< 2 Sarakuna 23 >

1 Sai sarki ya kira dukan dattawan Yahuda da Urushalima.
Then the king sent, —and there were gathered unto him, all the elders of Judah, and Jerusalem;
2 Sai ya haura zuwa cikin haikalin Ubangiji tare da mutanen Yahuda, da na Urushalima, da firistoci, da annabawa, dukan mutane, manya da ƙanana. Ya karanta musu duk kalmomin Littafin Alkawari, wanda aka samu a haikalin Ubangiji.
and the king went up to the house of Yahweh, and all the men of Judah and all the inhabitants of Jerusalem with him, and the priests, and the prophets, and all the people, both small and great, —and he read in their ears, all the words of the book of the covenant, which had been found in the house of Yahweh.
3 Sarki ya tsaya dab da ginshiƙi ya kuma sabunta alkawarin a gaban Ubangiji, ya ce zai bi Ubangiji, yă kiyaye dokokinsa, da ƙa’idodinsa, da farillansa, da dukan zuciyarsa da dukan ransa, ta haka ya tabbatar da kalmomin alkawarin da yake a rubuce a cikin littafin nan. Sa’an nan dukan mutane ma suka yi alkawari yin haka.
And the king took his stand by the pillar, and solemnised a covenant before Yahweh—to follow Yahweh, and to keep his commandments and his testimonies and his statutes, with all [their] heart and with all [their] soul, to confirm the words of this covenant, written in this book. And all the people took their stand in the covenant.
4 Sai Yosiya ya umarci Hilkiya babban firist, tare da firistocin da suke taimakonsa, da masu tsaron ƙofa su kawar da dukan abubuwan da aka yi domin Ba’al, da domin Ashera, da kuma domin dukan rundunar taurari, daga haikalin Ubangiji. Ya ƙone su a bayan Urushalima a filayen Kwarin Kidron, ya kwashe tokan zuwa Betel.
Then the king commanded Hilkiah the high priest, and the priests of the second order, and the keepers of the entrance-hall, to bring forth, out of the temple of Yahweh, all the vessels that had been made for Baal and for the Sacred Stem, and for all the army of the heavens, —and he burned them up outside Jerusalem, in the fields of Kidron, and carried the ashes of them to Bethel;
5 Ya kawar da firistocin gumakan da sarakunan Yahuda suka naɗa don su ƙona turare a masujadan kan tuddai na garuruwan Yahuda, da kuma waɗanda suke kewaye da Urushalima, masu ƙona turare wa Ba’al, rana da wata, ga rukunin taurari, da kuma ga dukan rundunan taurari.
and he put down the idol-priests, whom the kings of Judah had appointed, so that incense might be burned in the high places, in the cities of Judah, and round about Jerusalem, —them also that burned incense to Baal, to the sun, and to the moon, and to the constellations, and to all the army of the heavens;
6 Ya ɗauke ginshiƙin Ashera daga haikalin Ubangiji zuwa Kwarin Kidron can bayan Urushalima, ya ƙone shi a can. Ya niƙa shi sai da ya zama toka, sai ya watsar da ƙurar a filin kabarin talakawa.
and he brought forth the Sacred Stem out of the house of Yahweh, outside Jerusalem, into the Kidron ravine, and burned it in the Kidron ravine, and crushed it to powder, —and cast the powder upon the graves of the sons of the people;
7 Ya kuma rurrushe mazaunan karuwai mazan haikali waɗanda suke a haikalin Ubangiji, da kuma inda mata suke yi wa Ashera saƙa.
and he brake down the houses of the male devotees, which were in the house of Yahweh, —where the women did weave houses to the Sacred Stem;
8 Yosiya ya kawo dukan firistoci daga garuruwan Yahuda, ya kuma lalatar da masujadan kan tuddai daga Geba har zuwa Beyersheba, inda firistoci suke ƙona turare. Ya rurrushe matsafai a ƙofofi shigan gari na mashigi zuwa Ƙofar Yoshuwa, gwamnan birnin, wanda yake a hagu da ƙofar birnin.
