin Kidron can bayan Urushalima, ya ƙone shi a can. Ya niƙa shi sai da ya zama toka, sai ya watsar da ƙurar a filin kabarin talakawa.
Wakhupha isixuku endlini yeNkosi, ngaphandle kweJerusalema, wasisa esifuleni iKidroni, wasitshisa esifuleni iKidroni, wasichola saba luthuli, waphosela uthuli lwaso emangcwabeni abantwana babantu.
7 Ya kuma rurrushe mazaunan karuwai mazan haikali waɗanda suke a haikalin Ubangiji, da kuma inda mata suke yi wa Ashera saƙa.
Wadiliza izindlu zezinkotshana ezazingasendlini yeNkosi lapho abesifazana ababeselukela khona amaveyili esixuku.
8 Yosiya ya kawo dukan firistoci daga garuruwan Yahuda, ya kuma lalatar da masujadan kan tuddai daga Geba har zuwa Beyersheba, inda firistoci suke ƙona turare. Ya rurrushe matsafai a ƙofofi shigan gari na mashigi zuwa Ƙofar Yoshuwa, gwamnan birnin, wanda yake a hagu da ƙofar birnin.
Wakhupha bonke abapristi emizini yakoJuda, wangcolisa indawo eziphakemeyo lapho abapristi ababetshisela khona impepha, kusukela eGeba kusiya eBherishebha. Wadiliza indawo eziphakemeyo zamasango ezisekungeneni kwesango likaJoshuwa umbusi womuzi, ezazingakwesokhohlo somuntu esangweni lomuzi.
9 Ko da yake firistocin masujadan kan tuddai ba su yi hidima a bagaden Ubangiji a Urushalima ba, sun ci burodi marar yisti tare da sauran firistoci.
Loba kunjalo abapristi bendawo eziphakemeyo kabenyukelanga elathini leNkosi eJerusalema, kodwa badla izinkwa ezingelamvubelo phakathi kwabafowabo.
10 Ya lalatar da Tofet, wanda yake a Kwarin Ben Hinnom, don kada kowa yă iya yin amfani da wurin don yă miƙa hadayar ɗansa, ko’yarsa a wuta ga Molek.
Wasengcolisa iTofethi elisesihotsheni sendodana kaHinomu ukuze kungabi khona umuntu odabulisa indodana yakhe kumbe indodakazi yakhe emlilweni kuMoleki.
11 Ya kawar da dawakan nan da sarakunan Yahuda suka keɓe wa gumakan nan na rana daga mashigin haikalin Ubangiji. Waɗannan dawakan suna kusa da ɗakin Natan Melek, ɗaya daga cikin dattawan sarki. Yosiya ya kuma ƙone kekunan yaƙi a yin sujada ga gumakan nan rana.
Wasesusa amabhiza amakhosi akoJuda ayewanikele elangeni ekungeneni kwendlu yeNkosi, ngasekamelweni likaNathani-Meleki umthenwa elalisekhulusini, wazitshisa inqola zelanga ngomlilo.
12 Ya rushe bagadan da sarakunan Yahuda suka kafa a kan ɗakin sama kusa da ɗakin sama na Ahaz, da kuma bagadai biyu da Manasse ya gina a filaye biyu na haikalin Ubangiji. Ya kawar da su daga can, ya farfashe su, ya zubar da tarkacen a Kwarin Kidron.
Lamalathi ayesephahleni lwendlu kaAhazi engaphezulu awenzayo amakhosi akoJuda, lamalathi uManase ayewenzile emagumeni womabili endlu yeNkosi, inkosi yawadiliza yawachoboza iwasusa lapho, yaluphosela uthuli lwawo esifuleni iKidroni.
13 Sarkin kuma ya lalatar da masujadan kan tuddan da suke gabas da Urushalima, kudu da Tudun Hallaka, waɗanda Solomon sarkin Isra’ila ya gina don Ashtarot, ƙazantacciyar alliyar Sidoniyawa, da Kemosh ƙazantaccen allah na Mowab, da kuma Molek allahn banƙyama na mutanen Ammon.
