< 2 Sarakuna 23 >

1 Sai sarki ya kira dukan dattawan Yahuda da Urushalima.
Nampañitrike i mpanjakay, le natontoñ’ ama’e ze hene androanavi’ Iehoda naho Ierosalaimeo.
2 Sai ya haura zuwa cikin haikalin Ubangiji tare da mutanen Yahuda, da na Urushalima, da firistoci, da annabawa, dukan mutane, manya da ƙanana. Ya karanta musu duk kalmomin Littafin Alkawari, wanda aka samu a haikalin Ubangiji.
Le nionjomb’ añ’ anjomba’ Iehovà mb’eo i mpanjakay rekets’ ondati’ Iehoda iabio naho ze fonga mpimone’ Ierosalaime naho mpisoroñe naho mpitoky, naho ze kila ondaty, ty kede naho ty bey, vaho hene vinaki’e an-dravembia’ iareo ze tsara amy bokem-pañina nitendrek’ añ’ anjomba’ Iehovày.
3 Sarki ya tsaya dab da ginshiƙi ya kuma sabunta alkawarin a gaban Ubangiji, ya ce zai bi Ubangiji, yă kiyaye dokokinsa, da ƙa’idodinsa, da farillansa, da dukan zuciyarsa da dukan ransa, ta haka ya tabbatar da kalmomin alkawarin da yake a rubuce a cikin littafin nan. Sa’an nan dukan mutane ma suka yi alkawari yin haka.
Nijohañe ami’ty fahañe eo i mpanjakay naho nifañina añatrefa’ Iehovà, t’ie hañavelo am-pañorihañe Iehovà naho hiambeñe o lili’eo naho o taro’eo vaho o fañè’eo añ’ ampon’ arofo naho an-kaliforam-pañova, hahatafetera’e o tsara’ i fañina sinokitse amy bokeio; le niantofa’ o fonga ondatio i fañinay.
4 Sai Yosiya ya umarci Hilkiya babban firist, tare da firistocin da suke taimakonsa, da masu tsaron ƙofa su kawar da dukan abubuwan da aka yi domin Ba’al, da domin Ashera, da kuma domin dukan rundunar taurari, daga haikalin Ubangiji. Ya ƙone su a bayan Urushalima a filayen Kwarin Kidron, ya kwashe tokan zuwa Betel.
Linili’ i mpanjakay amy zao t’i Kil­kià mpisoroñe naho o mpisoroñe am-pi­rim­­boñañe faha-roe naho o mpitan-dalam­beio, ty hañakara’ iareo an-kivoho’ Iehovà ze fanake nanoeñe amy Baale naho an-tsamposampo naho amy valobohòn-dikerañey; le niforototoe’e alafe’ Ierosalaime an-kivo’ i Kidrone ao vaho nendese’e mb’e Betele añe ty laveno’e.
5 Ya kawar da firistocin gumakan da sarakunan Yahuda suka naɗa don su ƙona turare a masujadan kan tuddai na garuruwan Yahuda, da kuma waɗanda suke kewaye da Urushalima, masu ƙona turare wa Ba’al, rana da wata, ga rukunin taurari, da kuma ga dukan rundunan taurari.
Nafotsa’e iaby o mpisorom-pahasive noriza’ o mpanjaka’ Iehodao hañenga amy ze toets’ abo amo rova’ Iehodào, naho amo toetse mañohoke Ierosalaimeo; le o nañenga amy Baale, amy àndroy, amy volañey, amo vasiañe mifamorohotseo, vaho amy valobohòn-dikerañeio.
6 Ya ɗauke ginshiƙin Ashera daga haikalin Ubangiji zuwa Kwarin Kidron can bayan Urushalima, ya ƙone shi a can. Ya niƙa shi sai da ya zama toka, sai ya watsar da ƙurar a filin kabarin talakawa.
