< 2 Sarakuna 22 >

1 Yosiya yana da shekara takwas sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekara talatin da ɗaya a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Yedida’yar Adahiya; mutuniyar Bozkat.
V osmi letech byl Joziáš, když počal kralovati, a kraloval jedno a třidceti let v Jeruzalémě. Jméno matky jeho bylo Jedida, dcera Adaiášova z Baskat.
2 Ya aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji ya kuma bi dukan gurbin kakansa Dawuda, bai bauɗe hagu ko dama ba.
Ten činil to, což pravého jest před očima Hospodinovýma, chodě po vší cestě Davida otce svého, a neuchyluje se na pravo ani na levo.
3 A shekara ta goma sha takwas ta mulkinsa, Sarki Yosiya ya aiki Shafan ɗan Azaliya, ɗan Meshullam, magatakarda, zuwa haikalin Ubangiji. Ya ce,
Stalo se pak osmnáctého léta krále Joziáše, že poslal král Safana syna Azaliášova, syna Mesullamova, písaře, do domu Hospodinova, řka:
4 “Ka haura zuwa wurin Hilkiya babban firist ka sa yă shirya kuɗin da aka kawo a haikalin Ubangiji, wanda masu tsaron ƙofa suka tara daga mutane.
Jdi k Helkiášovi knězi nejvyššímu, ať sečtou peníze, kteréž jsou vneseny do domu Hospodinova, kteréž sebrali strážní prahu od lidu.
5 Ka sa su danƙa su a hannun waɗanda aka zaɓa don biyan ma’aikatan da suka yi gyara a haikalin Ubangiji,
A ať je dadí v ruce řemeslníků představených nad dílem domu Hospodinova, aby je obraceli na dělníky, kteříž dělají dílo v domě Hospodinově, k opravení zbořenin domu,
6 wato, kafintoci, da magina, da masu tsara gini. Ka kuma sa su sayi katakai da sassaƙaƙƙun duwatsu don a gyara haikalin.
Totiž na tesaře a stavitele a zedníky, též aby jednali dříví a tesané kamení k opravování domu.
7 Amma ba sa bukata su ba da bayanin kuɗin da aka danƙa musu domin suna aikinsu da aminci.”
A však ať počtu nečiní z peněz, kteréž se dávají v ruce jejich; nebo věrně dělati budou.
8 Hilkiya babban firist ya ce wa Shafan magatakarda, “Na sami Littafin Doka a haikalin Ubangiji.” Sai ya ba wa Shafan, shi kuma ya karanta.
I řekl Helkiáš kněz nejvyšší Safanovi písaři: Knihu zákona nalezl jsem v domě Hospodinově. I dal Helkiáš knihu tu Safanovi, kterýž četl v ní.
9 Sa’an nan Shafan ya koma wurin sarki ya ce masa, “Hafsoshinka sun kwashe kuɗin da suke a haikalin Ubangiji, suka ba wa masu aiki da masu lura da haikalin.”
Přišel pak Safan písař k králi, a oznamuje králi tu věc, řekl: Sebrali služebníci tvoji peníze, kteréž se nalezly v domě Páně, a dali je v ruce řemeslníků představených nad dílem domu Hospodinova.
10 Sa’an nan Shafan magatakarda ya ce wa sarki, “Hilkiya firist ya ba ni wani littafi.” Sai Shafan ya karanta shi a gaban sarki.
Oznámil také Safan písař králi, řka: Knihu mi dal Helkiáš kněz. I četl ji Safan před králem.
11 Da sarki ya ji kalmomin Littafin Doka, sai ya kece tufafinsa.
A když slyšel král slova knihy zákona, roztrhl roucho své.
