< 2 Sarakuna 21 >
1 Manasse yana da shekara goma sha biyu sa’ad da ya zama sarki, ya yi mulki shekara hamsin da biyar a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Hefziba.
Manassé avait douze ans à son avènement, et il régna cinquante-cinq ans à Jérusalem. Or le nom de sa mère était Hephtsiba.
2 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, ya bi munanan al’adun al’umman da Ubangiji ya kora a gaban Isra’ilawa.
Et il fit ce qui est mal aux yeux de l'Éternel, imitant les pratiques abominables des nations que l'Éternel avait chassées devant les enfants d'Israël.
3 Ya sāke gina masujadan da mahaifinsa Hezekiya ya rurrushe. Ya kuma gina wa Ba’al bagadai. Ya kafa ginshiƙin Ashera kamar yadda Ahab sarkin Isra’ila ya yi. Ya durƙusa wa dukan rundunan taurari ya yi musu sujada.
Et il releva les tertres qu'avait rasés Ezéchias, son père, et dressa des autels à Baal et fit une Astarté comme avait fait Achab, roi d'Israël, et il adora toute l'armée des cieux, qu'il servit.
4 Ya gina bagadai a haikalin Ubangiji, wurin da Ubangiji ya ce, “A Urushalima ne zan sa Sunana.”
Et il érigea des autels dans le temple de l'Éternel, dont l'Éternel avait dit: C'est dans Jérusalem que je fixerai mon Nom.
5 Cikin filaye biyu na haikalin Ubangiji kuwa, ya gina bagadai na dukan rundunan taurari.
Et il bâtit des autels à toute l'armée des cieux dans les deux parvis du temple de l'Éternel.
6 Ya miƙa ɗansa hadaya ta ƙonawa, ya yi sihiri da tsubu, ya tuntuɓi masu duba da masu ruhohi. Ya aikata mugunta ƙwarai a gaban Ubangiji, ya sa Ubangiji ya yi fushi.
Et il fit passer son fils par le feu, et s'adonna à la divination et aux augures et institua des évocateurs et des devins et il multiplia le mal aux yeux de l'Éternel à l'effet de Le provoquer.
7 Ya ɗauki siffar ginshiƙin Asherar da ya yi, ya sa a haikalin da Ubangiji ya ce wa Dawuda da ɗansa Solomon, “A cikin wannan haikali, da kuma cikin Urushalima inda na zaɓa daga kabilan Isra’ila, zan sa Sunana har abada.
Et il plaça le simulacre d'Astarté, qu'il avait fait, dans le temple duquel l'Éternel avait dit à David et à Salomon, son fils: Dans ce temple et à Jérusalem que j'ai choisie dans toutes les Tribus d'Israël, je fixerai mon Nom pour l'éternité.
8 Ba zan ƙara sa Isra’ilawa su fita daga ƙasar da na ba kakanninsu ba, idan dai za su kula su aikata dukan abin da na umarce su, su kuma kiyaye dukan dokokin da na ba wa bawana Musa yă umarce su.”
Et je ne veux plus qu'Israël porte ses pas errants loin du sol que j'ai donné à ses pères, pourvu seulement qu'il prenne garde de se conformer à tout ce que je lui ai prescrit, et à la totalité de la Loi que lui a prescrite mon serviteur Moïse.
9 Amma mutanen ba su kasa kunne ba. Manasse ya ɓad da su, har suka yi muguntar da ta fi ta al’umman da Ubangiji ya hallaka a gaban Isra’ilawa.
Mais ils n'écoutèrent point, et Manassé les entraîna à faire pis que les nations que l'Éternel avait détruites devant les enfants d'Israël.
10 Ubangiji ya yi magana ta bakin bayinsa annabawa,
Et l'Éternel parla par l'organe de ses serviteurs, les prophètes, et dit:
11 “Manasse, sarkin Yahuda ya aikata waɗannan ƙazantattun zunubai. Ya aikata mugunta fiye da ta Amoriyawan da suka riga shi, ya kuma sa Yahuda ta bauɗe ta wurin yin zunubi saboda gumakansa.