Naaka’e añ’ anjomba’ Iehovà mb’ alafe’ Ierosalaime mb’eo, mb’an toraha’ i Kidroney o Aserào naho finorototo’e an-toraha’ i Kidrone ey naho dinemodemo’e ho bo vaho nafitse’e amo kibori’ o ana’ ondatio i debokey.
7 Ya kuma rurrushe mazaunan karuwai mazan haikali waɗanda suke a haikalin Ubangiji, da kuma inda mata suke yi wa Ashera saƙa.
Narotsa’e o kibohom-borololo añ’ila’ i anjomba’ Iehovày amy fanenoñan-drakemba o tèmen’ Aseràoy.
8 Yosiya ya kawo dukan firistoci daga garuruwan Yahuda, ya kuma lalatar da masujadan kan tuddai daga Geba har zuwa Beyersheba, inda firistoci suke ƙona turare. Ya rurrushe matsafai a ƙofofi shigan gari na mashigi zuwa Ƙofar Yoshuwa, gwamnan birnin, wanda yake a hagu da ƙofar birnin.
Fonga nakare’e amo rova’ Iehodao o mpisoroñeo naho nileore’e o toets’ abo nañemboha’ o mpisoroñeo mifototse e Geba pake Beeresebà vaho narotsa’e o toets’ abo am-pimoahañe i lalambei’ Iehosoà bein-tanañeio, am-pitàn-kavia an-dalambei’ i rovaio.
9 Ko da yake firistocin masujadan kan tuddai ba su yi hidima a bagaden Ubangiji a Urushalima ba, sun ci burodi marar yisti tare da sauran firistoci.
ie amy zao tsy nionjom-b’ amy kitreli’ Iehovà e Ierosalaimey añe o mpisoron-toets’aboo, f’ie nitrao-pikama mofo tsi-aman-dali­vae amo rahalahi’eo.
10 Ya lalatar da Tofet, wanda yake a Kwarin Ben Hinnom, don kada kowa yă iya yin amfani da wurin don yă miƙa hadayar ɗansa, ko’yarsa a wuta ga Molek.
Nileore’e ty Topete, am-bavatane’ i ana’ i Hino­mey, tsy hampirangà’ ondaty añ’afo’ i Moleke ao ty ana-dahi’e ndra ty anak’ ampela’e.
11 Ya kawar da dawakan nan da sarakunan Yahuda suka keɓe wa gumakan nan na rana daga mashigin haikalin Ubangiji. Waɗannan dawakan suna kusa da ɗakin Natan Melek, ɗaya daga cikin dattawan sarki. Yosiya ya kuma ƙone kekunan yaƙi a yin sujada ga gumakan nan rana.
Nafaha’e o soavala noriza’ o mpanjaka’ Iehodao amy àndroy, am-pimoahañe añ’ anjomba’ Iehovà, marine’ ty efe’ i Matane-meleke, vosie, am-pariparitse ey, vaho finorototo’e añ’ afo o sareten’ androo.
12 Ya rushe bagadan da sarakunan Yahuda suka kafa a kan ɗakin sama kusa da ɗakin sama na Ahaz, da kuma bagadai biyu da Manasse ya gina a filaye biyu na haikalin Ubangiji. Ya kawar da su daga can, ya farfashe su, ya zubar da tarkacen a Kwarin Kidron.
Le naro­tsa’ i mpanjakay i kitrely an-tafo’ i efetse ambone’ i Ahkaze namboare’ o mpanjaka’ Ieho­daoy naho o kitreli’ i Menasè niranjie’e an-kiririsa roe’ i anjomba’ Iehovà eio le dinemodemo’e vaho nahifi’e an-tora­han-Kidrone ao ty debo’e.
13 Sarkin kuma ya lalatar da masujadan kan tuddan da suke gabas da Urushalima, kudu da Tudun Hallaka, waɗanda Solomon sarkin Isra’ila ya gina don Ashtarot, ƙazantacciyar alliyar Sidoniyawa, da Kemosh ƙazantaccen allah na Mowab, da kuma Molek allahn banƙyama na mutanen Ammon.
