< 2 Sarakuna 22 >

1 Yosiya yana da shekara takwas sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekara talatin da ɗaya a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Yedida’yar Adahiya; mutuniyar Bozkat.
Josias était âgé de huit ans quand il devint roi, et il régna trente et un ans à Jérusalem. Sa mère s'appelait Jédida, fille d'Adaja, de Botskath.
2 Ya aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji ya kuma bi dukan gurbin kakansa Dawuda, bai bauɗe hagu ko dama ba.
Il fit ce qui est droit aux yeux de l'Éternel, il marcha dans toutes les voies de David, son père, et ne s'en détourna ni à droite ni à gauche.
3 A shekara ta goma sha takwas ta mulkinsa, Sarki Yosiya ya aiki Shafan ɗan Azaliya, ɗan Meshullam, magatakarda, zuwa haikalin Ubangiji. Ya ce,
Or, la dix-huitième année du roi Josias, le roi envoya à la maison de l'Éternel Shaphan le secrétaire, fils d'Atsalia, fils de Meshullam, en lui disant:
4 “Ka haura zuwa wurin Hilkiya babban firist ka sa yă shirya kuɗin da aka kawo a haikalin Ubangiji, wanda masu tsaron ƙofa suka tara daga mutane.
Monte vers Hilkija, le grand sacrificateur, et qu'il donne l'argent qu'on a apporté dans la maison de l'Éternel, et que ceux qui gardent le seuil ont recueilli du peuple.
5 Ka sa su danƙa su a hannun waɗanda aka zaɓa don biyan ma’aikatan da suka yi gyara a haikalin Ubangiji,
Qu'on le remette entre les mains de ceux qui ont la charge de l'ouvrage, et qui sont préposés à la maison de l'Éternel; et qu'ils le donnent à ceux qui exécutent l'ouvrage qui se fait dans la maison de l'Éternel, pour en réparer les dégradations:
6 wato, kafintoci, da magina, da masu tsara gini. Ka kuma sa su sayi katakai da sassaƙaƙƙun duwatsu don a gyara haikalin.
Aux charpentiers, aux constructeurs et aux maçons, pour acheter du bois et des pierres de taille pour réparer le temple.
7 Amma ba sa bukata su ba da bayanin kuɗin da aka danƙa musu domin suna aikinsu da aminci.”
Mais qu'on ne leur fasse pas rendre compte de l'argent qu'on leur délivre entre les mains, car ils agissent avec fidélité.
8 Hilkiya babban firist ya ce wa Shafan magatakarda, “Na sami Littafin Doka a haikalin Ubangiji.” Sai ya ba wa Shafan, shi kuma ya karanta.
Alors Hilkija, le grand sacrificateur, dit à Shaphan, le secrétaire: J'ai trouvé le livre de la loi dans la maison de l'Éternel. Et Hilkija donna ce livre-là à Shaphan, qui le lut.
9 Sa’an nan Shafan ya koma wurin sarki ya ce masa, “Hafsoshinka sun kwashe kuɗin da suke a haikalin Ubangiji, suka ba wa masu aiki da masu lura da haikalin.”
Et Shaphan, le secrétaire, vint vers le roi et lui fit ce rapport, en disant: Tes serviteurs ont versé l'argent qui a été trouvé dans le temple, et l'ont délivré entre les mains de ceux qui ont la charge de l'ouvrage, et qui sont préposés à la maison de l'Éternel.
10 Sa’an nan Shafan magatakarda ya ce wa sarki, “Hilkiya firist ya ba ni wani littafi.” Sai Shafan ya karanta shi a gaban sarki.
Shaphan, le secrétaire, fit encore ce rapport au roi: Hilkija, le sacrificateur, m'a donné un livre. Et Shaphan le lut devant le roi;
11 Da sarki ya ji kalmomin Littafin Doka, sai ya kece tufafinsa.
Et dès que le roi eut entendu les paroles du livre de la loi, il déchira ses vêtements.
