< 2 Sarakuna 23 >

1 Sai sarki ya kira dukan dattawan Yahuda da Urushalima.
Et ils rapportèrent au roi ce qu’elle avait dit. Et le roi envoya, et tous les anciens de Juda et de Jérusalem s’assemblèrent près de lui.
2 Sai ya haura zuwa cikin haikalin Ubangiji tare da mutanen Yahuda, da na Urushalima, da firistoci, da annabawa, dukan mutane, manya da ƙanana. Ya karanta musu duk kalmomin Littafin Alkawari, wanda aka samu a haikalin Ubangiji.
Et le roi monta dans le temple du Seigneur, ainsi que tous les hommes de Juda et tous ceux qui habitaient dans Jérusalem avec lui, les prêtres, les prophètes et tout le peuple, depuis le petit jusqu’au grand, et il lut, tous l’écoutant, toutes les paroles du livre de l’alliance, qui avait été trouvé dans la maison du Seigneur.
3 Sarki ya tsaya dab da ginshiƙi ya kuma sabunta alkawarin a gaban Ubangiji, ya ce zai bi Ubangiji, yă kiyaye dokokinsa, da ƙa’idodinsa, da farillansa, da dukan zuciyarsa da dukan ransa, ta haka ya tabbatar da kalmomin alkawarin da yake a rubuce a cikin littafin nan. Sa’an nan dukan mutane ma suka yi alkawari yin haka.
Et le roi se tint debout dans la tribune, et fit l’alliance devant le Seigneur, afin qu’ils marchassent à la suite du Seigneur, qu’ils observassent ses préceptes, ses lois et ses cérémonies en tout leur cœur et en toute leur âme, et qu’ils rétablissent toutes les paroles de l’alliance qui étaient écrites dans ce livre; et le peuple acquiesça à l’alliance.
4 Sai Yosiya ya umarci Hilkiya babban firist, tare da firistocin da suke taimakonsa, da masu tsaron ƙofa su kawar da dukan abubuwan da aka yi domin Ba’al, da domin Ashera, da kuma domin dukan rundunar taurari, daga haikalin Ubangiji. Ya ƙone su a bayan Urushalima a filayen Kwarin Kidron, ya kwashe tokan zuwa Betel.
Alors le roi ordonna à Helcias, le pontife, aux prêtres du second ordre, et aux portiers, de jeter hors du temple du Seigneur tous les vases qui avaient appartenu à Baal, au bois sacré et à toute l’armée du ciel, et il les brûla hors de Jérusalem, dans la vallée de Cédron, et il en emporta la poussière à Béthel.
5 Ya kawar da firistocin gumakan da sarakunan Yahuda suka naɗa don su ƙona turare a masujadan kan tuddai na garuruwan Yahuda, da kuma waɗanda suke kewaye da Urushalima, masu ƙona turare wa Ba’al, rana da wata, ga rukunin taurari, da kuma ga dukan rundunan taurari.
Et il détruisit les aruspices qu’avaient établis les rois de Juda pour sacrifier sur les hauts lieux, dans les villes de Juda et autour de Jérusalem, et ceux qui brûlaient de l’encens à Baal, au Soleil, à la Lune, aux douze signes et à toute la milice du ciel.
6 Ya ɗauke ginshiƙin Ashera daga haikalin Ubangiji zuwa Kwarin Kidron can bayan Urushalima, ya ƙone shi a can. Ya niƙa shi sai da ya zama toka, sai ya watsar da ƙurar a filin kabarin talakawa.
Et il fit emporter le bois sacré de la maison du Seigneur hors de Jérusalem, dans la vallée de Cédron, où il le brûla et le réduisit en poussière qu’il jeta sur les sépulcres du petit peuple.
7 Ya kuma rurrushe mazaunan karuwai mazan haikali waɗanda suke a haikalin Ubangiji, da kuma inda mata suke yi wa Ashera saƙa.
Il détruisit aussi les petites maisons des efféminés, lesquelles étaient dans la maison du Seigneur, et dans lesquelles les femmes tissaient comme des tentes pour le bois sacré.
8 Yosiya ya kawo dukan firistoci daga garuruwan Yahuda, ya kuma lalatar da masujadan kan tuddai daga Geba har zuwa Beyersheba, inda firistoci suke ƙona turare. Ya rurrushe matsafai a ƙofofi shigan gari na mashigi zuwa Ƙofar Yoshuwa, gwamnan birnin, wanda yake a hagu da ƙofar birnin.