and be brought in all the priests out of the cities of Judah, and defiled the high places where, the priests, had burned incense, from Geba unto Beer-sheba, —and brake down the high places of the gates, that were at the entrance of the gate of Joshua, the governor of the city, which were on one’s left hand, in the gate of the city;
9 Ko da yake firistocin masujadan kan tuddai ba su yi hidima a bagaden Ubangiji a Urushalima ba, sun ci burodi marar yisti tare da sauran firistoci.
howbeit, the priests of the high places came not up unto the altar of Yahweh, in Jerusalem, save only that they did eat unleavened bread in the midst of their brethren;
10 Ya lalatar da Tofet, wanda yake a Kwarin Ben Hinnom, don kada kowa yă iya yin amfani da wurin don yă miƙa hadayar ɗansa, ko’yarsa a wuta ga Molek.
and he defiled Topheth, which was in the valley of the son of Hinnom, —so that no man might cause his son or his daughter to pass through the fire unto Molech;
11 Ya kawar da dawakan nan da sarakunan Yahuda suka keɓe wa gumakan nan na rana daga mashigin haikalin Ubangiji. Waɗannan dawakan suna kusa da ɗakin Natan Melek, ɗaya daga cikin dattawan sarki. Yosiya ya kuma ƙone kekunan yaƙi a yin sujada ga gumakan nan rana.
and he did away with the horses, which the kings of Judah had devoted to the sun, at the entrance of the house of Yahweh, near the chamber of Nathan-melech the courtier, which was in the suburbs, also, the chariots of the sun, burned he with fire;
12 Ya rushe bagadan da sarakunan Yahuda suka kafa a kan ɗakin sama kusa da ɗakin sama na Ahaz, da kuma bagadai biyu da Manasse ya gina a filaye biyu na haikalin Ubangiji. Ya kawar da su daga can, ya farfashe su, ya zubar da tarkacen a Kwarin Kidron.
and, the altars which were on the roof of the upper chamber of Ahaz, which the kings of Judah had made, also the altars which Manasseh had made, in the two courts of the house of Yahweh, did the king break down, —and hurried away from thence, and cast out the powder of them into the Kidron ravine;
13 Sarkin kuma ya lalatar da masujadan kan tuddan da suke gabas da Urushalima, kudu da Tudun Hallaka, waɗanda Solomon sarkin Isra’ila ya gina don Ashtarot, ƙazantacciyar alliyar Sidoniyawa, da Kemosh ƙazantaccen allah na Mowab, da kuma Molek allahn banƙyama na mutanen Ammon.
and, the high places that were before Jerusalem, which were on the right hand of the mount of destruction, which Solomon king of Israel had built unto Ashtoreth—the abomination of the Zidonians, and unto Chemosh—the abomination of the Moabites, and unto Milcom—the disgusting thing of the sons of Ammon, did the king defile;
14 Yosiya ya farfashe keɓaɓɓun duwatsu, ya rurrushe ginshiƙan Asheransu, ya baza ƙasusuwan mutane a can.
and he brake in pieces the pillars, and cut down the Sacred Stems, —and filled their place with human bones:
15 Har ma da bagaden Betel, masujadan kan tudun da Yerobowam ɗan Nebat ya yi, wanda ya sa Isra’ila suka yi zunubi. Wannan bagade da masujadan kan tudun ma ya kawar, ya ƙone masujadan kan tudun, ya niƙa su, ya kuma ƙone ginshiƙin Ashera.
moreover also, the altar that was in Bethel, the high place which Jeroboam son of Nebat made, wherewith he caused, Israel, to sin, —even that altar, and the high place, brake he down, —and burned the high place, crushing it to powder, and burned a Sacred Stem.
16 Da Yosiya ya dubi kewaye da shi, ya ga kaburburan da suke can a gefen tudu, sai ya sa aka kwaso ƙasusuwan da suke cikinsu aka ƙone a kan bagade don yă lalatar da shi bisa ga maganar Ubangiji ta bakin mutumin Allah, wanda ya yi annabcin waɗannan abubuwa.
And, when Josiah turned, and saw the graves which were there, in the mount, he sent and took the bones out of the graves, and burned upon the altar, and defiled it, —according to the word of Yahweh, which the man of God proclaimed, who proclaimed these things.
