< 2 Sarakuna 22 >
1 Yosiya yana da shekara takwas sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekara talatin da ɗaya a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Yedida’yar Adahiya; mutuniyar Bozkat.
Josias avait huit ans lorsqu'il devint roi, et il régna trente et un ans à Jérusalem. Le nom de sa mère était Jedida, fille d'Adaja, de Bozkath.
2 Ya aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji ya kuma bi dukan gurbin kakansa Dawuda, bai bauɗe hagu ko dama ba.
Il fit ce qui est droit aux yeux de l'Éternel, il marcha dans toute la voie de David, son père, et ne se détourna ni à droite ni à gauche.
3 A shekara ta goma sha takwas ta mulkinsa, Sarki Yosiya ya aiki Shafan ɗan Azaliya, ɗan Meshullam, magatakarda, zuwa haikalin Ubangiji. Ya ce,
La dix-huitième année du roi Josias, le roi envoya Shaphan, fils d'Azalia, fils de Meshullam, le scribe, à la maison de l'Éternel, en disant:
4 “Ka haura zuwa wurin Hilkiya babban firist ka sa yă shirya kuɗin da aka kawo a haikalin Ubangiji, wanda masu tsaron ƙofa suka tara daga mutane.
« Monte vers Hilkija, le grand prêtre, pour qu'il compte l'argent qu'on apporte à la maison de l'Éternel et que les gardiens du seuil ont recueilli du peuple.
5 Ka sa su danƙa su a hannun waɗanda aka zaɓa don biyan ma’aikatan da suka yi gyara a haikalin Ubangiji,
Qu'ils le remettent entre les mains des ouvriers qui ont la garde de la maison de l'Éternel, et qu'ils le donnent aux ouvriers de la maison de l'Éternel, pour réparer les dégâts de la maison,
6 wato, kafintoci, da magina, da masu tsara gini. Ka kuma sa su sayi katakai da sassaƙaƙƙun duwatsu don a gyara haikalin.
aux charpentiers, aux constructeurs et aux maçons, et pour acheter du bois et des pierres de taille pour réparer la maison.
7 Amma ba sa bukata su ba da bayanin kuɗin da aka danƙa musu domin suna aikinsu da aminci.”
Mais on ne leur demandera pas de compte pour l'argent remis entre leurs mains, car ils agissent fidèlement. »
8 Hilkiya babban firist ya ce wa Shafan magatakarda, “Na sami Littafin Doka a haikalin Ubangiji.” Sai ya ba wa Shafan, shi kuma ya karanta.
Hilkija, le grand prêtre, dit à Shaphan, le scribe: « J'ai trouvé le livre de la loi dans la maison de Yahvé. » Hilkija remit le livre à Shaphan, qui le lut.
9 Sa’an nan Shafan ya koma wurin sarki ya ce masa, “Hafsoshinka sun kwashe kuɗin da suke a haikalin Ubangiji, suka ba wa masu aiki da masu lura da haikalin.”
Shaphan, le scribe, revint vers le roi et lui rapporta la parole, en disant: « Tes serviteurs ont vidé l'argent qui se trouvait dans la maison et l'ont remis entre les mains des ouvriers chargés de la surveillance de la maison de l'Éternel. »
10 Sa’an nan Shafan magatakarda ya ce wa sarki, “Hilkiya firist ya ba ni wani littafi.” Sai Shafan ya karanta shi a gaban sarki.
Shaphan, le scribe, informa le roi en disant: « Le prêtre Hilkija m'a remis un livre. » Puis Shaphan le lut devant le roi.
11 Da sarki ya ji kalmomin Littafin Doka, sai ya kece tufafinsa.
Lorsque le roi eut entendu les paroles du livre de la loi, il déchira ses vêtements.