Et il assembla tous les prêtres des villes de Juda, et il profana les hauts lieux où sacrifiaient les prêtres, depuis Gabaa jusqu’à Bersabée, et il détruisit les autels des portes, à l’entrée de la porte de Josué, prince de la ville, laquelle était à la gauche de la porte de la ville.
9 Ko da yake firistocin masujadan kan tuddai ba su yi hidima a bagaden Ubangiji a Urushalima ba, sun ci burodi marar yisti tare da sauran firistoci.
Cependant les prêtres des hauts lieux ne montaient point à l’autel du Seigneur dans Jérusalem; mais seulement ils mangeaient des azymes au milieu de leurs frères.
10 Ya lalatar da Tofet, wanda yake a Kwarin Ben Hinnom, don kada kowa yă iya yin amfani da wurin don yă miƙa hadayar ɗansa, ko’yarsa a wuta ga Molek.
Le roi profana aussi Topheth, qui est dans la vallée du fils d’Ennom, afin que personne ne consacrât son fils ou sa fille par le feu à Moloch.
11 Ya kawar da dawakan nan da sarakunan Yahuda suka keɓe wa gumakan nan na rana daga mashigin haikalin Ubangiji. Waɗannan dawakan suna kusa da ɗakin Natan Melek, ɗaya daga cikin dattawan sarki. Yosiya ya kuma ƙone kekunan yaƙi a yin sujada ga gumakan nan rana.
Il enleva aussi les chevaux qu’avaient donnés les rois de Juda au Soleil, à l’entrée du temple du Seigneur, près de la salle de Nathanmélech, l’eunuque, qui était à Pharurim; mais les chariots du Soleil, il les brûla au feu.
12 Ya rushe bagadan da sarakunan Yahuda suka kafa a kan ɗakin sama kusa da ɗakin sama na Ahaz, da kuma bagadai biyu da Manasse ya gina a filaye biyu na haikalin Ubangiji. Ya kawar da su daga can, ya farfashe su, ya zubar da tarkacen a Kwarin Kidron.
Les autels mêmes qui étaient sur le toit de la chambre d’Achaz, qu’avaient faits les rois de Juda, et les autels qu’avait faits Manassé dans les deux parvis du temple du Seigneur, le roi les détruisit, et il répandit les cendres dans le torrent de Cédron.
13 Sarkin kuma ya lalatar da masujadan kan tuddan da suke gabas da Urushalima, kudu da Tudun Hallaka, waɗanda Solomon sarkin Isra’ila ya gina don Ashtarot, ƙazantacciyar alliyar Sidoniyawa, da Kemosh ƙazantaccen allah na Mowab, da kuma Molek allahn banƙyama na mutanen Ammon.
Le roi profana aussi les hauts lieux qui étaient à Jérusalem, du côté droit de la montagne du Scandale, que Salomon, roi d’Israël, avait bâtis à Astaroth, idole des Sidoniens, à Chamos, le scandale de Moab, et à Melchom, l’abomination des enfants d’Ammon.
14 Yosiya ya farfashe keɓaɓɓun duwatsu, ya rurrushe ginshiƙan Asheransu, ya baza ƙasusuwan mutane a can.
Et il brisa les statues et coupa les bois sacrés, et il remplit ces lieux-là d’os de morts.
15 Har ma da bagaden Betel, masujadan kan tudun da Yerobowam ɗan Nebat ya yi, wanda ya sa Isra’ila suka yi zunubi. Wannan bagade da masujadan kan tudun ma ya kawar, ya ƙone masujadan kan tudun, ya niƙa su, ya kuma ƙone ginshiƙin Ashera.
En outre, quant à l’autel même qui était à Béthel, et le haut lieu qu’avait bâti Jéroboam, fils de Nabath, qui fit pécher Israël, il détruisit et cet autel et ce haut lieu; il les brûla et les réduisit en poussière, et il mit aussi le feu au bois sacré.
16 Da Yosiya ya dubi kewaye da shi, ya ga kaburburan da suke can a gefen tudu, sai ya sa aka kwaso ƙasusuwan da suke cikinsu aka ƙone a kan bagade don yă lalatar da shi bisa ga maganar Ubangiji ta bakin mutumin Allah, wanda ya yi annabcin waɗannan abubuwa.
Et, se tournant, Josias vit là les sépulcres qui étaient sur la montagne, et il envoya et il prit les os de ces sépulcres, et les brûla sur l’autel, et il le profana, selon la parole du Seigneur, qu’avait dite l’homme de Dieu qui avait prédit ces choses.
