< 2 Sarakuna 23 >

1 Sai sarki ya kira dukan dattawan Yahuda da Urushalima.
Tada kralj posla da se saberu kod njega sve judejske i jeruzalemske starješine.
2 Sai ya haura zuwa cikin haikalin Ubangiji tare da mutanen Yahuda, da na Urushalima, da firistoci, da annabawa, dukan mutane, manya da ƙanana. Ya karanta musu duk kalmomin Littafin Alkawari, wanda aka samu a haikalin Ubangiji.
Kralj potom uzađe u Dom Jahvin s Judejcima, Jeruzalemcima, svećenicima i prorocima i sa svim narodom, od najmanjega do najvećega. I pročita im sve riječi Knjige Saveza koja je nađena u Domu Jahvinu.
3 Sarki ya tsaya dab da ginshiƙi ya kuma sabunta alkawarin a gaban Ubangiji, ya ce zai bi Ubangiji, yă kiyaye dokokinsa, da ƙa’idodinsa, da farillansa, da dukan zuciyarsa da dukan ransa, ta haka ya tabbatar da kalmomin alkawarin da yake a rubuce a cikin littafin nan. Sa’an nan dukan mutane ma suka yi alkawari yin haka.
Kralj, stojeći na svome mjestu, obnovi pred Jahvom Savez da će slijediti Jahvu i držati se njegovih zapovijedi, pouka i uredaba svim srcem i svom dušom da bi ispunio sve stavke toga Saveza zapisane u ovoj knjizi. Sav je narod stupio u Savez.
4 Sai Yosiya ya umarci Hilkiya babban firist, tare da firistocin da suke taimakonsa, da masu tsaron ƙofa su kawar da dukan abubuwan da aka yi domin Ba’al, da domin Ashera, da kuma domin dukan rundunar taurari, daga haikalin Ubangiji. Ya ƙone su a bayan Urushalima a filayen Kwarin Kidron, ya kwashe tokan zuwa Betel.
Kralj je zapovjedio velikom svećeniku Hilkiji, svećenicima drugog reda i čuvarima hramskog praga da iz Svetišta Jahvina iznesu sve bogoslužne predmete što bijahu načinjeni za Baala, za Ašeru i za svu nebesku vojsku. Odredio je da sve to spale izvan Jeruzalema u poljima kidronskim, a pepeo je odnio u Betel.
5 Ya kawar da firistocin gumakan da sarakunan Yahuda suka naɗa don su ƙona turare a masujadan kan tuddai na garuruwan Yahuda, da kuma waɗanda suke kewaye da Urushalima, masu ƙona turare wa Ba’al, rana da wata, ga rukunin taurari, da kuma ga dukan rundunan taurari.
Uklonio je lažne svećenike koje su judejski kraljevi postavili da pale kad na uzvišicama, u gradovima judejskim i u okolici Jeruzalema; i one koji su palili kad Baalu, suncu, mjesecu, zvijezdama i svoj vojsci nebeskoj.
6 Ya ɗauke ginshiƙin Ashera daga haikalin Ubangiji zuwa Kwarin Kidron can bayan Urushalima, ya ƙone shi a can. Ya niƙa shi sai da ya zama toka, sai ya watsar da ƙurar a filin kabarin talakawa.
Izvan Jeruzalema iznio je iz Doma Jahvina, u dolinu kidronsku, Ašeru i spalio ju je u dolini kidronskoj, satro u prah, a prah bacio na groblje sinova pučkih.
7 Ya kuma rurrushe mazaunan karuwai mazan haikali waɗanda suke a haikalin Ubangiji, da kuma inda mata suke yi wa Ashera saƙa.
Razorio je stanove posvećenih bludnica koji su bili u Domu Jahvinu i u kojima su žene tkale haljine Ašeri.
8 Yosiya ya kawo dukan firistoci daga garuruwan Yahuda, ya kuma lalatar da masujadan kan tuddai daga Geba har zuwa Beyersheba, inda firistoci suke ƙona turare. Ya rurrushe matsafai a ƙofofi shigan gari na mashigi zuwa Ƙofar Yoshuwa, gwamnan birnin, wanda yake a hagu da ƙofar birnin.
Iz svih judejskih gradova doveo je svećenike i oskvrnuo je uzvišice gdje su ti svećenici prinosili kad, od Gebe do Beer Šebe. Zatim je srušio uzvišice pred vratima, one koje su bile na ulazu vrata Jošue, upravitelja grada, nalijevo kad se prilazi gradskim vratima.