Lendawo eziphakemeyo, ezaziphambi kweJerusalema, ezazingakwesokunene sentaba yokubola, uSolomoni inkosi yakoIsrayeli eyayizakhele uAshitarothi isinengiso samaSidoni, loKemoshi isinengiso samaMowabi, loMilkomu isinengiso sabantwana bakoAmoni, inkosi yazingcolisa.
14 Yosiya ya farfashe keɓaɓɓun duwatsu, ya rurrushe ginshiƙan Asheransu, ya baza ƙasusuwan mutane a can.
Wasephahlaza insika eziyizithombe, wagamula izixuku, wagcwalisa izindawo zazo ngamathambo abantu.
15 Har ma da bagaden Betel, masujadan kan tudun da Yerobowam ɗan Nebat ya yi, wanda ya sa Isra’ila suka yi zunubi. Wannan bagade da masujadan kan tudun ma ya kawar, ya ƙone masujadan kan tudun, ya niƙa su, ya kuma ƙone ginshiƙin Ashera.
Lelathi lalo elaliseBhetheli, lendawo ephakemeyo, ayenzayo uJerobhowamu indodana kaNebati owenza uIsrayeli ukuthi one, kokubili lelolathi lendawo ephakemeyo wakudiliza, watshisa indawo ephakemeyo, wayichoboza yaba luthuli, watshisa isixuku.
16 Da Yosiya ya dubi kewaye da shi, ya ga kaburburan da suke can a gefen tudu, sai ya sa aka kwaso ƙasusuwan da suke cikinsu aka ƙone a kan bagade don yă lalatar da shi bisa ga maganar Ubangiji ta bakin mutumin Allah, wanda ya yi annabcin waɗannan abubuwa.
Lapho uJosiya ephenduka wabona amangcwaba ayelapho entabeni, wathuma wasekhupha amathambo emangcwabeni, wawatshisela phezu kwelathi, walingcolisa, njengelizwi leNkosi umuntu kaNkulunkulu ayelimemezele, owamemezela lamazwi.
17 Sarkin ya yi tambaya, ya ce, “Wane kabari ke nan nake gani?” Mutanen birnin suka ce, “Ai, kabarin annabin Allah ne wanda ya fito daga Yahuda, shi ne ya yi annabcin waɗannan abubuwan da ka aikata gāba da bagaden Betel.”
Wasesithi: Yisikhumbuzo sani lesiyana engisibonayo? Abantu bomuzi basebesithi kuye: Lingcwaba lomuntu kaNkulunkulu owavela koJuda wamemezela lezizinto ozenzileyo umelene lelathi leBhetheli.
18 Sai ya ce, “Ku rabu da shi, kada wani yă dami ƙasusuwansa.” Saboda haka suka bar kasusuwansa, da na annabin da ya fito Samariya.
Wasesithi: Myekeleni, kakungabi lamuntu othinta amathambo akhe. Basebewayekela amathambo akhe kanye lamathambo omprofethi owavela eSamariya.
19 Kamar yadda ya yi a Betel, Yosiya ya kawar da dukan ɗakunan gumaka a kan tuddan da sarakunan Isra’ila suka gina a garuruwan Samariya, waɗanda suka tozarta Ubangiji.
Njalo lazo zonke izindlu zezindawo eziphakemeyo ezisemizini yeSamariya, amakhosi akoIsrayeli ayezenzile ukuthukuthelisa, uJosiya wazisusa, wenza kizo njengayo yonke imisebenzi ayeyenze eBhetheli.
20 Yosiya ya yayyanka dukan firistoci na waɗannan masujadan kan tuddai, ya kuma ƙone ƙasusuwan mutane a kansu. Sa’an nan ya koma Urushalima.
