< 2 Sarakuna 22 >

1 Yosiya yana da shekara takwas sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekara talatin da ɗaya a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Yedida’yar Adahiya; mutuniyar Bozkat.
Josias était âgé de huit ans quand il commença à régner, et il régna trente et un ans à Jérusalem; sa mère avait nom Jédida, fille de Hadaja de Botskath.
2 Ya aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji ya kuma bi dukan gurbin kakansa Dawuda, bai bauɗe hagu ko dama ba.
Il fit ce qui est droit devant l'Eternel, et marcha dans toute la voie de David son père, et ne s'en détourna ni à droite ni à gauche.
3 A shekara ta goma sha takwas ta mulkinsa, Sarki Yosiya ya aiki Shafan ɗan Azaliya, ɗan Meshullam, magatakarda, zuwa haikalin Ubangiji. Ya ce,
Or il arriva la dix-huitième année du Roi Josias, que le Roi envoya dans la maison de l'Eternel, Saphan, fils d'Atsalia, fils de Mésullam, le Secrétaire, en lui disant:
4 “Ka haura zuwa wurin Hilkiya babban firist ka sa yă shirya kuɗin da aka kawo a haikalin Ubangiji, wanda masu tsaron ƙofa suka tara daga mutane.
Monte vers Hilkija le grand Sacrificateur, et dis-lui de lever la somme de l'argent qu'on apporte dans la maison de l'Eternel, et que ceux qui gardent les vaisseaux ont recueilli du peuple.
5 Ka sa su danƙa su a hannun waɗanda aka zaɓa don biyan ma’aikatan da suka yi gyara a haikalin Ubangiji,
Et qu'on le délivre entre les mains de ceux qui ont la charge de l'œuvre, et qui sont commis sur la maison de l'Eternel, qu'on le délivre, dis-je, à ceux qui ont la charge de l'œuvre qui se fait dans la maison de l'Eternel, pour réparer ce qui est à réparer au Temple;
6 wato, kafintoci, da magina, da masu tsara gini. Ka kuma sa su sayi katakai da sassaƙaƙƙun duwatsu don a gyara haikalin.
[Savoir] aux charpentiers, aux architectes, et aux maçons, et afin d'acheter du bois et des pierres de taille pour réparer le Temple.
7 Amma ba sa bukata su ba da bayanin kuɗin da aka danƙa musu domin suna aikinsu da aminci.”
Mais qu'on ne leur fasse pas rendre compte de l'argent qu'on leur délivre entre les mains, parce qu'ils s'y portent fidèlement.
8 Hilkiya babban firist ya ce wa Shafan magatakarda, “Na sami Littafin Doka a haikalin Ubangiji.” Sai ya ba wa Shafan, shi kuma ya karanta.
Alors Hilkija le grand Sacrificateur, dit à Saphan le Secrétaire: J'ai trouvé le Livre de la Loi dans la maison de l'Eternel; et Hilkija donna ce livre à Saphan, qui le lut.
9 Sa’an nan Shafan ya koma wurin sarki ya ce masa, “Hafsoshinka sun kwashe kuɗin da suke a haikalin Ubangiji, suka ba wa masu aiki da masu lura da haikalin.”
Et Saphan le Secrétaire s'en vint au Roi, et rapporta la chose au Roi, et dit: Tes serviteurs ont amassé l'argent qui a été trouvé dans le Temple, et l'ont délivré entre les mains de ceux qui ont la charge de l'œuvre, [et] qui sont commis sur la maison de l'Eternel.
10 Sa’an nan Shafan magatakarda ya ce wa sarki, “Hilkiya firist ya ba ni wani littafi.” Sai Shafan ya karanta shi a gaban sarki.
Saphan le secrétaire fit aussi entendre au Roi, en disant: Hilkija le Sacrificateur m'a donné un Livre; et Saphan le lut devant le Roi.
11 Da sarki ya ji kalmomin Littafin Doka, sai ya kece tufafinsa.
Et il arriva qu'aussitôt que le Roi eut entendu les paroles du Livre de la Loi, il déchira ses vêtements.