Le nileore’ i mpanjakay o tamboho aolo’ Ierosalaime am-pitàn-kavanan-kaboan-kaleorañeo, i namboare’ i Selomò mpanjaka’ Israele amy Astorete, ty haloloa’ o nte-Tsidoneo, naho amy Kemose, ty haloloa’ o nte-Moabeo vaho amy Milkome, ty haloloa’ o ana’ i Amoneo.
14 Yosiya ya farfashe keɓaɓɓun duwatsu, ya rurrushe ginshiƙan Asheransu, ya baza ƙasusuwan mutane a can.
Dinoro-demo’e o saren-drahao naho finira’e o hazomangao, vaho natsafe’e taola’ ondaty o toe’eo.
15 Har ma da bagaden Betel, masujadan kan tudun da Yerobowam ɗan Nebat ya yi, wanda ya sa Isra’ila suka yi zunubi. Wannan bagade da masujadan kan tudun ma ya kawar, ya ƙone masujadan kan tudun, ya niƙa su, ya kuma ƙone ginshiƙin Ashera.
Le i kitrely e Beteley, naho i toets’ abo’ Iarovame namboare’ i ana’ i Nebate nampanan-kakeo Israeley; fonga narotsa’e i kitreliy naho i toets’ aboy, le finorototo’e i toets’ aboy, naho dinemodemo’e ho deboke vaho hinotomomo’e i Aserày.
16 Da Yosiya ya dubi kewaye da shi, ya ga kaburburan da suke can a gefen tudu, sai ya sa aka kwaso ƙasusuwan da suke cikinsu aka ƙone a kan bagade don yă lalatar da shi bisa ga maganar Ubangiji ta bakin mutumin Allah, wanda ya yi annabcin waɗannan abubuwa.
Ie nitolike t’Iosià, le niisa’e o kibory an-kaboañeio naho nampañitrife’e naho nakare’e amy kibory rey o taolañeo vaho finorototo’e ambone’ i kitreliy handeora’e aze, hambañe amy tsara’ Iehovà tsinei’ indatin’ Añahare nikoike irezaiy.
17 Sarkin ya yi tambaya, ya ce, “Wane kabari ke nan nake gani?” Mutanen birnin suka ce, “Ai, kabarin annabin Allah ne wanda ya fito daga Yahuda, shi ne ya yi annabcin waɗannan abubuwan da ka aikata gāba da bagaden Betel.”
Aa hoe re, Lona’ ia o treakoo? Le hoe ondati’ i rovaio ama’e: Kibori’ indatin’ Añahare niheo mb’etoa boak’ Iehoda nitsey o raha anoe’o amy kitreli’ i Beteleioy.
18 Sai ya ce, “Ku rabu da shi, kada wani yă dami ƙasusuwansa.” Saboda haka suka bar kasusuwansa, da na annabin da ya fito Samariya.
Le hoe re: Adono; ko apo’ areo ho tsiborè’ ondaty o taola’eo. Aa le nado’ iareo o taola’eo, rekets’ o taola’ i mpitoky boake Someroneio.
19 Kamar yadda ya yi a Betel, Yosiya ya kawar da dukan ɗakunan gumaka a kan tuddan da sarakunan Isra’ila suka gina a garuruwan Samariya, waɗanda suka tozarta Ubangiji.
Nafaha’ Iosià iaby o anjomban-toets’ abo an-drova’ i Somerone namboare’ o mpanjaka’ Israeleo nampiviñetse Iehovào, le hene nanoe’e am’ iereo i nanoe’e e Beteley.
20 Yosiya ya yayyanka dukan firistoci na waɗannan masujadan kan tuddai, ya kuma ƙone ƙasusuwan mutane a kansu. Sa’an nan ya koma Urushalima.
Fonga zinevo’e ambone kitrely eo o mpisoron-toets’ abo taoo naho noroa’e ambone’ iereo ty taola’ ondaty; vaho nimpoly mb’e Ierosala­ime mb’eo.
