< 2 Sarakuna 23 >
1 Sai sarki ya kira dukan dattawan Yahuda da Urushalima.
And the king sends, and they gather all [the] elderly of Judah and Jerusalem to him,
2 Sai ya haura zuwa cikin haikalin Ubangiji tare da mutanen Yahuda, da na Urushalima, da firistoci, da annabawa, dukan mutane, manya da ƙanana. Ya karanta musu duk kalmomin Littafin Alkawari, wanda aka samu a haikalin Ubangiji.
and the king goes up to the house of YHWH, and every man of Judah, and all the inhabitants of Jerusalem, with him, and the priests, and the prophets, and all the people, from small to great, and he reads in their ears all the words of the Scroll of the Covenant that is found in the house of YHWH.
3 Sarki ya tsaya dab da ginshiƙi ya kuma sabunta alkawarin a gaban Ubangiji, ya ce zai bi Ubangiji, yă kiyaye dokokinsa, da ƙa’idodinsa, da farillansa, da dukan zuciyarsa da dukan ransa, ta haka ya tabbatar da kalmomin alkawarin da yake a rubuce a cikin littafin nan. Sa’an nan dukan mutane ma suka yi alkawari yin haka.
And the king stands by the pillar, and makes the covenant before YHWH, to walk after YHWH, and to keep His commands, and His testimonies, and His statutes, with all the heart, and with all the soul, to establish the words of this covenant that are written on this scroll, and all the people stand in the covenant.
4 Sai Yosiya ya umarci Hilkiya babban firist, tare da firistocin da suke taimakonsa, da masu tsaron ƙofa su kawar da dukan abubuwan da aka yi domin Ba’al, da domin Ashera, da kuma domin dukan rundunar taurari, daga haikalin Ubangiji. Ya ƙone su a bayan Urushalima a filayen Kwarin Kidron, ya kwashe tokan zuwa Betel.
And the king commands Hilkiah the high priest, and the priests of the second order, and the keepers of the threshold, to bring out from the temple of YHWH all the vessels that are made for Ba‘al, and for the Asherah, and for all the host of the heavens, and he burns them at the outside of Jerusalem, in the fields of Kidron, and has carried their ashes to Beth-El.
5 Ya kawar da firistocin gumakan da sarakunan Yahuda suka naɗa don su ƙona turare a masujadan kan tuddai na garuruwan Yahuda, da kuma waɗanda suke kewaye da Urushalima, masu ƙona turare wa Ba’al, rana da wata, ga rukunin taurari, da kuma ga dukan rundunan taurari.
And he has caused to cease the idolatrous priests whom the kings of Judah have appointed (and they make incense in high places, in cities of Judah and outskirts of Jerusalem), and those making incense to Ba‘al, to the sun, and to the moon, and to the twelve signs, and to all the host of the heavens.
6 Ya ɗauke ginshiƙin Ashera daga haikalin Ubangiji zuwa Kwarin Kidron can bayan Urushalima, ya ƙone shi a can. Ya niƙa shi sai da ya zama toka, sai ya watsar da ƙurar a filin kabarin talakawa.
And he brings out the Asherah from the house of YHWH to the outside of Jerusalem, to the Brook of Kidron, and burns it at the Brook of Kidron, and beats it small to dust, and casts its dust on the grave of the sons of the people.
7 Ya kuma rurrushe mazaunan karuwai mazan haikali waɗanda suke a haikalin Ubangiji, da kuma inda mata suke yi wa Ashera saƙa.
And he breaks down the houses of the whoremongers that [are] in the house of YHWH, where the women are weaving houses for the Asherah.
8 Yosiya ya kawo dukan firistoci daga garuruwan Yahuda, ya kuma lalatar da masujadan kan tuddai daga Geba har zuwa Beyersheba, inda firistoci suke ƙona turare. Ya rurrushe matsafai a ƙofofi shigan gari na mashigi zuwa Ƙofar Yoshuwa, gwamnan birnin, wanda yake a hagu da ƙofar birnin.