12 Ya ba da waɗannan umarnai ga Hilkiya firist, da Ahikam ɗan Shafan, da Akbor ɗan Mikahiya, da Shafan magatakarda, da kuma Asahiya mai hidimar sarki, ya ce,
A rozkázal král Helkiášovi knězi, a Achikamovi synu Safanovu, a Achborovi synu Michaia, a Safanovi písaři, a Asaiášovi služebníku královskému, řka:
13 “Ku je, ku nemi nufin Ubangiji saboda ni da saboda jama’a da kuma saboda dukan Yahuda game da abin da wannan littafi da aka samo ya ƙunsa. Fushin Ubangiji mai girma ne a kanmu domin kakanninmu ba su kiyaye kalmomin littafin nan ba; ba su aikata bisa ga abin da yake a rubuce game da mu ba.”
Jděte, poraďte se s Hospodinem o mne i o lid, a o všeho Judu z strany slov knihy této, kteráž jest nalezena; nebo veliký jest hněv Hospodinův, kterýž rozpálen jest proti nám, proto že otcové naši neposlouchali slov knihy této, aby činili všecko tak, jakž jest nám zapsáno.
14 Sai Hilkiya firist, da Ahikam, Akbor, da Shafan, da kuma Asahiya suka je don su yi magana da annabiya Hulda, matan Shallum ɗan Tikba, ɗan Harhas, mai ajiyar tufafi. Tana zama a Urushalima, a Yanki na Biyu.
Tedy šli Helkiáš kněz a Achikam, a Achbor, a Safan a Asaia k Chuldě prorokyni, manželce Salluma, syna Tekue, syna Charchas, strážného nad rouchem; nebo bydlila v Jeruzalémě na druhé straně. A mluvili s ní.
15 Sai ta ce musu, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ku faɗa wa mutumin da ya aike ku wurina,
Kteráž řekla jim: Toto praví Hospodin Bůh Izraelský: Povězte muži, kterýž vás poslal ke mně:
16 ‘Ga abin da Ubangiji ya ce, zan kawo masifa wa wannan wuri da kuma wa kan mutanen wurin, bisa ga dukan abubuwan da suke a rubuce a cikin littafin da sarkin Yahuda ya karanta.
Takto praví Hospodin: Aj, já uvedu zlé věci na místo toto a na obyvatele jeho, všecka slova knihy té, kterouž četl král Judský,
17 Domin sun yashe ni suka ƙona turare wa waɗansu alloli, suka tozarta ni da dukan gumakan da hannuwansu suka sassaƙa, fushina zai yi ƙuna a kan wannan wuri, ba kuwa zai huce ba.’
Proto že mne opustili a kadili bohům cizím, aby mne popouzeli všelikým dílem rukou svých. Z té příčiny rozpálila se prchlivost má na místo toto, aniž bude uhašena.
18 Ku faɗa wa sarkin Yahuda, wanda ya aike ku ku nemi nufin Ubangiji, ‘Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yana cewa game da kalmomin da ka ji.
Králi pak Judskému, kterýž vás poslal, abyste se tázali Hospodina, takto povíte: Toto praví Hospodin Bůh Izraelský o slovích těch, kteráž jsi slyšel:
19 Domin zuciyarka mai tuba ce, ka kuma ƙasƙantar da kanka a gaban Ubangiji sa’ad da ka ji abin da na faɗa game da wannan wuri da mutanen wurin, cewa za su zama la’antattu da kuma kango, domin kuma ka kece tufafinka, ka kuma yi kuka a gabana, na ji ka, in ji Ubangiji.
Poněvadž obměkčeno jest srdce tvé, a ponížils se před tváří Hospodinovou, když jsi slyšel, které věci jsem mluvil proti místu tomuto, a proti obyvatelům jeho, že má přijíti v zpuštění a v zlořečení, a roztrhl jsi roucho své, a plakals přede mnou, i já také uslyšel jsem tě, praví Hospodin.
20 Saboda haka zan haɗa ka da kakanninka, za a kuma binne ka cikin salama. Idanunka kuma ba za su ga dukan wannan masifan da zan jawo wa wurin nan ba.’” Sai suka kai wa sarki abin da ta faɗa.
Protož, aj, já připojím tě k otcům tvým, a pochován budeš v hrobích svých v pokoji, aby neviděly oči tvé ničeho z toho zlého, kteréž přivedu na místo toto. I oznámili králi tu řeč.

< 2 Sarakuna 22 >