21 Sarkin ya ba da umarnin nan ga dukan mutane, cewa, “Ku yi Bikin Ƙetarewa ga Ubangiji Allahnku, yadda aka rubuta a Littafin Alkawari.”
Linili’ i mpanjakay o hene ondatio, ami’ty hoe: Ambeno i fihelañ’ ambone’ Iehovà Andria­nañahare’oy, i sinokitse amy bokem-pañinaiy.
22 Ba a taɓa yin irin Bikin Ƙetarewa haka ba, tun zamanin da masu shari’a suke aiki a matsayin sarakuna, ko a kwanakin sarakunan Isra’ila, ko na Yahuda.
Aa le mboe lia’e tsy nanoeñe ty fihelañ’ ambone manahake izay boak’ añ’andro’ o mpizaka nizaka Israeleo ndra amo androm-panjaka’ Israeleo naho o mpanjaka’ Iehodào;
23 Amma a shekara ta goma sha takwas ta mulkin sarki Yosiya, aka yi Bikin Ƙetarewan nan ga Ubangiji a Urushalima.
amy taom-paha-folo-valo’ ambi’ Iosià mpanjakay ty nañambenañe i fihelañ’ ambone am’ Iehovày e Ierosalaime ao.
24 Ban da haka, Yosiya ya kawar da masu duba, da masu maita, da allolin gidaje, da gumaka, da duk wani abin banƙyaman da ya gani a Yahuda da Urushalima. Ya yi wannan domin yă cika wa’adodin shari’a yadda suke a littafin da Hilkiya firist ya samu a haikalin Ubangiji.
Fonga nafaha’ Iosià ze mpandrombo anga­tse naho jiny naho terafime naho hazomanga vaho ze hene haloloañe nizoeñe an-tane’ Iehoda naho e Ierosa­laime ao hamente ty enta’ i Hake sinokitse amy boke nioni’ i Kilkià mpisoroñey añ’anjomba’ Iehovà aoiy.
25 Babu wani sarki kafin Yosiya, ko kuma a bayansa, wanda ya juya ga Ubangiji da dukan zuciyarsa, da dukan ransa, da dukan ƙarfinsa bisa ga shari’ar Musa, kamar yadda ya yi.
Le tsy eo ty nañirinkiriñe aze amy ze mpanjaka niaolo aze, ie nitolik’ am’ Iehovà an-kaampon’ arofo naho an-kalifo­ram-pa­ñova vaho an-kene hao­zara’e, ty amy Hà’ i Mosey; ie tsy amam-panonjohy nitroatse nanahak’ aze.
26 Duk da haka, Ubangiji bai huce daga zafin fushinsa wanda ya ƙuna game da Yahuda saboda abin da Manasse ya aikata don yă tozarta shi ba.
Fe tsy nitolik’ amy fifombo’e niforoforoy t’Iehovà, amy haviñera’e nisolebotse am’ Iehodà, ty amo fonga sigý nisigihe’ i Menasè Azeo.
27 Saboda haka Ubangiji ya ce, “Zan shafe Yahuda ma kamar yadda na shafe Isra’ila, daga gabana, zan ƙi Urushalima birnin da na zaɓa, da wannan haikali wanda na ce, ‘A can Sunana zai kasance.’”
Le hoe t’Iehovà, hafahako am-pahatreavako t’Iehoda, manahake ty nañafahako Israele vaho hahifiko añe ty rova jinoboko toy naho i anjom­ba nataoko ty hoe: Ho ao i añarakoiy.
28 Game da sauran ayyukan mulkin Yosiya, da duk abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
Aa naho o fitoloña’ Iosià ila’eo, o raha nanoe’e iabio, tsy fa sinokitse amy bokem-pamoliliañe o mpanjaka’ Iehodaoy hao?
29 Yayinda Yosiya yake sarki, Fir’auna Neko, sarkin Masar ya haura zuwa Kogin Yuferites don yă taimaki sarkin Assuriya da yaƙi. Sarki Yosiya kuwa ya yi ƙoƙari ya hana shi wucewa, sa’ad da Fir’auna Neko ya gan shi, sai ya kashe shi a filin yaƙi a Megiddo.