9 Ko da yake firistocin masujadan kan tuddai ba su yi hidima a bagaden Ubangiji a Urushalima ba, sun ci burodi marar yisti tare da sauran firistoci.
Isto tako svećenici uzvišica nisu mogli uzlaziti žrtveniku Jahvinu u Jeruzalemu, ali su jeli kruhove bez kvasa među svojom braćom.
10 Ya lalatar da Tofet, wanda yake a Kwarin Ben Hinnom, don kada kowa yă iya yin amfani da wurin don yă miƙa hadayar ɗansa, ko’yarsa a wuta ga Molek.
Oskvrnio je Tofet u dolini Ben Hinom, kako nitko ne bi svoga sina ili kćerku provodio kroz oganj u čast Moleku.
11 Ya kawar da dawakan nan da sarakunan Yahuda suka keɓe wa gumakan nan na rana daga mashigin haikalin Ubangiji. Waɗannan dawakan suna kusa da ɗakin Natan Melek, ɗaya daga cikin dattawan sarki. Yosiya ya kuma ƙone kekunan yaƙi a yin sujada ga gumakan nan rana.
Razagnao je konje koje su judejski kraljevi prinijeli suncu na ulazu u Dom Jahvin, kraj sobe dvoranina Netan Meleka, koja se nalazila u blizini, i spalio je u ognju sunčana kola.
12 Ya rushe bagadan da sarakunan Yahuda suka kafa a kan ɗakin sama kusa da ɗakin sama na Ahaz, da kuma bagadai biyu da Manasse ya gina a filaye biyu na haikalin Ubangiji. Ya kawar da su daga can, ya farfashe su, ya zubar da tarkacen a Kwarin Kidron.
Žrtvenike na krovu koje bijahu sagradili judejski kraljevi i one koje je sagradio Manaše u oba predvorja Hrama Jahvina, kralj je srušio, uklonio ih odatle i bacio njihov prah u dolinu kidronsku.
13 Sarkin kuma ya lalatar da masujadan kan tuddan da suke gabas da Urushalima, kudu da Tudun Hallaka, waɗanda Solomon sarkin Isra’ila ya gina don Ashtarot, ƙazantacciyar alliyar Sidoniyawa, da Kemosh ƙazantaccen allah na Mowab, da kuma Molek allahn banƙyama na mutanen Ammon.
Uzvišice koje su bile sučelice Jeruzalemu, na južnom dijelu Maslinske gore, i koje je izraelski kralj Salomon bio sagradio Aštarti, sramoti sidonskoj, Kemošu, sramoti moapskoj, i Milkomu, nakazi amonskoj - sve ih je kralj oskvrnio.
14 Yosiya ya farfashe keɓaɓɓun duwatsu, ya rurrushe ginshiƙan Asheransu, ya baza ƙasusuwan mutane a can.
Razbio je stupove, iskorijenio ašere i njihova je mjesta ispunio ljudskim kostima.
15 Har ma da bagaden Betel, masujadan kan tudun da Yerobowam ɗan Nebat ya yi, wanda ya sa Isra’ila suka yi zunubi. Wannan bagade da masujadan kan tudun ma ya kawar, ya ƙone masujadan kan tudun, ya niƙa su, ya kuma ƙone ginshiƙin Ashera.
Isto tako i žrtvenik u Betelu, uzvišicu koju je sagradio Jeroboam, sin Nebatov, koji je naveo Izraela na grijeh, kralj je srušio, oborio žrtvenik i tu uzvišicu, satro kamenje u prah, spalio ašere.
16 Da Yosiya ya dubi kewaye da shi, ya ga kaburburan da suke can a gefen tudu, sai ya sa aka kwaso ƙasusuwan da suke cikinsu aka ƙone a kan bagade don yă lalatar da shi bisa ga maganar Ubangiji ta bakin mutumin Allah, wanda ya yi annabcin waɗannan abubuwa.
