< 2 Sarakuna 21 >

1 Manasse yana da shekara goma sha biyu sa’ad da ya zama sarki, ya yi mulki shekara hamsin da biyar a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Hefziba.
Manasés tenía doce años cuando se convirtió en rey, y reinó en Jerusalén durante cincuenta y cinco años. El nombre de su madre era Hefzibá.
2 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, ya bi munanan al’adun al’umman da Ubangiji ya kora a gaban Isra’ilawa.
Sus hechos fueron malos a los ojos del Señor, al seguir las repugnantes prácticas paganas de las naciones que el Señor había expulsado ante los israelitas.
3 Ya sāke gina masujadan da mahaifinsa Hezekiya ya rurrushe. Ya kuma gina wa Ba’al bagadai. Ya kafa ginshiƙin Ashera kamar yadda Ahab sarkin Isra’ila ya yi. Ya durƙusa wa dukan rundunan taurari ya yi musu sujada.
Reconstruyó los lugares altos que su padre Ezequías había destruido, y levantó altares para Baal. Hizo un poste de ídolos de Asera, tal como lo había hecho Acab, rey de Israel, y adoró y sirvió al sol, la luna y las estrellas.
4 Ya gina bagadai a haikalin Ubangiji, wurin da Ubangiji ya ce, “A Urushalima ne zan sa Sunana.”
Levantó altares paganos en el Templo del Señor, justo donde el Señor había dicho: “Pondré mi nombre en Jerusalén para siempre”.
5 Cikin filaye biyu na haikalin Ubangiji kuwa, ya gina bagadai na dukan rundunan taurari.
Erigió altares para adorar al sol, la luna y las estrellas en los dos patios del Templo del Señor.
6 Ya miƙa ɗansa hadaya ta ƙonawa, ya yi sihiri da tsubu, ya tuntuɓi masu duba da masu ruhohi. Ya aikata mugunta ƙwarai a gaban Ubangiji, ya sa Ubangiji ya yi fushi.
Incluso sacrificó a su propio hijo como holocausto, y utilizó la adivinación y la brujería, y trató con médiums y espiritistas. Hizo mucho mal a los ojos del Señor, haciendo que éste se enojara.
7 Ya ɗauki siffar ginshiƙin Asherar da ya yi, ya sa a haikalin da Ubangiji ya ce wa Dawuda da ɗansa Solomon, “A cikin wannan haikali, da kuma cikin Urushalima inda na zaɓa daga kabilan Isra’ila, zan sa Sunana har abada.
Tomó el poste del ídolo de Asera que había hecho y lo colocó en el Templo. Este era el lugar al que se refería el Señor cuando les dijo a David y a Salomón, su hijo: “En este Templo y en Jerusalén, que he elegido entre todas las tribus de Israel, pondré mi nombre para siempre.
8 Ba zan ƙara sa Isra’ilawa su fita daga ƙasar da na ba kakanninsu ba, idan dai za su kula su aikata dukan abin da na umarce su, su kuma kiyaye dukan dokokin da na ba wa bawana Musa yă umarce su.”
Nunca más haré que los israelitas se alejen de la tierra que les di a sus antepasados si tienen cuidado de seguir todo lo que les he ordenado: toda la ley que les dio mi siervo Moisés”.
9 Amma mutanen ba su kasa kunne ba. Manasse ya ɓad da su, har suka yi muguntar da ta fi ta al’umman da Ubangiji ya hallaka a gaban Isra’ilawa.
El pueblo se negó a escuchar y Manasés los llevó a pecar, de modo que el mal que hicieron fue aún peor que el de las naciones que el Señor había destruido antes de los israelitas.
10 Ubangiji ya yi magana ta bakin bayinsa annabawa,
El Señor dijo por medio de sus siervos los profetas
11 “Manasse, sarkin Yahuda ya aikata waɗannan ƙazantattun zunubai. Ya aikata mugunta fiye da ta Amoriyawan da suka riga shi, ya kuma sa Yahuda ta bauɗe ta wurin yin zunubi saboda gumakansa.
“Puesto que Manasés, rey de Judá, ha cometido todos estos repugnantes pecados, haciendo cosas aún más malas que los amorreos que vivieron antes que él, y con su fomento del culto a los ídolos ha hecho pecar a Judá,
12 Saboda haka ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, zan jawo wa Urushalima da kuma Yahuda masifar da duk kunnen da ya ji, sai ya kusa suma.
esto es lo que dice el Señor, el Dios de Israel: ¡Cuidado! Voy a hacer caer sobre Jerusalén y Judá un desastre tal que hará zumbar los oídos de todo el que lo oiga.