And he brings in all the priests out of the cities of Judah, and defiles the high places where the priests have made incense, from Geba to Beer-Sheba, and has broken down the high places of the gates that [are] at the opening of the Gate of Joshua, head of the city, that [is] on a man’s left hand at the gate of the city;
9 Ko da yake firistocin masujadan kan tuddai ba su yi hidima a bagaden Ubangiji a Urushalima ba, sun ci burodi marar yisti tare da sauran firistoci.
only, the priests of the high places do not come up to the altar of YHWH in Jerusalem, but they have eaten unleavened things in the midst of their brothers.
10 Ya lalatar da Tofet, wanda yake a Kwarin Ben Hinnom, don kada kowa yă iya yin amfani da wurin don yă miƙa hadayar ɗansa, ko’yarsa a wuta ga Molek.
And he has defiled Topheth that [is] in the Valley of the Son of Hinnom, so that no man causes his son and his daughter to pass over through fire to Molech.
11 Ya kawar da dawakan nan da sarakunan Yahuda suka keɓe wa gumakan nan na rana daga mashigin haikalin Ubangiji. Waɗannan dawakan suna kusa da ɗakin Natan Melek, ɗaya daga cikin dattawan sarki. Yosiya ya kuma ƙone kekunan yaƙi a yin sujada ga gumakan nan rana.
And he causes to cease the horses that the kings of Judah have given to the sun from the entering in of the house of YHWH, by the chamber of Nathan-Melech the eunuch, that [is] in the outskirts; and he has burned the chariots of the sun with fire.
12 Ya rushe bagadan da sarakunan Yahuda suka kafa a kan ɗakin sama kusa da ɗakin sama na Ahaz, da kuma bagadai biyu da Manasse ya gina a filaye biyu na haikalin Ubangiji. Ya kawar da su daga can, ya farfashe su, ya zubar da tarkacen a Kwarin Kidron.
And the altars that [are] on the top of the upper chamber of Ahaz, that the kings of Judah made, and the altars that Manasseh made in the two courts of the house of YHWH, the king has broken down, and removes from there, and has cast their dust into the Brook of Kidron.
13 Sarkin kuma ya lalatar da masujadan kan tuddan da suke gabas da Urushalima, kudu da Tudun Hallaka, waɗanda Solomon sarkin Isra’ila ya gina don Ashtarot, ƙazantacciyar alliyar Sidoniyawa, da Kemosh ƙazantaccen allah na Mowab, da kuma Molek allahn banƙyama na mutanen Ammon.
And the high places that [are] on the front of Jerusalem, that [are] on the right of the Mount of Corruption, that Solomon king of Israel had built to Ashtoreth, abomination of the Zidonians, and Chemosh, abomination of Moab, and to Milcom, abomination of the sons of Ammon, the king has defiled.
14 Yosiya ya farfashe keɓaɓɓun duwatsu, ya rurrushe ginshiƙan Asheransu, ya baza ƙasusuwan mutane a can.
And he has broken the standing-pillars in pieces, and cuts down the Asherim, and fills their place with bones of men;
15 Har ma da bagaden Betel, masujadan kan tudun da Yerobowam ɗan Nebat ya yi, wanda ya sa Isra’ila suka yi zunubi. Wannan bagade da masujadan kan tudun ma ya kawar, ya ƙone masujadan kan tudun, ya niƙa su, ya kuma ƙone ginshiƙin Ashera.
and also the altar that [is] in Beth-El, the high place that Jeroboam son of Nebat made, by which he made Israel sin, both that altar and the high place he has broken down, and burns the high place—he has beat it small to dust, and has burned the Asherah.
16 Da Yosiya ya dubi kewaye da shi, ya ga kaburburan da suke can a gefen tudu, sai ya sa aka kwaso ƙasusuwan da suke cikinsu aka ƙone a kan bagade don yă lalatar da shi bisa ga maganar Ubangiji ta bakin mutumin Allah, wanda ya yi annabcin waɗannan abubuwa.
And Josiah turns, and sees the graves that [are] there on the mountain, and sends and takes the bones out of the graves, and burns [them] on the altar, and defiles it, according to the word of YHWH that the man of God proclaimed, who proclaimed these things.