17 Sarkin ya yi tambaya, ya ce, “Wane kabari ke nan nake gani?” Mutanen birnin suka ce, “Ai, kabarin annabin Allah ne wanda ya fito daga Yahuda, shi ne ya yi annabcin waɗannan abubuwan da ka aikata gāba da bagaden Betel.”
Et il demanda: Quel est ce tombeau que je vois? Et les citoyens de cette ville lui dirent: C’est le sépulcre de l’homme de Dieu qui vint de Juda, et qui prédit ce que vous avez fait sur l’autel de Béthel.
18 Sai ya ce, “Ku rabu da shi, kada wani yă dami ƙasusuwansa.” Saboda haka suka bar kasusuwansa, da na annabin da ya fito Samariya.
Et il dit: Laissez-le, que personne ne remue ses os. Et ses os demeurèrent intacts, avec les os du prophète qui était venu de Samarie.
19 Kamar yadda ya yi a Betel, Yosiya ya kawar da dukan ɗakunan gumaka a kan tuddan da sarakunan Isra’ila suka gina a garuruwan Samariya, waɗanda suka tozarta Ubangiji.
De plus, tous les temples mêmes des hauts lieux qui étaient dans les villes de Samarie, qu’avaient faits les rois d’Israël pour irriter le Seigneur, Josias les détruisit; et il leur fit selon tout ce qu’il avait fait à Béthel.
20 Yosiya ya yayyanka dukan firistoci na waɗannan masujadan kan tuddai, ya kuma ƙone ƙasusuwan mutane a kansu. Sa’an nan ya koma Urushalima.
Et il tua tous les prêtres des hauts lieux qui étaient là préposés aux autels, et il brûla des ossements humains sur ces autels, et il retourna à Jérusalem.
21 Sarkin ya ba da umarnin nan ga dukan mutane, cewa, “Ku yi Bikin Ƙetarewa ga Ubangiji Allahnku, yadda aka rubuta a Littafin Alkawari.”
Et il ordonna à tout le peuple, disant: Faites une Pâque du Seigneur votre Dieu, selon ce qui est écrit dans le livre de cette alliance;
22 Ba a taɓa yin irin Bikin Ƙetarewa haka ba, tun zamanin da masu shari’a suke aiki a matsayin sarakuna, ko a kwanakin sarakunan Isra’ila, ko na Yahuda.
Car il n’a été fait aucune Pâque depuis les jours des juges qui jugèrent Israël, et pendant tous les jours des rois d’Israël et des rois de Juda,
23 Amma a shekara ta goma sha takwas ta mulkin sarki Yosiya, aka yi Bikin Ƙetarewan nan ga Ubangiji a Urushalima.
Comme à la dix-huitième année du roi Josias a été faite cette Pâque du Seigneur dans Jérusalem.
24 Ban da haka, Yosiya ya kawar da masu duba, da masu maita, da allolin gidaje, da gumaka, da duk wani abin banƙyaman da ya gani a Yahuda da Urushalima. Ya yi wannan domin yă cika wa’adodin shari’a yadda suke a littafin da Hilkiya firist ya samu a haikalin Ubangiji.
Mais aussi ceux qui avaient un esprit de python, les devins et les figures des idoles, les impuretés et les abominations qui avaient été dans la terre de Juda et de Jérusalem, Josias les fit disparaître pour accomplir les paroles de la loi qui sont écrites dans le livre que trouva Helcias, le prêtre, dans le temple du Seigneur.
25 Babu wani sarki kafin Yosiya, ko kuma a bayansa, wanda ya juya ga Ubangiji da dukan zuciyarsa, da dukan ransa, da dukan ƙarfinsa bisa ga shari’ar Musa, kamar yadda ya yi.
Il n’y a point eu avant Josias de roi semblable, qui soit retourné comme lui au Seigneur en tout son cœur, en toute son âme, et en toute sa force, selon toute la loi de Moïse, et après lui, il n’y en a pas eu de semblable à lui.
26 Duk da haka, Ubangiji bai huce daga zafin fushinsa wanda ya ƙuna game da Yahuda saboda abin da Manasse ya aikata don yă tozarta shi ba.
Cependant le Seigneur ne revint point de la colère de sa grande fureur, dont fut irritée sa fureur contre Juda, à cause des sujets d’irritation qu’avait provoqués en lui Manassé.