Wasebulala bonke abapristi bezindawo eziphakemeyo, ababekhonapho, phezu kwamalathi, watshisa amathambo abantu phezu kwawo. Wasebuyela eJerusalema.
21 Sarkin ya ba da umarnin nan ga dukan mutane, cewa, “Ku yi Bikin Ƙetarewa ga Ubangiji Allahnku, yadda aka rubuta a Littafin Alkawari.”
Inkosi yasilaya bonke abantu isithi: Gcinani iphasika eNkosini uNkulunkulu wenu, njengalokhu kubhaliwe kulolugwalo lwesivumelwano.
22 Ba a taɓa yin irin Bikin Ƙetarewa haka ba, tun zamanin da masu shari’a suke aiki a matsayin sarakuna, ko a kwanakin sarakunan Isra’ila, ko na Yahuda.
Ngoba kwakungagcinwanga elinjengaleli iphasika kusukela ensukwini zabehluleli abehlulela uIsrayeli, kumbe kuzo zonke izinsuku zamakhosi akoIsrayeli, kumbe zamakhosi akoJuda.
23 Amma a shekara ta goma sha takwas ta mulkin sarki Yosiya, aka yi Bikin Ƙetarewan nan ga Ubangiji a Urushalima.
Kodwa ngomnyaka wetshumi lesificaminwembili wenkosi uJosiya lagcinwa leliphasika eNkosini eJerusalema.
24 Ban da haka, Yosiya ya kawar da masu duba, da masu maita, da allolin gidaje, da gumaka, da duk wani abin banƙyaman da ya gani a Yahuda da Urushalima. Ya yi wannan domin yă cika wa’adodin shari’a yadda suke a littafin da Hilkiya firist ya samu a haikalin Ubangiji.
Ngaphezu kwalokho-ke abalamadlozi, labalumbayo, lamatherafi, lezithombe, lawo wonke amanyala abonakala elizweni lakoJuda leJerusalema, uJosiya wakususa, ukuze aqinise amazwi omlayo ayebhalwe ogwalweni uHilikhiya umpristi alufica endlini yeNkosi.
25 Babu wani sarki kafin Yosiya, ko kuma a bayansa, wanda ya juya ga Ubangiji da dukan zuciyarsa, da dukan ransa, da dukan ƙarfinsa bisa ga shari’ar Musa, kamar yadda ya yi.
Langaphambi kwakhe kakubanga khona inkosi eyafanana laye eyaphendukela eNkosini ngenhliziyo yayo yonke langomphefumulo wayo wonke langamandla ayo wonke, njengokomlayo wonke kaMozisi. Futhi emva kwakhe kakuvelanga eyafanana laye.
26 Duk da haka, Ubangiji bai huce daga zafin fushinsa wanda ya ƙuna game da Yahuda saboda abin da Manasse ya aikata don yă tozarta shi ba.
Kanti iNkosi kayiphendukanga ekuvutheni kolaka lwayo olukhulu, olaka lwayo eyavuthela ngalo uJuda, ngenxa yazo zonke intukutheliso uManase ayithukuthelisa ngazo.
27 Saboda haka Ubangiji ya ce, “Zan shafe Yahuda ma kamar yadda na shafe Isra’ila, daga gabana, zan ƙi Urushalima birnin da na zaɓa, da wannan haikali wanda na ce, ‘A can Sunana zai kasance.’”
INkosi yasisithi: Ngizamsusa loJuda phambi kwami, njengoba ngasusa uIsrayeli, ngiwulahle lumuzi weJerusalema engawukhethayo, lendlu engathi ngayo: Ibizo lami lizakuba lapho.
28 Game da sauran ayyukan mulkin Yosiya, da duk abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
Ezinye-ke zezindaba zikaJosiya, lakho konke akwenzayo, kakubhalwanga yini egwalweni lwemilando yamakhosi akoJuda?