Ie tañ’ andro’e le nionjo haname ty mpanjaka’ i Asore t’i Parò-Nekò mpanjaka’ i Mitsraime mb’an-tsaka Perate añe; nomb’ ama’e mb’eo t’Ioase, mpanjaka, fe vata’e niisa’e le zinevo’e e Megidò añe.
30 Bayin Yosiya suka ɗauko gawarsa daga Megiddo suka kai Urushalima, suka binne shi a kabarinsa. Sai mutanen ƙasar suka ɗauki Yehoyahaz ɗan Yosiya suka naɗa shi sarki a madadin mahaifinsa.
Nitakone’ o mpi­toro’eo an-tsarete i fañova’ey, nendese’ iereo mb’e Ierosalaime mb’eo vaho nalentek’ an-kibori’e ao. Rinambe ondati’ i taneio t’Ie­hoakaze, ie ty noriza’ iareo ho mpanjaka handimbe an-drae’e.
31 Yehoyahaz yana da shekara ashirin da uku sa’ad da ya zama sarki. Ya yi mulki na wata uku a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Hamutal’yar Irmiya; mutuniyar Libna.
Roapolo-taoñe telo’ amby t’Ie­ho­­akaze te niorotse nifehe, le nifeleke telo volañe e Ierosalaime ao; i Kamotale, ana’ Irm-meà nte-Libnà, ty tahi­nan-drene’e.
32 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, yadda kakanninsa suka yi.
Nanao haratiañe am-pivazohoa’ Iehovà re manahake o fonga satan-droae’eo.
33 Fir’auna Neko ya sa shi a sarƙa a Ribla a ƙasar Hamat don kada yă yi mulki a Urushalima, sa’an nan ya sa wa Yahuda harajin talenti ɗari na azurfa, da talenti ɗaya na zinariya.
Le vinaho’ i Parò-Neko e Ribà an-tane Kamate añe re, tsy hameleha’e t’Ierosalaime; le sinaze’e ta­lenta zato volafoty naho talenta volamena raike i taney.
34 Fir’auna Neko ya naɗa Eliyakim ɗan Yosiya sarki a maimakon mahaifinsa, ya kuma canja masa suna zuwa Yehohiyakim. Ya ɗauki Yehoyahaz ya kai Masar, a can ya mutu.
Le nanoe’ i Parò-Neko mpanjaka t’i Eliakime ana’ Iosia han­dimbe an-drae’e Iosia naho novae’e ho Iehoiakime ty tahina’e naho nendese’e mb’e Mitsraime mb’eo t’Iehoakaze, vaho nihomake añe.
35 Yehohiyakim ya riƙa biyan Fir’auna Neko azurfa da zinariyar da ya umarta. Don yă yi haka sai ya riƙa karɓar azurfa da zinariya daga mutanen ƙasar, kowa bisa ga ƙarfinsa.
Natolo’ Iehoiakime amy Parò i volafoty naho volamenay, le nangalà’e haba i taney ty amy lili’ i Paròy; rinambe’e am’ ondati’ i taneio i volafoty naho volamenay, sambe ty amy vili-loha’ey, hanolotse aze amy Parò-Neko.
36 Yehohiyakim yana da shekara ashirin da biyar sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekara goma sha ɗaya a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Zebuda’yar Fedahiya, mutuniyar Ruma.
Roapolo-taoñe lime amby t’Iehoiakime te niorotse nifehe; vaho nifeleke folo-taoñe raik’ amby e Ierosalaime ao; i Zebidà, ana’ i Pedaià nte-Romà, ty tahinan-drene’e.
37 Ya kuma aika mugunta a gaban Ubangiji yadda kakanninsa suka yi.
Le nanao haratiañe am-pivazohoa’ Iehovà re manahake o satan-droae’eo.

< 2 Sarakuna 23 >