27 Saboda haka Ubangiji ya ce, “Zan shafe Yahuda ma kamar yadda na shafe Isra’ila, daga gabana, zan ƙi Urushalima birnin da na zaɓa, da wannan haikali wanda na ce, ‘A can Sunana zai kasance.’”
C’est pourquoi le Seigneur dit: Juda aussi, je l’ôterai de devant ma face, comme j’en ai ôté Israël, et je rejetterai cette ville, que j’ai choisie, Jérusalem et cette maison dont j’ai dit: Mon nom sera là.
28 Game da sauran ayyukan mulkin Yosiya, da duk abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
Mais le reste des actions de Josias, et tout ce qu’il a fait, n’est-ce pas écrit dans le Livre des actions des jours des rois de Juda?
29 Yayinda Yosiya yake sarki, Fir’auna Neko, sarkin Masar ya haura zuwa Kogin Yuferites don yă taimaki sarkin Assuriya da yaƙi. Sarki Yosiya kuwa ya yi ƙoƙari ya hana shi wucewa, sa’ad da Fir’auna Neko ya gan shi, sai ya kashe shi a filin yaƙi a Megiddo.
Aux jours de Josias, Pharaon Néchao, roi d’Egypte, monta contre le roi des Assyriens, vers le fleuve d’Euphrate, et Josias, le roi, alla à sa rencontre; et il fut tué à Mageddo, lorsqu’il l’eut vu.
30 Bayin Yosiya suka ɗauko gawarsa daga Megiddo suka kai Urushalima, suka binne shi a kabarinsa. Sai mutanen ƙasar suka ɗauki Yehoyahaz ɗan Yosiya suka naɗa shi sarki a madadin mahaifinsa.
Et ses serviteurs l’enlevèrent mort de Mageddo, le portèrent à Jérusalem et l’ensevelirent dans son sépulcre. Alors le peuple du pays prit Joachaz, fils de Josias; et ils l’oignirent, et l’établirent en la place de son père.
31 Yehoyahaz yana da shekara ashirin da uku sa’ad da ya zama sarki. Ya yi mulki na wata uku a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Hamutal’yar Irmiya; mutuniyar Libna.
Joachaz avait vingt-trois ans lorsqu’il commença à régner, et il régna trois mois à Jérusalem: le nom de sa mère était Amital, fille de Jérémie de Lobna,
32 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, yadda kakanninsa suka yi.
Et il fit le mal devant le Seigneur, selon tout ce que ses pères avaient fait.
33 Fir’auna Neko ya sa shi a sarƙa a Ribla a ƙasar Hamat don kada yă yi mulki a Urushalima, sa’an nan ya sa wa Yahuda harajin talenti ɗari na azurfa, da talenti ɗaya na zinariya.
Et Pharaon Néchao l’enchaîna à Rébla, qui est dans la terre d’Emath, afin qu’il ne régnât point à Jérusalem, et il imposa une amende au pays de cent talents d’argent et un talent d’or.
34 Fir’auna Neko ya naɗa Eliyakim ɗan Yosiya sarki a maimakon mahaifinsa, ya kuma canja masa suna zuwa Yehohiyakim. Ya ɗauki Yehoyahaz ya kai Masar, a can ya mutu.
Et Pharaon Néchao établit roi Eliacim, fils de Josias, en la place de Josias, son père, et il changea son nom en Joakim: or il prit Joachaz et le conduisit en Egypte, et il y mourut.
35 Yehohiyakim ya riƙa biyan Fir’auna Neko azurfa da zinariyar da ya umarta. Don yă yi haka sai ya riƙa karɓar azurfa da zinariya daga mutanen ƙasar, kowa bisa ga ƙarfinsa.
Joakim donna à Pharaon l’argent et l’or, puisqu’il avait taxé le pays par tête, afin qu’ils fussent apportés ensemble selon l’ordre de Pharaon; et il exigea de chacun, selon ses moyens, tant l’argent que l’or du peuple du pays, pour donner à Pharaon Néchao.
36 Yehohiyakim yana da shekara ashirin da biyar sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekara goma sha ɗaya a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Zebuda’yar Fedahiya, mutuniyar Ruma.
Joakim avait vingt-cinq ans lorsqu’il commença à régner, et il régna onze ans à Jérusalem: le nom de sa mère était Zébida, fille de Phadaïa de Ruma.
37 Ya kuma aika mugunta a gaban Ubangiji yadda kakanninsa suka yi.
Et il fit le mal devant le Seigneur, selon tout ce qu’avaient fait ses pères.

< 2 Sarakuna 23 >