17 Sarkin ya yi tambaya, ya ce, “Wane kabari ke nan nake gani?” Mutanen birnin suka ce, “Ai, kabarin annabin Allah ne wanda ya fito daga Yahuda, shi ne ya yi annabcin waɗannan abubuwan da ka aikata gāba da bagaden Betel.”
And he says, “What [is] this sign that I see?” And the men of the city say to him, “The grave of the man of God who has come from Judah, and proclaims these things that you have done concerning the altar of Beth-El.”
18 Sai ya ce, “Ku rabu da shi, kada wani yă dami ƙasusuwansa.” Saboda haka suka bar kasusuwansa, da na annabin da ya fito Samariya.
And he says, “Leave him alone, let no man touch his bones”; and they let his bones escape with the bones of the prophet who came out of Samaria.
19 Kamar yadda ya yi a Betel, Yosiya ya kawar da dukan ɗakunan gumaka a kan tuddan da sarakunan Isra’ila suka gina a garuruwan Samariya, waɗanda suka tozarta Ubangiji.
And also all the houses of the high places that [are] in the cities of Samaria, that the kings of Israel made to provoke to anger, Josiah has turned aside, and does to them according to all the deeds that he did in Beth-El.
20 Yosiya ya yayyanka dukan firistoci na waɗannan masujadan kan tuddai, ya kuma ƙone ƙasusuwan mutane a kansu. Sa’an nan ya koma Urushalima.
And he slays all the priests of the high places who [are] there by the altars, and burns the bones of man on them, and turns back to Jerusalem.
21 Sarkin ya ba da umarnin nan ga dukan mutane, cewa, “Ku yi Bikin Ƙetarewa ga Ubangiji Allahnku, yadda aka rubuta a Littafin Alkawari.”
And the king commands the whole of the people, saying, “Make a Passover to your God YHWH, as it is written on this scroll of the covenant.”
22 Ba a taɓa yin irin Bikin Ƙetarewa haka ba, tun zamanin da masu shari’a suke aiki a matsayin sarakuna, ko a kwanakin sarakunan Isra’ila, ko na Yahuda.
Surely there has not been made like this Passover from the days of the ones judging who judged Israel, even all the days of the kings of Israel, and of the kings of Judah;
23 Amma a shekara ta goma sha takwas ta mulkin sarki Yosiya, aka yi Bikin Ƙetarewan nan ga Ubangiji a Urushalima.
but in the eighteenth year of King Josiah, this Passover has been made to YHWH in Jerusalem.
24 Ban da haka, Yosiya ya kawar da masu duba, da masu maita, da allolin gidaje, da gumaka, da duk wani abin banƙyaman da ya gani a Yahuda da Urushalima. Ya yi wannan domin yă cika wa’adodin shari’a yadda suke a littafin da Hilkiya firist ya samu a haikalin Ubangiji.
And also, those having familiar spirits, and the wizards, and the teraphim, and the idols, and all the abominations that were seen in the land of Judah, and in Jerusalem, Josiah has put away, in order to establish the words of the Law that are written on the scroll that Hilkiah the priest has found in the house of YHWH.
25 Babu wani sarki kafin Yosiya, ko kuma a bayansa, wanda ya juya ga Ubangiji da dukan zuciyarsa, da dukan ransa, da dukan ƙarfinsa bisa ga shari’ar Musa, kamar yadda ya yi.
And like him there has not been before him a king who turned back to YHWH with all his heart, and with all his soul, and with all his might, according to all the Law of Moses, and after him there has none risen like him.
26 Duk da haka, Ubangiji bai huce daga zafin fushinsa wanda ya ƙuna game da Yahuda saboda abin da Manasse ya aikata don yă tozarta shi ba.