17 Sarkin ya yi tambaya, ya ce, “Wane kabari ke nan nake gani?” Mutanen birnin suka ce, “Ai, kabarin annabin Allah ne wanda ya fito daga Yahuda, shi ne ya yi annabcin waɗannan abubuwan da ka aikata gāba da bagaden Betel.”
Then said he—What is yonder erection, which I do see? And the men of the city said unto him—The grave of the man of God, who came in out of Judah, and proclaimed these things, which thou hast done, concerning the altar of Bethel.
18 Sai ya ce, “Ku rabu da shi, kada wani yă dami ƙasusuwansa.” Saboda haka suka bar kasusuwansa, da na annabin da ya fito Samariya.
And he said—Let him rest, let, no man, disturb his bones. So they let his bones rest, with the bones of the prophet who came in out of Samaria.
19 Kamar yadda ya yi a Betel, Yosiya ya kawar da dukan ɗakunan gumaka a kan tuddan da sarakunan Isra’ila suka gina a garuruwan Samariya, waɗanda suka tozarta Ubangiji.
Moreover also, all the houses of the high places which were in the cities of Samaria, which the kings of Israel had made, so as to provoke Yahweh to anger, did Josiah remove, —and he did to them according to all the doings which he had done in Bethel;
20 Yosiya ya yayyanka dukan firistoci na waɗannan masujadan kan tuddai, ya kuma ƙone ƙasusuwan mutane a kansu. Sa’an nan ya koma Urushalima.
and he sacrificed all the priests of the high places, who were there, by the altars, and burned human bones thereupon, —and returned to Jerusalem.
21 Sarkin ya ba da umarnin nan ga dukan mutane, cewa, “Ku yi Bikin Ƙetarewa ga Ubangiji Allahnku, yadda aka rubuta a Littafin Alkawari.”
Then did the king command all the people, saying, Keep ye a passover unto Yahweh, your God, —such as is written in this book of the covenant.
22 Ba a taɓa yin irin Bikin Ƙetarewa haka ba, tun zamanin da masu shari’a suke aiki a matsayin sarakuna, ko a kwanakin sarakunan Isra’ila, ko na Yahuda.
Surely there had not been held such a passover as this, from the days of the Judges who judged Israel, —nor all the days of the kings of Israel, and the kings of Judah;
23 Amma a shekara ta goma sha takwas ta mulkin sarki Yosiya, aka yi Bikin Ƙetarewan nan ga Ubangiji a Urushalima.
save only, in the eighteenth year of King Josiah, when this passover was held unto Yahweh, in Jerusalem.
24 Ban da haka, Yosiya ya kawar da masu duba, da masu maita, da allolin gidaje, da gumaka, da duk wani abin banƙyaman da ya gani a Yahuda da Urushalima. Ya yi wannan domin yă cika wa’adodin shari’a yadda suke a littafin da Hilkiya firist ya samu a haikalin Ubangiji.
Moreover also, them who had familiar spirits, and the wizards, and the household gods, and the manufactured gods, and the abominations which were to be seen in the land of Judah, and in Jerusalem, did Josiah consume, —that he might confirm the words of the law which were written in the book that Hilkiah the priest had found in the house of Yahweh.
25 Babu wani sarki kafin Yosiya, ko kuma a bayansa, wanda ya juya ga Ubangiji da dukan zuciyarsa, da dukan ransa, da dukan ƙarfinsa bisa ga shari’ar Musa, kamar yadda ya yi.
And, like him, was no king, before him, who turned unto Yahweh with all his heart, and with all his soul, and with all his might, according to all the law of Moses, —neither, after him, arose one, like him.
26 Duk da haka, Ubangiji bai huce daga zafin fushinsa wanda ya ƙuna game da Yahuda saboda abin da Manasse ya aikata don yă tozarta shi ba.
Howbeit, Yahweh turned not away from the glow of his great anger, wherewith his anger glowed against Judah—because of all the provocations wherewith, Manasseh, had provoked him.
27 Saboda haka Ubangiji ya ce, “Zan shafe Yahuda ma kamar yadda na shafe Isra’ila, daga gabana, zan ƙi Urushalima birnin da na zaɓa, da wannan haikali wanda na ce, ‘A can Sunana zai kasance.’”
