< 2 Sarakuna 21 >

1 Manasse yana da shekara goma sha biyu sa’ad da ya zama sarki, ya yi mulki shekara hamsin da biyar a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Hefziba.
Manasés tenía doce años cuando comenzó a reinar; por cincuenta y cinco años estuvo gobernando en Jerusalén; y el nombre de su madre era Hepsiba.
2 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, ya bi munanan al’adun al’umman da Ubangiji ya kora a gaban Isra’ilawa.
E hizo lo malo ante los ojos del Señor, copiando los caminos repugnantes de aquellas naciones que el Señor había arrojado de delante de los hijos de Israel.
3 Ya sāke gina masujadan da mahaifinsa Hezekiya ya rurrushe. Ya kuma gina wa Ba’al bagadai. Ya kafa ginshiƙin Ashera kamar yadda Ahab sarkin Isra’ila ya yi. Ya durƙusa wa dukan rundunan taurari ya yi musu sujada.
Volvió a levantar los lugares altos que habían sido derribados por Ezequías su padre; hizo altares para Baal, de Asera, como Acab, rey de Israel, había hecho; Él adoró y rindió culto al ejército de estrellas del cielo.
4 Ya gina bagadai a haikalin Ubangiji, wurin da Ubangiji ya ce, “A Urushalima ne zan sa Sunana.”
Y puso altares en la casa del Señor, de lo cual el Señor había dicho: En Jerusalén pondré mi nombre.
5 Cikin filaye biyu na haikalin Ubangiji kuwa, ya gina bagadai na dukan rundunan taurari.
E instaló altares para todas las estrellas del cielo en los dos cuadrados exteriores de la casa del Señor.
6 Ya miƙa ɗansa hadaya ta ƙonawa, ya yi sihiri da tsubu, ya tuntuɓi masu duba da masu ruhohi. Ya aikata mugunta ƙwarai a gaban Ubangiji, ya sa Ubangiji ya yi fushi.
E hizo pasar a su hijo por el fuego, práctico la invocación de espíritus y la adivinación, estableció el espiritismo y la hechicería; hizo mucho mal ante los ojos del Señor, provocándolo a la ira.
7 Ya ɗauki siffar ginshiƙin Asherar da ya yi, ya sa a haikalin da Ubangiji ya ce wa Dawuda da ɗansa Solomon, “A cikin wannan haikali, da kuma cikin Urushalima inda na zaɓa daga kabilan Isra’ila, zan sa Sunana har abada.
Puso la imagen de Asera que había hecho en la casa que el Señor había dicho a David y a su hijo Salomón, en esta casa y en Jerusalén, el pueblo que he hecho mío. Las tribus de Israel, pondré mi nombre para siempre.
8 Ba zan ƙara sa Isra’ilawa su fita daga ƙasar da na ba kakanninsu ba, idan dai za su kula su aikata dukan abin da na umarce su, su kuma kiyaye dukan dokokin da na ba wa bawana Musa yă umarce su.”
Y nunca más enviaré los pies de Israel vagando por la tierra que di a sus padres; si solo se ocuparan de cumplir todas mis órdenes, y de guardar toda la ley que les dio mi siervo Moisés.
9 Amma mutanen ba su kasa kunne ba. Manasse ya ɓad da su, har suka yi muguntar da ta fi ta al’umman da Ubangiji ya hallaka a gaban Isra’ilawa.
Pero no oyeron; y Manasés les hizo hacer más mal que aquellas naciones, a quienes el Señor entregó a la destrucción delante de los hijos de Israel.
10 Ubangiji ya yi magana ta bakin bayinsa annabawa,
Y él Señor dijo, a través de sus siervos los profetas:
11 “Manasse, sarkin Yahuda ya aikata waɗannan ƙazantattun zunubai. Ya aikata mugunta fiye da ta Amoriyawan da suka riga shi, ya kuma sa Yahuda ta bauɗe ta wurin yin zunubi saboda gumakansa.
Porque Manasés, rey de Judá, ha hecho estas cosas repugnantes, haciendo más mal que todos los amorreos antes que él, y haciendo que Judá haga mal con sus dioses falsos,
12 Saboda haka ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, zan jawo wa Urushalima da kuma Yahuda masifar da duk kunnen da ya ji, sai ya kusa suma.