13 Zan auna Urushalima da ma’aunin da na yi amfani da shi a kan Samariya, zan kuma yi amfani da magwajin da na yi amfani da shi a kan gidan Ahab. Zan shafe Urushalima yadda mutum yake wanke kwano yă kife.
Extenderé sobre Jerusalén el cordel de medir usado contra Samaria y la plomada usada contra la casa de Acab, y limpiaré a Jerusalén como se limpia un cuenco, limpiándolo y dándole la vuelta.
14 Zan rabu da ragowar gādona, in kuma miƙa su ga maƙiyansu. Abokan gābansu za su washe suka kuma kwashi ganima daga gare su,
Abandonaré al resto de mi pueblo especial y lo entregaré a sus enemigos. Serán despojo y botín para todos sus enemigos,
15 domin sun aikata mugunta a idanuna, suka kuma tsokane ni tun daga ranar da kakanninsu suka fito daga Masar, har yă zuwa yau.”
porque han hecho lo que es malo a mis ojos y me han hecho enojar desde el día en que sus padres salieron de Egipto hasta hoy”.
16 Ban da haka ma, Manasse ya zub da jinin marasa laifi har ya cika Urushalima daga wannan ɓangare zuwa wancan, ban da zunubin da ya sa Yahuda ta aikata, ta haka suka yi mugunta a gaban Ubangiji.
Además, Manasés asesinó a tantos inocentes que Jerusalén se llenó de un lado a otro con su sangre. Esto se sumaba al pecado que había hecho cometer a Judá, haciendo el mal a los ojos del Señor.
17 Game da sauran ayyukan mulkin Manasse, da duk abin da ya yi, har da zunubin da ya aikata, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
El resto de lo que sucedió en el reinado de Manasés, todo lo que hizo, así como los pecados que cometió, están registrados en el Libro de las Crónicas de los Reyes de Judá.
18 Manasse ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a lambun fadansa, lambun Uzza. Sai Amon ɗansa ya gāje shi.
Manasés murió y fue enterrado en el jardín de su palacio, el jardín de Uzza. Su hijo Amón le sucedió como rey.
19 Amon yana da shekara ashirin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya yi mulki shekara biyu a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Meshullemet’yar Haruz; ita mutuniyar Yotba ce.
Amón tenía veintidós años cuando llegó a ser rey, y reinó en Jerusalén durante dos años. Su madre se llamaba Mesulémet, hija de Jaruz. Ella era de Jotba.
20 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, yadda Manasse mahaifinsa ya yi.
Sus hechos fueron malos a los ojos del Señor, tal como los de su padre Manasés.
21 Ya bi duk gurbin mahaifinsa a kome, ya yi sujada ga gumakan da mahaifinsa ya yi wa, ya kuma durƙusa musu.
Siguió todos los caminos de su padre, y sirvió a los ídolos que su padre había servido, inclinándose en adoración a ellos.
22 Ya rabu da Ubangiji Allah na kakanninsa, bai kuwa yi tafiya a hanyar Ubangiji ba.
Rechazó al Señor, el Dios de sus antepasados, y no siguió el camino del Señor.
23 Fadawan Amon suka ƙulla maƙarƙashiya suka kashe shi a cikin fadarsa.
Los funcionarios de Amón conspiraron contra él y lo asesinaron en su palacio real.
24 Sai mutanen ƙasar suka kashe duk waɗanda suka ƙulla wa Sarki Amon maƙarƙashiya, sa’an nan suka naɗa ɗansa sarki a maimakonsa.
Pero entonces el pueblo del país mató a todos los que habían conspirado contra el rey Amón, y eligieron a su hijo Josías como rey para sucederlo.
25 Game da sauran ayyukan mulkin Amon, da abubuwan da ya aikata, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
El resto de lo que sucedió en el reinado de Amón, y todo lo que hizo, están registrados en el Libro de las Crónicas de los Reyes de Judá.
26 Aka binne shi a kabarinsa a lambun Uzza. Yosiya ɗansa kuma ya gāje shi.
Fue enterrado en su tumba en el jardín de Uza, y su hijo Josías lo sucedió como rey.

< 2 Sarakuna 21 >