So Yahweh said: Even Judah, will I remove from my presence, as I have removed Israel, —and will reject this city, which I had chosen, even Jerusalem, and the house as to which I had said, My Name, shall be, there.
28 Game da sauran ayyukan mulkin Yosiya, da duk abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
Now, the rest of the story of Josiah, and all that he did, are, they, not written in the book of the Chronicles of the Kings of Judah?
29 Yayinda Yosiya yake sarki, Fir’auna Neko, sarkin Masar ya haura zuwa Kogin Yuferites don yă taimaki sarkin Assuriya da yaƙi. Sarki Yosiya kuwa ya yi ƙoƙari ya hana shi wucewa, sa’ad da Fir’auna Neko ya gan shi, sai ya kashe shi a filin yaƙi a Megiddo.
In his days, came up Pharaoh-necoh king of Egypt, against the king of Assyria, unto the river Euphrates, —and, when King Josiah went against him, he slew him at Megiddo, as soon as he saw him.
30 Bayin Yosiya suka ɗauko gawarsa daga Megiddo suka kai Urushalima, suka binne shi a kabarinsa. Sai mutanen ƙasar suka ɗauki Yehoyahaz ɗan Yosiya suka naɗa shi sarki a madadin mahaifinsa.
And his servants conveyed him in a chariot, dead, from Megiddo, and brought him to Jerusalem, and buried him in his own sepulchre, —and the people of the land took Jehoahaz, son of Josiah, and anointed him, and made, him, king, in his father’s stead.
31 Yehoyahaz yana da shekara ashirin da uku sa’ad da ya zama sarki. Ya yi mulki na wata uku a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Hamutal’yar Irmiya; mutuniyar Libna.
Twenty-three years old, was Jehoahaz when he began to reign, and, three months, reigned he in Jerusalem, —and, his mother’s name, was Hamutal daughter of Jeremiah, of Libnah.
32 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, yadda kakanninsa suka yi.
And he did the thing that was wicked in the eyes of Yahweh, according to all that his, fathers, had done.
33 Fir’auna Neko ya sa shi a sarƙa a Ribla a ƙasar Hamat don kada yă yi mulki a Urushalima, sa’an nan ya sa wa Yahuda harajin talenti ɗari na azurfa, da talenti ɗaya na zinariya.
And Pharaoh-necoh put him in bonds at Riblah, in the land of Hamath, that he might not reign in Jerusalem, —and he laid a fine upon the land, a hundred talents of silver, and a talent of gold.
34 Fir’auna Neko ya naɗa Eliyakim ɗan Yosiya sarki a maimakon mahaifinsa, ya kuma canja masa suna zuwa Yehohiyakim. Ya ɗauki Yehoyahaz ya kai Masar, a can ya mutu.
And Pharaoh-necoh made Eliakim son of Josiah king, instead of Josiah his father, and turned his name to Jehoiakim, —and, Jehoahaz, took he away, so he entered Egypt, and died there.
35 Yehohiyakim ya riƙa biyan Fir’auna Neko azurfa da zinariyar da ya umarta. Don yă yi haka sai ya riƙa karɓar azurfa da zinariya daga mutanen ƙasar, kowa bisa ga ƙarfinsa.
And, the silver and the gold, did Jehoiakim give unto Pharaoh, howbeit he assessed the land, that he might give the silver at the bidding of Pharaoh, —every man, according to his assessment, exacted the silver and the gold of the people of the land, that he might give it to Pharaoh-necoh.
36 Yehohiyakim yana da shekara ashirin da biyar sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekara goma sha ɗaya a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Zebuda’yar Fedahiya, mutuniyar Ruma.
Twenty-five years old, was Jehoiakim when he began to reign, and, eleven years, reigned he in Jerusalem, —and, his mother’s name, was Zebudah daughter of Pedaiah, of Rumah.
37 Ya kuma aika mugunta a gaban Ubangiji yadda kakanninsa suka yi.
And he did the thing that was wicked in the eyes of Yahweh, —according to all that, his fathers, had done.

< 2 Sarakuna 23 >