12 Ya ba da waɗannan umarnai ga Hilkiya firist, da Ahikam ɗan Shafan, da Akbor ɗan Mikahiya, da Shafan magatakarda, da kuma Asahiya mai hidimar sarki, ya ce,
Et il commanda au Sacrificateur Hilkija, et à Ahikam fils de Saphan, et à Hacbor fils de Micaja, et à Saphan le Secrétaire, et à Hasaja serviteur du Roi, en disant:
13 “Ku je, ku nemi nufin Ubangiji saboda ni da saboda jama’a da kuma saboda dukan Yahuda game da abin da wannan littafi da aka samo ya ƙunsa. Fushin Ubangiji mai girma ne a kanmu domin kakanninmu ba su kiyaye kalmomin littafin nan ba; ba su aikata bisa ga abin da yake a rubuce game da mu ba.”
Allez, consultez l'Eternel pour moi, et pour le peuple, et pour tout Juda, touchant les paroles de ce Livre qui a été trouvé; car la colère de l'Eternel qui s'est allumée contre nous, est grande, parce que nos pères n'ont point obéi aux paroles de ce Livre, pour faire tout ce qui nous y est prescrit.
14 Sai Hilkiya firist, da Ahikam, Akbor, da Shafan, da kuma Asahiya suka je don su yi magana da annabiya Hulda, matan Shallum ɗan Tikba, ɗan Harhas, mai ajiyar tufafi. Tana zama a Urushalima, a Yanki na Biyu.
Hilkija donc le Sacrificateur, et Ahikam, et Hacbor, et Saphan, et Hasaja s'en allèrent vers Hulda la prophétesse, femme de Sallum fils de Tikva, fils de Harhas, gardien des vêtements, laquelle demeurait à Jérusalem au collège, et ils parlèrent avec elle.
15 Sai ta ce musu, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ku faɗa wa mutumin da ya aike ku wurina,
Et elle leur répondit: Ainsi a dit l'Eternel le Dieu d'Israël: Dites à l'homme qui vous a envoyés vers moi;
16 ‘Ga abin da Ubangiji ya ce, zan kawo masifa wa wannan wuri da kuma wa kan mutanen wurin, bisa ga dukan abubuwan da suke a rubuce a cikin littafin da sarkin Yahuda ya karanta.
Ainsi a dit l'Eternel: Voici je m'en vais faire venir du mal sur ce lieu-ci, et sur ses habitants, selon toutes les paroles du Livre que le Roi de Juda a lu;
17 Domin sun yashe ni suka ƙona turare wa waɗansu alloli, suka tozarta ni da dukan gumakan da hannuwansu suka sassaƙa, fushina zai yi ƙuna a kan wannan wuri, ba kuwa zai huce ba.’
Parce qu'ils m'ont abandonné, et qu'ils ont fait des encensements aux autres dieux, pour m'irriter par toutes les actions de leurs mains, ma colère s'est allumée contre ce lieu, et elle ne sera point éteinte.
18 Ku faɗa wa sarkin Yahuda, wanda ya aike ku ku nemi nufin Ubangiji, ‘Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yana cewa game da kalmomin da ka ji.
Mais quant au Roi de Juda qui vous a envoyés pour consulter l'Eternel; vous lui direz: Ainsi a dit l'Eternel le Dieu d'Israël, touchant les paroles que tu as entendues;
19 Domin zuciyarka mai tuba ce, ka kuma ƙasƙantar da kanka a gaban Ubangiji sa’ad da ka ji abin da na faɗa game da wannan wuri da mutanen wurin, cewa za su zama la’antattu da kuma kango, domin kuma ka kece tufafinka, ka kuma yi kuka a gabana, na ji ka, in ji Ubangiji.
Parce que ton cœur s'est amolli, et que tu t'es humilié devant l'Eternel, quand tu as entendu ce que j'ai prononcé contre ce lieu-ci, et contre ses habitants, qu'ils seraient en désolation et en malédiction, parce que tu as déchiré tes vêtements, et que tu as pleuré devant moi, je t'ai exaucé, dit l'Eternel.
20 Saboda haka zan haɗa ka da kakanninka, za a kuma binne ka cikin salama. Idanunka kuma ba za su ga dukan wannan masifan da zan jawo wa wurin nan ba.’” Sai suka kai wa sarki abin da ta faɗa.
C'est pourquoi voici, je vais te retirer avec tes pères, et tu seras retiré dans tes sépulcres en paix, et tes yeux ne verront point tout ce mal que je m'en vais faire venir sur ce lieu. Et ils rapportèrent toutes ces choses au Roi.

< 2 Sarakuna 22 >