Por esta causa, dice el Señor, el Dios de Israel, enviaré tal maldad sobre Jerusalén y Judá, que los oídos le dolerán a todos a quienes lleguen las noticias.
13 Zan auna Urushalima da ma’aunin da na yi amfani da shi a kan Samariya, zan kuma yi amfani da magwajin da na yi amfani da shi a kan gidan Ahab. Zan shafe Urushalima yadda mutum yake wanke kwano yă kife.
Y sobre Jerusalén será medida con la misma medida que a Samaria y la simiente de Acab; Jerusalén se lavará limpiamente como se lava un plato y se voltea sobre su cara.
14 Zan rabu da ragowar gādona, in kuma miƙa su ga maƙiyansu. Abokan gābansu za su washe suka kuma kwashi ganima daga gare su,
Y apartaré de mí el resto de mi herencia, y los entregaré en manos de sus enemigos, que tomarán sus bienes y sus bienes para sí mismos;
15 domin sun aikata mugunta a idanuna, suka kuma tsokane ni tun daga ranar da kakanninsu suka fito daga Masar, har yă zuwa yau.”
Porque han hecho lo malo ante mis ojos, llevándome a la ira, desde el día en que sus padres salieron de Egipto hasta el día de hoy.
16 Ban da haka ma, Manasse ya zub da jinin marasa laifi har ya cika Urushalima daga wannan ɓangare zuwa wancan, ban da zunubin da ya sa Yahuda ta aikata, ta haka suka yi mugunta a gaban Ubangiji.
Más que esto, Manasés tomó la vida de hombres rectos, hasta que Jerusalén, de un extremo a otro, estaba llena de sangre; además de su pecado al hacer que Judá hiciera el mal a los ojos del Señor.
17 Game da sauran ayyukan mulkin Manasse, da duk abin da ya yi, har da zunubin da ya aikata, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
Los demás hechos de Manasés, y todo lo que hizo, y sus pecados, ¿no están registrados en el libro de las crónicas de los reyes de Judá?
18 Manasse ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a lambun fadansa, lambun Uzza. Sai Amon ɗansa ya gāje shi.
Manasés durmió con sus padres, y fue enterrado en el jardín de su palacio, en el jardín de Uza; y Amón su hijo se convirtió en rey en su lugar.
19 Amon yana da shekara ashirin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya yi mulki shekara biyu a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Meshullemet’yar Haruz; ita mutuniyar Yotba ce.
Amón tenía veintidós años cuando se convirtió en rey, gobernando en Jerusalén durante dos años; el nombre de su madre era Mesulemet, la hija de Haruz de Jotba.
20 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, yadda Manasse mahaifinsa ya yi.
Él hizo lo malo ante los ojos del Señor, como había hecho Manasés su padre.
21 Ya bi duk gurbin mahaifinsa a kome, ya yi sujada ga gumakan da mahaifinsa ya yi wa, ya kuma durƙusa musu.
Recorrió todos los caminos de su padre, sirviendo y adorando a los dioses falsos de los que su padre había sido servidor;
22 Ya rabu da Ubangiji Allah na kakanninsa, bai kuwa yi tafiya a hanyar Ubangiji ba.
Alejándose del Señor, el Dios de sus padres, y no andando en sus caminos.
23 Fadawan Amon suka ƙulla maƙarƙashiya suka kashe shi a cikin fadarsa.
Y los criados de Amón conspiraron contra él, y mataron al rey en su casa.
24 Sai mutanen ƙasar suka kashe duk waɗanda suka ƙulla wa Sarki Amon maƙarƙashiya, sa’an nan suka naɗa ɗansa sarki a maimakonsa.
Pero él pueblo de la tierra mató a todos los que habían participado en el plan contra el rey, e hicieron rey a Josías su hijo en su lugar.
25 Game da sauran ayyukan mulkin Amon, da abubuwan da ya aikata, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
Ahora, el resto de los actos que hizo Amón, ¿no están registrados en el libro de las crónicas de los reyes de Judá?
26 Aka binne shi a kabarinsa a lambun Uzza. Yosiya ɗansa kuma ya gāje shi.
Lo enterraron en pusieron en el jardín de Uza, y Josías su hijo se convirtió en rey en su lugar.

< 2 Sarakuna 21 >