< 2 Sarakuna 21 >

1 Manasse yana da shekara goma sha biyu sa’ad da ya zama sarki, ya yi mulki shekara hamsin da biyar a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Hefziba.
UManase wayeleminyaka elitshumi lambili lapho esiba yinkosi; wabusa iminyaka engamatshumi amahlanu lanhlanu eJerusalema. Lebizo likanina lalinguHefiziba.
2 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, ya bi munanan al’adun al’umman da Ubangiji ya kora a gaban Isra’ilawa.
Wasesenza okubi emehlweni eNkosi njengokwamanyala ezizwe iNkosi eyazixotsha elifeni phambi kwabantwana bakoIsrayeli.
3 Ya sāke gina masujadan da mahaifinsa Hezekiya ya rurrushe. Ya kuma gina wa Ba’al bagadai. Ya kafa ginshiƙin Ashera kamar yadda Ahab sarkin Isra’ila ya yi. Ya durƙusa wa dukan rundunan taurari ya yi musu sujada.
Ngoba wabuya wakha indawo eziphakemeyo uyise uHezekhiya ayezichithile, wamisela uBhali amalathi, wenza isixuku, njengokwenza kukaAhabi inkosi yakoIsrayeli, wakhothamela ibutho lonke lamazulu, walikhonza.
4 Ya gina bagadai a haikalin Ubangiji, wurin da Ubangiji ya ce, “A Urushalima ne zan sa Sunana.”
Wasesakha amalathi endlini yeNkosi, iNkosi eyathi ngayo: EJerusalema ngizabeka ibizo lami.
5 Cikin filaye biyu na haikalin Ubangiji kuwa, ya gina bagadai na dukan rundunan taurari.
Wasesakhela ibutho lonke lamazulu amalathi emagumeni womabili endlini yeNkosi.
6 Ya miƙa ɗansa hadaya ta ƙonawa, ya yi sihiri da tsubu, ya tuntuɓi masu duba da masu ruhohi. Ya aikata mugunta ƙwarai a gaban Ubangiji, ya sa Ubangiji ya yi fushi.
Wasedabulisa indodana yakhe emlilweni, wachasisa ngemibono, wenza imilingo, wasebenza labalamadlozi labalumbayo. Wenza okubi kakhulu emehlweni eNkosi ukuyithukuthelisa.
7 Ya ɗauki siffar ginshiƙin Asherar da ya yi, ya sa a haikalin da Ubangiji ya ce wa Dawuda da ɗansa Solomon, “A cikin wannan haikali, da kuma cikin Urushalima inda na zaɓa daga kabilan Isra’ila, zan sa Sunana har abada.
Wasemisa isithombe esibaziweyo sesixuku ayesenzile endlini, iNkosi eyakhuluma ngayo kuDavida lakuSolomoni indodana yakhe yathi: Kulindlu, leJerusalema engiyikhethe kuzo zonke izizwe zakoIsrayeli, ngizabeka ibizo lami kuze kube nininini.
8 Ba zan ƙara sa Isra’ilawa su fita daga ƙasar da na ba kakanninsu ba, idan dai za su kula su aikata dukan abin da na umarce su, su kuma kiyaye dukan dokokin da na ba wa bawana Musa yă umarce su.”
Kangisayikuzulisa unyawo lukaIsrayeli luphume futhi elizweni engalinika oyise, kuphela uba bezananzelela ukwenza njengakho konke engabalaya khona langokomlayo wonke inceku yami uMozisi eyabalaya wona.
9 Amma mutanen ba su kasa kunne ba. Manasse ya ɓad da su, har suka yi muguntar da ta fi ta al’umman da Ubangiji ya hallaka a gaban Isra’ilawa.
Kodwa kabalalelanga; uManase wasebaphambukisa ukuthi benze okubi okwedlula izizwe iNkosi eyazichitha phambi kwabantwana bakoIsrayeli.
10 Ubangiji ya yi magana ta bakin bayinsa annabawa,
INkosi yasikhuluma ngezinceku zayo abaprofethi isithi:
11 “Manasse, sarkin Yahuda ya aikata waɗannan ƙazantattun zunubai. Ya aikata mugunta fiye da ta Amoriyawan da suka riga shi, ya kuma sa Yahuda ta bauɗe ta wurin yin zunubi saboda gumakansa.
Ngenxa yokuthi uManase inkosi yakoJuda wenzile lamanyala, wenze okubi okwedlula konke amaAmori akwenzayo, ayephambi kwakhe, wonisa loJuda ngezithombe zakhe.
12 Saboda haka ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, zan jawo wa Urushalima da kuma Yahuda masifar da duk kunnen da ya ji, sai ya kusa suma.