12 Ya ba da waɗannan umarnai ga Hilkiya firist, da Ahikam ɗan Shafan, da Akbor ɗan Mikahiya, da Shafan magatakarda, da kuma Asahiya mai hidimar sarki, ya ce,
Et il donna ce commandement au sacrificateur Hilkija, à Achikam, fils de Shaphan, à Acbor, fils de Micaja, à Shaphan, le secrétaire, et à Asaja, serviteur du roi:
13 “Ku je, ku nemi nufin Ubangiji saboda ni da saboda jama’a da kuma saboda dukan Yahuda game da abin da wannan littafi da aka samo ya ƙunsa. Fushin Ubangiji mai girma ne a kanmu domin kakanninmu ba su kiyaye kalmomin littafin nan ba; ba su aikata bisa ga abin da yake a rubuce game da mu ba.”
Allez, consultez l'Éternel pour moi, pour le peuple et pour tout Juda, touchant les paroles de ce livre qui a été trouvé. Car la colère de l'Éternel, qui s'est allumée contre nous, est grande, parce que nos pères n'ont pas obéi aux paroles de ce livre, pour faire tout ce qui nous y est prescrit.
14 Sai Hilkiya firist, da Ahikam, Akbor, da Shafan, da kuma Asahiya suka je don su yi magana da annabiya Hulda, matan Shallum ɗan Tikba, ɗan Harhas, mai ajiyar tufafi. Tana zama a Urushalima, a Yanki na Biyu.
Et Hilkija, le sacrificateur, Achikam, Acbor, Shaphan et Asaja, s'en allèrent vers Hulda, la prophétesse, femme de Shallum, le gardien des vêtements, fils de Thikva, fils de Harhas, laquelle habitait à Jérusalem dans le second quartier; et ils lui parlèrent.
15 Sai ta ce musu, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ku faɗa wa mutumin da ya aike ku wurina,
Et elle leur dit: Ainsi a dit l'Éternel, le Dieu d'Israël: Dites à l'homme qui vous a envoyés vers moi:
16 ‘Ga abin da Ubangiji ya ce, zan kawo masifa wa wannan wuri da kuma wa kan mutanen wurin, bisa ga dukan abubuwan da suke a rubuce a cikin littafin da sarkin Yahuda ya karanta.
Ainsi parle l'Éternel: Voici, je vais faire venir du mal sur ce lieu et sur ses habitants, tout ce qui est dit dans le livre qu'a lu le roi de Juda.
17 Domin sun yashe ni suka ƙona turare wa waɗansu alloli, suka tozarta ni da dukan gumakan da hannuwansu suka sassaƙa, fushina zai yi ƙuna a kan wannan wuri, ba kuwa zai huce ba.’
Parce qu'ils m'ont abandonné et ont fait des encensements à d'autres dieux, pour m'irriter par toutes les œuvres de leurs mains, ma colère s'est allumée contre ce lieu, et elle ne s'éteindra point.
18 Ku faɗa wa sarkin Yahuda, wanda ya aike ku ku nemi nufin Ubangiji, ‘Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yana cewa game da kalmomin da ka ji.
Mais quant au roi de Juda, qui vous a envoyés pour consulter l'Éternel, vous lui direz: Ainsi a dit I'Éternel, le Dieu d'Israël, touchant les paroles que tu as entendues:
19 Domin zuciyarka mai tuba ce, ka kuma ƙasƙantar da kanka a gaban Ubangiji sa’ad da ka ji abin da na faɗa game da wannan wuri da mutanen wurin, cewa za su zama la’antattu da kuma kango, domin kuma ka kece tufafinka, ka kuma yi kuka a gabana, na ji ka, in ji Ubangiji.
Puisque ton cœur s'est ému, et que tu t'es humilié devant l'Éternel, lorsque tu as entendu ce que j'ai prononcé contre ce lieu et contre ses habitants, savoir, qu'ils seraient désolés et maudits; parce que tu as déchiré tes vêtements et que tu as pleuré devant moi, moi aussi j'ai entendu, dit l'Éternel.
20 Saboda haka zan haɗa ka da kakanninka, za a kuma binne ka cikin salama. Idanunka kuma ba za su ga dukan wannan masifan da zan jawo wa wurin nan ba.’” Sai suka kai wa sarki abin da ta faɗa.
C'est pourquoi, voici, je vais te retirer avec tes pères, tu seras recueilli en paix dans tes tombeaux, et tes yeux ne verront point tout ce mal que je vais faire venir sur ce lieu. Et ils rapportèrent ces choses au roi.

< 2 Sarakuna 22 >