12 Ya ba da waɗannan umarnai ga Hilkiya firist, da Ahikam ɗan Shafan, da Akbor ɗan Mikahiya, da Shafan magatakarda, da kuma Asahiya mai hidimar sarki, ya ce,
Le roi donna cet ordre au sacrificateur Hilkija, à Ahikam, fils de Schaphan, à Acbor, fils de Michée, à Schaphan, le scribe, et à Asaja, serviteur du roi:
13 “Ku je, ku nemi nufin Ubangiji saboda ni da saboda jama’a da kuma saboda dukan Yahuda game da abin da wannan littafi da aka samo ya ƙunsa. Fushin Ubangiji mai girma ne a kanmu domin kakanninmu ba su kiyaye kalmomin littafin nan ba; ba su aikata bisa ga abin da yake a rubuce game da mu ba.”
« Allez consulter Yahvé pour moi, pour le peuple et pour tout Juda, au sujet des paroles de ce livre qui a été trouvé; Car la colère de Yahvé s'est enflammée contre nous, parce que nos pères n'ont pas écouté les paroles de ce livre et n'ont pas agi selon tout ce qui est écrit à notre sujet. »
14 Sai Hilkiya firist, da Ahikam, Akbor, da Shafan, da kuma Asahiya suka je don su yi magana da annabiya Hulda, matan Shallum ɗan Tikba, ɗan Harhas, mai ajiyar tufafi. Tana zama a Urushalima, a Yanki na Biyu.
Et Hilkija, le prêtre, Ahikam, Acbor, Shaphan et Asaiah allèrent chez Hulda, la prophétesse, femme de Shallum, fils de Tikva, fils de Harhas, gardien de l'armoire (elle habitait maintenant à Jérusalem, dans le deuxième quartier), et ils lui parlèrent.
15 Sai ta ce musu, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ku faɗa wa mutumin da ya aike ku wurina,
Elle leur dit: « L'Éternel, le Dieu d'Israël, dit: 'Dis à l'homme qui t'envoie vers moi:
16 ‘Ga abin da Ubangiji ya ce, zan kawo masifa wa wannan wuri da kuma wa kan mutanen wurin, bisa ga dukan abubuwan da suke a rubuce a cikin littafin da sarkin Yahuda ya karanta.
L'Éternel dit: 'Voici, je vais faire venir le malheur sur ce lieu et sur ses habitants, toutes les paroles du livre que le roi de Juda a lu.
17 Domin sun yashe ni suka ƙona turare wa waɗansu alloli, suka tozarta ni da dukan gumakan da hannuwansu suka sassaƙa, fushina zai yi ƙuna a kan wannan wuri, ba kuwa zai huce ba.’
Parce qu'ils m'ont abandonné et qu'ils ont offert de l'encens à d'autres dieux, afin de m'irriter par tout l'ouvrage de leurs mains, ma colère s'enflammera contre ce lieu, et elle ne s'éteindra pas. »
18 Ku faɗa wa sarkin Yahuda, wanda ya aike ku ku nemi nufin Ubangiji, ‘Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yana cewa game da kalmomin da ka ji.
Mais dis au roi de Juda, qui t'a envoyé consulter Yahvé: « Yahvé, le Dieu d'Israël, dit: 'Au sujet des paroles que tu as entendues,
19 Domin zuciyarka mai tuba ce, ka kuma ƙasƙantar da kanka a gaban Ubangiji sa’ad da ka ji abin da na faɗa game da wannan wuri da mutanen wurin, cewa za su zama la’antattu da kuma kango, domin kuma ka kece tufafinka, ka kuma yi kuka a gabana, na ji ka, in ji Ubangiji.
parce que ton cœur s'est attendri et que tu t'es humilié devant Yahvé en entendant ce que j'ai dit de ce lieu et de ses habitants, pour qu'ils deviennent une désolation et une malédiction, et que tu as déchiré tes vêtements et pleuré devant moi, moi aussi je t'ai entendu, dit Yahvé.
20 Saboda haka zan haɗa ka da kakanninka, za a kuma binne ka cikin salama. Idanunka kuma ba za su ga dukan wannan masifan da zan jawo wa wurin nan ba.’” Sai suka kai wa sarki abin da ta faɗa.
C'est pourquoi voici que je vous rassemblerai auprès de vos pères, et vous serez rassemblés en paix dans votre tombeau. Vos yeux ne verront pas tout le mal que je ferai venir sur ce lieu.'"" Ils rapportèrent donc ce message au roi.