Ngakho itsho njalo iNkosi, uNkulunkulu kaIsrayeli: Khangela, ngiletha okubi phezu kweJerusalema loJuda kuthi laye wonke ozwayo indlebe zakhe zombili zizakhenceza ngakho.
13 Zan auna Urushalima da ma’aunin da na yi amfani da shi a kan Samariya, zan kuma yi amfani da magwajin da na yi amfani da shi a kan gidan Ahab. Zan shafe Urushalima yadda mutum yake wanke kwano yă kife.
Ngizakwelula phezu kweJerusalema intambo yeSamariya, lentambo yokulinganisa yendlu kaAhabi, ngiyesule iJerusalema njengowesula umganu, awesule awumbokothe.
14 Zan rabu da ragowar gādona, in kuma miƙa su ga maƙiyansu. Abokan gābansu za su washe suka kuma kwashi ganima daga gare su,
Njalo ngizatshiya insali yelifa lami, ngibanikele esandleni sezitha zabo, babe ngokubanjiweyo lempango kwezitha zabo zonke,
15 domin sun aikata mugunta a idanuna, suka kuma tsokane ni tun daga ranar da kakanninsu suka fito daga Masar, har yă zuwa yau.”
ngenxa yokuthi benzile okubi emehlweni ami, bayangithukuthelisa, kusukela osukwini oyise abaphuma ngalo eGibhithe ngitsho kuze kube lamuhla.
16 Ban da haka ma, Manasse ya zub da jinin marasa laifi har ya cika Urushalima daga wannan ɓangare zuwa wancan, ban da zunubin da ya sa Yahuda ta aikata, ta haka suka yi mugunta a gaban Ubangiji.
Futhi-ke uManase uchithile igazi elinengi kakhulu elingelacala waze wayigcwalisa iJerusalema kusukela ekuqaleni kuze kube sekucineni, ngaphandle kwesono sakhe enza ngaso uJuda ukuthi one, ukwenza okubi emehlweni eNkosi.
17 Game da sauran ayyukan mulkin Manasse, da duk abin da ya yi, har da zunubin da ya aikata, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
Ezinye-ke zezindaba zikaManase, lakho konke akwenzayo, lesono sakhe asonayo, kakubhalwanga yini egwalweni lwemilando yamakhosi akoJuda?
18 Manasse ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a lambun fadansa, lambun Uzza. Sai Amon ɗansa ya gāje shi.
UManase waselala laboyise, wangcwatshelwa esivandeni sendlu yakhe, esivandeni sikaUza. UAmoni indodana yakhe wasesiba yinkosi esikhundleni sakhe.
19 Amon yana da shekara ashirin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya yi mulki shekara biyu a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Meshullemet’yar Haruz; ita mutuniyar Yotba ce.
UAmoni wayeleminyaka engamatshumi amabili lambili lapho esiba yinkosi; wabusa iminyaka emibili eJerusalema. Lebizo likanina lalinguMeshulemethi indodakazi kaHaruzi weJotiba.
20 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, yadda Manasse mahaifinsa ya yi.
Wasesenza okubi emehlweni eNkosi njengokwenza kukaManase uyise.
21 Ya bi duk gurbin mahaifinsa a kome, ya yi sujada ga gumakan da mahaifinsa ya yi wa, ya kuma durƙusa musu.
Wahamba ngendlela yonke uyise ahamba ngayo, wakhonza izithombe uyise azikhonzayo, wakhothama kuzo.
22 Ya rabu da Ubangiji Allah na kakanninsa, bai kuwa yi tafiya a hanyar Ubangiji ba.
Wayidela iNkosi, uNkulunkulu waboyise, kahambanga ngendlela yeNkosi.
23 Fadawan Amon suka ƙulla maƙarƙashiya suka kashe shi a cikin fadarsa.
Izinceku zikaAmoni zasezimenzela ugobe, zabulala inkosi endlini yayo.
24 Sai mutanen ƙasar suka kashe duk waɗanda suka ƙulla wa Sarki Amon maƙarƙashiya, sa’an nan suka naɗa ɗansa sarki a maimakonsa.
Kodwa abantu belizwe babatshaya bonke labo ababenzele inkosi uAmoni ugobe; abantu belizwe basebebeka uJosiya indodana yakhe ukuba yinkosi esikhundleni sakhe.
25 Game da sauran ayyukan mulkin Amon, da abubuwan da ya aikata, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
Ezinye-ke zezindaba zikaAmoni azenzayo kazibhalwanga yini egwalweni lwemilando yamakhosi akoJuda?
26 Aka binne shi a kabarinsa a lambun Uzza. Yosiya ɗansa kuma ya gāje shi.
Wasengcwatshelwa engcwabeni lakhe esivandeni sikaUza. UJosiya indodana yakhe wasesiba yinkosi esikhundleni sakhe.

< 2 Sarakuna 21 >