A kad se Jošija okrenuo i vidio grobove koji bijahu ondje na gori, posla da se sakupe kosti iz onih grobova i spali ih na žrtveniku. Tako ga je oskvrnuo, izvršavajući riječ Jahvinu, koju je objavio čovjek Božji (dok je Jeroboam bio na žrtveniku za vrijeme svečanosti). Okrenuvši se, Jošija baci oči na grob čovjeka Božjeg koji je objavio sve to
17 Sarkin ya yi tambaya, ya ce, “Wane kabari ke nan nake gani?” Mutanen birnin suka ce, “Ai, kabarin annabin Allah ne wanda ya fito daga Yahuda, shi ne ya yi annabcin waɗannan abubuwan da ka aikata gāba da bagaden Betel.”
i upita: “Kakav je ono spomenik što ga vidim?” Ljudi iz grada odgovoriše mu: “To je grob čovjeka Božjeg koji je došao iz Judeje i koji je prorekao sve ovo što si ti učinio s betelskim žrtvenikom.”
18 Sai ya ce, “Ku rabu da shi, kada wani yă dami ƙasusuwansa.” Saboda haka suka bar kasusuwansa, da na annabin da ya fito Samariya.
“Pustite ga na miru”, reče kralj, “i neka nitko ne dira njegove kosti.” Tako su ostale njegove kosti netaknute s kostima proroka koji je došao iz Samarije.
19 Kamar yadda ya yi a Betel, Yosiya ya kawar da dukan ɗakunan gumaka a kan tuddan da sarakunan Isra’ila suka gina a garuruwan Samariya, waɗanda suka tozarta Ubangiji.
Jošija je jednako razorio sve hramove uzvišica koje su izraelski kraljevi sagradili po gradovima Samarije da bi srdili Jahvu i učinio je s njima kao što je učinio u Betelu.
20 Yosiya ya yayyanka dukan firistoci na waɗannan masujadan kan tuddai, ya kuma ƙone ƙasusuwan mutane a kansu. Sa’an nan ya koma Urushalima.
Sve svećenike uzvišica poklao je na žrtvenicima; na njima je spalio i ljudske kosti. Potom se vratio u Jeruzalem.
21 Sarkin ya ba da umarnin nan ga dukan mutane, cewa, “Ku yi Bikin Ƙetarewa ga Ubangiji Allahnku, yadda aka rubuta a Littafin Alkawari.”
Kralj naredi svemu narodu: “Svetkujte Pashu u čast Jahve, Boga svoga, po običaju koji je zapisan u ovoj Knjizi Saveza.”
22 Ba a taɓa yin irin Bikin Ƙetarewa haka ba, tun zamanin da masu shari’a suke aiki a matsayin sarakuna, ko a kwanakin sarakunan Isra’ila, ko na Yahuda.
Takva se Pasha nije svetkovala od vremena sudaca koji su sudili Izraelu i za sve vrijeme kraljeva izraelskih i judejskih.
23 Amma a shekara ta goma sha takwas ta mulkin sarki Yosiya, aka yi Bikin Ƙetarewan nan ga Ubangiji a Urushalima.
Samo je osamnaeste godine kraljevanja Jošijina svetkovana takva Pasha u čast Jahve, u Jeruzalemu.
24 Ban da haka, Yosiya ya kawar da masu duba, da masu maita, da allolin gidaje, da gumaka, da duk wani abin banƙyaman da ya gani a Yahuda da Urushalima. Ya yi wannan domin yă cika wa’adodin shari’a yadda suke a littafin da Hilkiya firist ya samu a haikalin Ubangiji.
Osim toga, sve bajače i sve vračare, sve kućne bogove i idole i sve sramote koje se mogu vidjeti u zemlji judejskoj i Jeruzalemu - sve je to Jošija uklonio da izvrši riječi Zakona, zapisane u knjizi koju je našao Hilkija, svećenik Doma Jahvina.
25 Babu wani sarki kafin Yosiya, ko kuma a bayansa, wanda ya juya ga Ubangiji da dukan zuciyarsa, da dukan ransa, da dukan ƙarfinsa bisa ga shari’ar Musa, kamar yadda ya yi.
Nije bilo prije njega takva kralja koji se obratio Jahvi svim srcem svojim, svom dušom svojom i svom snagom svojom, u svemu vjeran Zakonu Mojsijevu, a ni poslije njega nije mu bilo ravna.
26 Duk da haka, Ubangiji bai huce daga zafin fushinsa wanda ya ƙuna game da Yahuda saboda abin da Manasse ya aikata don yă tozarta shi ba.
Ipak Jahve nije odustao od plamena svoga velikoga gnjeva kojim je uskipio protiv Judejaca zbog svih izazova kojima ga je Manaše ljutio.
27 Saboda haka Ubangiji ya ce, “Zan shafe Yahuda ma kamar yadda na shafe Isra’ila, daga gabana, zan ƙi Urushalima birnin da na zaɓa, da wannan haikali wanda na ce, ‘A can Sunana zai kasance.’”