29 Yayinda Yosiya yake sarki, Fir’auna Neko, sarkin Masar ya haura zuwa Kogin Yuferites don yă taimaki sarkin Assuriya da yaƙi. Sarki Yosiya kuwa ya yi ƙoƙari ya hana shi wucewa, sa’ad da Fir’auna Neko ya gan shi, sai ya kashe shi a filin yaƙi a Megiddo.
Ensukwini zakhe uFaro Neko inkosi yeGibhithe wenyuka wamelana lenkosi yeAsiriya emfuleni iYufrathi. Inkosi uJosiya yasisiyahlangabezana laye; wayibulalela eMegido eseyibonile.
30 Bayin Yosiya suka ɗauko gawarsa daga Megiddo suka kai Urushalima, suka binne shi a kabarinsa. Sai mutanen ƙasar suka ɗauki Yehoyahaz ɗan Yosiya suka naɗa shi sarki a madadin mahaifinsa.
Inceku zakhe zasezimthwala efile ngenqola, zisuka eMegido, zamusa eJerusalema, zamngcwaba engcwabeni lakhe. Abantu belizwe basebethatha uJehowahazi indodana kaJosiya, bamgcoba, bambeka waba yinkosi esikhundleni sikayise.
31 Yehoyahaz yana da shekara ashirin da uku sa’ad da ya zama sarki. Ya yi mulki na wata uku a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Hamutal’yar Irmiya; mutuniyar Libna.
UJehowahazi wayeleminyaka engamatshumi amabili lantathu lapho esiba yinkosi; wabusa inyanga ezintathu eJerusalema. Lebizo likanina lalinguHamuthali indodakazi kaJeremiya weLibhina.
32 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, yadda kakanninsa suka yi.
Wasesenza okubi emehlweni eNkosi njengakho konke oyise abakwenzayo.
33 Fir’auna Neko ya sa shi a sarƙa a Ribla a ƙasar Hamat don kada yă yi mulki a Urushalima, sa’an nan ya sa wa Yahuda harajin talenti ɗari na azurfa, da talenti ɗaya na zinariya.
UFaro Neko wasembopha eRibila elizweni leHamathi ukuthi angabusi eJerusalema, wahlawulisa ilizwe amathalenta esiliva alikhulu lethalenta legolide.
34 Fir’auna Neko ya naɗa Eliyakim ɗan Yosiya sarki a maimakon mahaifinsa, ya kuma canja masa suna zuwa Yehohiyakim. Ya ɗauki Yehoyahaz ya kai Masar, a can ya mutu.
UFaro Neko wasebeka uEliyakhimi indodana kaJosiya ukuthi abe yinkosi esikhundleni sikaJosiya uyise, waphendula ibizo lakhe wathi nguJehoyakhimi. Wasethatha uJehowahazi; wasesiza eGibhithe, wafela khona.
35 Yehohiyakim ya riƙa biyan Fir’auna Neko azurfa da zinariyar da ya umarta. Don yă yi haka sai ya riƙa karɓar azurfa da zinariya daga mutanen ƙasar, kowa bisa ga ƙarfinsa.
UJehoyakhimi wasemnika uFaro isiliva legolide, kodwa wathelisa ilizwe ukuze anike leyomali njengokomlayo kaFaro. Wakhuphisa abantu belizwe isiliva legolide, ngulowo lalowo ngokomthelo wakhe, yokunika uFaro Neko.
36 Yehohiyakim yana da shekara ashirin da biyar sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekara goma sha ɗaya a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Zebuda’yar Fedahiya, mutuniyar Ruma.
UJehoyakhimi wayeleminyaka engamatshumi amabili lanhlanu lapho esiba yinkosi; wabusa iminyaka elitshumi lanye eJerusalema. Lebizo likanina lalinguZebida indodakazi kaPhedaya weRuma.
37 Ya kuma aika mugunta a gaban Ubangiji yadda kakanninsa suka yi.
Wasesenza okubi emehlweni eNkosi njengakho konke oyise abakwenzayo.

< 2 Sarakuna 23 >