Only, YHWH has not turned back from the fierceness of His great anger with which His anger burned against Judah, because of all the provocations with which Manasseh provoked him,
27 Saboda haka Ubangiji ya ce, “Zan shafe Yahuda ma kamar yadda na shafe Isra’ila, daga gabana, zan ƙi Urushalima birnin da na zaɓa, da wannan haikali wanda na ce, ‘A can Sunana zai kasance.’”
and YHWH says, “I also turn Judah aside from my presence, as I turned Israel aside, and I have rejected this city that I have chosen—Jerusalem, and the house of which I said, My Name is there.”
28 Game da sauran ayyukan mulkin Yosiya, da duk abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
And the rest of the matters of Josiah and all that he did, are they not written on the scroll of the Chronicles of the Kings of Judah?
29 Yayinda Yosiya yake sarki, Fir’auna Neko, sarkin Masar ya haura zuwa Kogin Yuferites don yă taimaki sarkin Assuriya da yaƙi. Sarki Yosiya kuwa ya yi ƙoƙari ya hana shi wucewa, sa’ad da Fir’auna Neko ya gan shi, sai ya kashe shi a filin yaƙi a Megiddo.
In his days Pharaoh Necho king of Egypt has come up against the king of Asshur, by the Euphrates River, and King Josiah goes out to meet him, and [Pharaoh Necho] puts him to death in Megiddo when he sees him.
30 Bayin Yosiya suka ɗauko gawarsa daga Megiddo suka kai Urushalima, suka binne shi a kabarinsa. Sai mutanen ƙasar suka ɗauki Yehoyahaz ɗan Yosiya suka naɗa shi sarki a madadin mahaifinsa.
And his servants cause him to ride dying from Megiddo, and bring him to Jerusalem, and bury him in his own grave, and the people of the land take Jehoahaz son of Josiah, and anoint him, and cause him to reign instead of his father.
31 Yehoyahaz yana da shekara ashirin da uku sa’ad da ya zama sarki. Ya yi mulki na wata uku a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Hamutal’yar Irmiya; mutuniyar Libna.
Jehoahaz [is] a son of twenty-three years in his reigning, and he has reigned three months in Jerusalem, and the name of his mother [is] Hamutal daughter of Jeremiah of Libnah,
32 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, yadda kakanninsa suka yi.
and he does evil in the eyes of YHWH, according to all that his fathers did,
33 Fir’auna Neko ya sa shi a sarƙa a Ribla a ƙasar Hamat don kada yă yi mulki a Urushalima, sa’an nan ya sa wa Yahuda harajin talenti ɗari na azurfa, da talenti ɗaya na zinariya.
and Pharaoh Necho binds him in Riblah, in the land of Hamath, from reigning in Jerusalem, and he puts a fine on the land—one hundred talents of silver, and a talent of gold.
34 Fir’auna Neko ya naɗa Eliyakim ɗan Yosiya sarki a maimakon mahaifinsa, ya kuma canja masa suna zuwa Yehohiyakim. Ya ɗauki Yehoyahaz ya kai Masar, a can ya mutu.
And Pharaoh Necho causes Eliakim son of Josiah to reign instead of his father Josiah, and turns his name to Jehoiakim, and he has taken Jehoahaz away, and he comes to Egypt, and dies there.
35 Yehohiyakim ya riƙa biyan Fir’auna Neko azurfa da zinariyar da ya umarta. Don yă yi haka sai ya riƙa karɓar azurfa da zinariya daga mutanen ƙasar, kowa bisa ga ƙarfinsa.
And Jehoiakim has given the silver and the gold to Pharaoh; only he valued the land to give the silver by the command of Pharaoh; from each, according to his valuation, he exacted the silver and the gold, from the people of the land, to give to Pharaoh Necho.
36 Yehohiyakim yana da shekara ashirin da biyar sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekara goma sha ɗaya a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Zebuda’yar Fedahiya, mutuniyar Ruma.
Jehoiakim [is] a son of twenty-five years in his reigning, and he has reigned eleven years in Jerusalem, and the name of his mother [is] Zebudah daughter of Pedaiah of Rumah,
37 Ya kuma aika mugunta a gaban Ubangiji yadda kakanninsa suka yi.
and he does evil in the eyes of YHWH, according to all that his fathers did.