Jahve je odlučio: “Maknut ću Judejce ispred sebe kao što sam maknuo Izraela; odbacit ću ovaj grad koji sam izabrao, Jeruzalem, i Dom o kojem rekoh: 'Tu će biti Ime moje.'”
28 Game da sauran ayyukan mulkin Yosiya, da duk abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
Ostala povijest Jošijina i sve što je učinio, zar sve to nije zapisano u knjizi Ljetopisa judejskih kraljeva?
29 Yayinda Yosiya yake sarki, Fir’auna Neko, sarkin Masar ya haura zuwa Kogin Yuferites don yă taimaki sarkin Assuriya da yaƙi. Sarki Yosiya kuwa ya yi ƙoƙari ya hana shi wucewa, sa’ad da Fir’auna Neko ya gan shi, sai ya kashe shi a filin yaƙi a Megiddo.
U njegvo je vrijeme faraon Neko, egipatski kralj, krenuo protiv asirskoga kralja na rijeci Eufratu. Kralj Jošija pošao je preda nj, ali ga on ubi u Megidu, pri prvom susretu.
30 Bayin Yosiya suka ɗauko gawarsa daga Megiddo suka kai Urushalima, suka binne shi a kabarinsa. Sai mutanen ƙasar suka ɗauki Yehoyahaz ɗan Yosiya suka naɗa shi sarki a madadin mahaifinsa.
Sluge njegove prenesoše mu tijelo kolima iz Megida, odvezoše ga u Jeruzalem i sahraniše u njegovoj grobnici. Sav narod zemlje primi Joahaza, sina Jošijina; pomazaše ga i proglasiše kraljem namjesto njegova oca.
31 Yehoyahaz yana da shekara ashirin da uku sa’ad da ya zama sarki. Ya yi mulki na wata uku a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Hamutal’yar Irmiya; mutuniyar Libna.
Joahazu bijahu dvadeset i tri godine kad se zakraljio. Kraljevao je tri mjeseca u Jeruzalemu. Njegova se majka zvala Hamitah, kći Jeremije, i bila je iz Libne.
32 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, yadda kakanninsa suka yi.
On je činio što je zlo u očima Jahvinim, sve kao što su činili oci njegovi.
33 Fir’auna Neko ya sa shi a sarƙa a Ribla a ƙasar Hamat don kada yă yi mulki a Urushalima, sa’an nan ya sa wa Yahuda harajin talenti ɗari na azurfa, da talenti ɗaya na zinariya.
Faraon Neko bacio ga je u okove u Ribli, na području Hamata, da ne vlada u Jeruzalemu i udario je na zemlju danak od stotinu talenata srebra i deset talenata zlata.
34 Fir’auna Neko ya naɗa Eliyakim ɗan Yosiya sarki a maimakon mahaifinsa, ya kuma canja masa suna zuwa Yehohiyakim. Ya ɗauki Yehoyahaz ya kai Masar, a can ya mutu.
Faraon Neko postavio je za kralja Elijakima, sina Jošijina, na mjesto njegova oca Jošije. I ime mu je promijenio u Jojakim. A Joahaza je uzeo i odveo u Egipat te on umrije ondje.
35 Yehohiyakim ya riƙa biyan Fir’auna Neko azurfa da zinariyar da ya umarta. Don yă yi haka sai ya riƙa karɓar azurfa da zinariya daga mutanen ƙasar, kowa bisa ga ƙarfinsa.
Jojakim je dao faraonu srebro i zlato, ali je nametnuo zemlji porez da bi smogao svotu koju je faraon zahtijevao. Svakome je nametnuo prema njegovu stanju, uzimao srebro i zlato koje je morao davati faraonu Neku.
36 Yehohiyakim yana da shekara ashirin da biyar sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekara goma sha ɗaya a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Zebuda’yar Fedahiya, mutuniyar Ruma.
Jojakimu je bilo dvadeset i pet godina kad je postao kraljem i kraljevao je jedanaest godina u Jeruzalemu. Materi mu je bilo ime Zebida, kći Pedajina, i bila je iz Rume.
37 Ya kuma aika mugunta a gaban Ubangiji yadda kakanninsa suka yi.
On je činio što je zlo u očima Jahvinim, sve kao što su činili i oci njegovi.

< 2 Sarakuna 23 >