< 2 Sarakuna 22 >

1 Yosiya yana da shekara takwas sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekara talatin da ɗaya a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Yedida’yar Adahiya; mutuniyar Bozkat.
Josiah was eight years old when he became the king [of Judah]. He ruled from Jerusalem for 31 years. His mother was Jedidah and his grandfather was Adaiah from Bozkath [town].
2 Ya aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji ya kuma bi dukan gurbin kakansa Dawuda, bai bauɗe hagu ko dama ba.
Josiah did things that were pleasing to Yahweh and conducted his life as his ancestor King David had done. He completely obeyed [IDM] all the laws of God.
3 A shekara ta goma sha takwas ta mulkinsa, Sarki Yosiya ya aiki Shafan ɗan Azaliya, ɗan Meshullam, magatakarda, zuwa haikalin Ubangiji. Ya ce,
After Josiah had been ruling for almost 18 years, he sent his secretary Shaphan, the son of Azaliah and grandson of Meshullam, to the temple with these instructions:
4 “Ka haura zuwa wurin Hilkiya babban firist ka sa yă shirya kuɗin da aka kawo a haikalin Ubangiji, wanda masu tsaron ƙofa suka tara daga mutane.
“Go to Hilkiah, the Supreme Priest, and tell him to give me a report, telling me how much money the men who guard the doors of the temple have collected from the people [as offerings].
5 Ka sa su danƙa su a hannun waɗanda aka zaɓa don biyan ma’aikatan da suka yi gyara a haikalin Ubangiji,
Then tell him to give all that money to the men who are supervising the work of repairing the temple.
6 wato, kafintoci, da magina, da masu tsara gini. Ka kuma sa su sayi katakai da sassaƙaƙƙun duwatsu don a gyara haikalin.
They must give that money to the carpenters, the builders, and the masons, and they should also buy the timber and the stones that they will use to repair the temple.
7 Amma ba sa bukata su ba da bayanin kuɗin da aka danƙa musu domin suna aikinsu da aminci.”
But the men who supervise the work will not be required to make a report on the money that is given to them, saying what they spent it for, because those men are completely honest.”
8 Hilkiya babban firist ya ce wa Shafan magatakarda, “Na sami Littafin Doka a haikalin Ubangiji.” Sai ya ba wa Shafan, shi kuma ya karanta.
[After Shaphan said that to Hilkiah] the king’s secretary, Hilkiah said to Shaphan, “I have found in the temple a scroll on which is written the laws [that God gave to Moses]!” Hilkiah gave the scroll to Shaphan, and he started to read it.
9 Sa’an nan Shafan ya koma wurin sarki ya ce masa, “Hafsoshinka sun kwashe kuɗin da suke a haikalin Ubangiji, suka ba wa masu aiki da masu lura da haikalin.”
Then Shaphan [took the scroll] to the king and said to him, “Your temple guards have taken the money that was in the temple, and they have given it to the men who will supervise the work of repairing the temple.”
10 Sa’an nan Shafan magatakarda ya ce wa sarki, “Hilkiya firist ya ba ni wani littafi.” Sai Shafan ya karanta shi a gaban sarki.
Then Shaphan said to the king, [“I have brought to you] a scroll that Hilkiah gave to me.” And Shaphan started to read it to the king.
11 Da sarki ya ji kalmomin Littafin Doka, sai ya kece tufafinsa.
When the king heard the laws that were written in the scroll that Shaphan was reading to him, he tore his clothes [because he was very dismayed].
12 Ya ba da waɗannan umarnai ga Hilkiya firist, da Ahikam ɗan Shafan, da Akbor ɗan Mikahiya, da Shafan magatakarda, da kuma Asahiya mai hidimar sarki, ya ce,
Then he gave these instructions to Hilkiah, to Shaphan’s son Ahikam, to Micaiah’s son Achbor, and to Asaiah, the king’s special advisor:
13 “Ku je, ku nemi nufin Ubangiji saboda ni da saboda jama’a da kuma saboda dukan Yahuda game da abin da wannan littafi da aka samo ya ƙunsa. Fushin Ubangiji mai girma ne a kanmu domin kakanninmu ba su kiyaye kalmomin littafin nan ba; ba su aikata bisa ga abin da yake a rubuce game da mu ba.”
“Go and ask Yahweh for me and for all the people of Judah, about what is written in this scroll that has been found. Because [it is clear that] Yahweh is very angry with us because our ancestors disobeyed what was written on this scroll, things that we [should have done].”
14 Sai Hilkiya firist, da Ahikam, Akbor, da Shafan, da kuma Asahiya suka je don su yi magana da annabiya Hulda, matan Shallum ɗan Tikba, ɗan Harhas, mai ajiyar tufafi. Tana zama a Urushalima, a Yanki na Biyu.
So Hilkiah, Ahikam, Achbor, Shaphan, and Asaiah went to (consult/talk with) a woman whose name was Huldah, who was a prophetess who lived in the newer/northern part of Jerusalem. Her husband Shallum, son of Tikvah and grandson of Harhas, took care of the robes that were worn [in the temple] (OR, [by the king]). [Those five men told her about the scroll].
15 Sai ta ce musu, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ku faɗa wa mutumin da ya aike ku wurina,
She said to them, “This is what Yahweh the God whom we Israelis [worship] says: ‘Go back and tell the king who sent you
16 ‘Ga abin da Ubangiji ya ce, zan kawo masifa wa wannan wuri da kuma wa kan mutanen wurin, bisa ga dukan abubuwan da suke a rubuce a cikin littafin da sarkin Yahuda ya karanta.
that this is what Yahweh says: “Listen to this carefully. I am going to cause all the people who live here in Jerusalem to experience a disaster, which is what was written in the scroll that the king has read.
17 Domin sun yashe ni suka ƙona turare wa waɗansu alloli, suka tozarta ni da dukan gumakan da hannuwansu suka sassaƙa, fushina zai yi ƙuna a kan wannan wuri, ba kuwa zai huce ba.’
I will do that because they have abandoned me, and they burn incense to [honor] other gods. They have caused me to become very angry by [worshiping] the idols that they have made (OR, by all the wicked things that they have done), and my anger is like [MET] a fire that will not be put out.”
18 Ku faɗa wa sarkin Yahuda, wanda ya aike ku ku nemi nufin Ubangiji, ‘Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yana cewa game da kalmomin da ka ji.
The king of Judah sent you to inquire what I, Yahweh, wanted you to do, so this is what you should say to him: “Because you have heeded what was written in the scroll,
19 Domin zuciyarka mai tuba ce, ka kuma ƙasƙantar da kanka a gaban Ubangiji sa’ad da ka ji abin da na faɗa game da wannan wuri da mutanen wurin, cewa za su zama la’antattu da kuma kango, domin kuma ka kece tufafinka, ka kuma yi kuka a gabana, na ji ka, in ji Ubangiji.
and you repented and humbled yourself when you heard what I said to warn you [about what would happen to] this city and the people who live here and because you tore your robes and wept in my presence, I have heard you. I said that I would cause this city to be abandoned. It will be a city whose name people will use when they curse someone. But I have heard what you prayed,
20 Saboda haka zan haɗa ka da kakanninka, za a kuma binne ka cikin salama. Idanunka kuma ba za su ga dukan wannan masifan da zan jawo wa wurin nan ba.’” Sai suka kai wa sarki abin da ta faɗa.
so I will allow you to die [EUP] and be buried peacefully. I will cause the people who live here to experience a terrible disaster, but you will not [be alive to] see it.”’” After the men heard that, they returned to King Josiah and gave him that message.

< 2 Sarakuna 22 >