Parce que Manassé, roi de Juda, a pratiqué ces abominations faisant pis que tout ce qu'avaient, fait les Amoréens, antérieurs à lui, et qu'il a aussi entraîné Juda au péché par son idolâtrie,
12 Saboda haka ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, zan jawo wa Urushalima da kuma Yahuda masifar da duk kunnen da ya ji, sai ya kusa suma.
dès là, ainsi prononce l'Éternel, Dieu d'Israël: Voici, j'amène une calamité sur Jérusalem et Juda telle que à quiconque en ouïra parler les deux oreilles lui résonneront,
13 Zan auna Urushalima da ma’aunin da na yi amfani da shi a kan Samariya, zan kuma yi amfani da magwajin da na yi amfani da shi a kan gidan Ahab. Zan shafe Urushalima yadda mutum yake wanke kwano yă kife.
et j'étendrai sur Jérusalem le cordeau de Samarie et le niveau de la maison d'Achab et je frotterai Jérusalem comme on frotte un plat: après l'avoir frotté on le retourne sens dessus dessous.
14 Zan rabu da ragowar gādona, in kuma miƙa su ga maƙiyansu. Abokan gābansu za su washe suka kuma kwashi ganima daga gare su,
Et je ferai abandon du reste de mon héritage que je livrerai à la merci de leurs ennemis, afin qu'ils soient une proie, une dépouille pour tous leurs ennemis,
15 domin sun aikata mugunta a idanuna, suka kuma tsokane ni tun daga ranar da kakanninsu suka fito daga Masar, har yă zuwa yau.”
parce qu'ils ont fait ce qui est mal à mes yeux et qu'ils m'ont provoqué dès le jour où leurs pères sont sortis de l'Egypte, jusqu'aujourd'hui.
16 Ban da haka ma, Manasse ya zub da jinin marasa laifi har ya cika Urushalima daga wannan ɓangare zuwa wancan, ban da zunubin da ya sa Yahuda ta aikata, ta haka suka yi mugunta a gaban Ubangiji.
Et Manassé répandit aussi le sang innocent à grands flots jusqu'à en remplir Jérusalem d'un bout à l'autre bout, non compris son péché où il entraîna Juda pour faire ce qui est mal aux yeux de l'Éternel.
17 Game da sauran ayyukan mulkin Manasse, da duk abin da ya yi, har da zunubin da ya aikata, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
Le reste des actes de Manassé, et toutes ses entreprises et son péché qu'il commit, sont d'ailleurs consignés dans le livre des annales des rois de Juda.
18 Manasse ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a lambun fadansa, lambun Uzza. Sai Amon ɗansa ya gāje shi.
Et Manassé reposa avec ses pères et reçut la sépulture dans le jardin de son palais, dans le jardin d'Uzza, et Amon, son fils, devint roi en sa place.
19 Amon yana da shekara ashirin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya yi mulki shekara biyu a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Meshullemet’yar Haruz; ita mutuniyar Yotba ce.
Amon avait vingt-deux ans à son avènement, et il régna deux ans à Jérusalem. Or le nom de sa mère était Mesullémeth, fille de Harouts de Jotbah.
20 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, yadda Manasse mahaifinsa ya yi.
Et il fit ce qui est mal aux yeux de l'Éternel, comme avait fait Manassé, son père.
21 Ya bi duk gurbin mahaifinsa a kome, ya yi sujada ga gumakan da mahaifinsa ya yi wa, ya kuma durƙusa musu.
Et il marcha sur tous les errements qu'avait suivis son père, et servit les idoles qu'avait servies son père, et il les adora,
22 Ya rabu da Ubangiji Allah na kakanninsa, bai kuwa yi tafiya a hanyar Ubangiji ba.
et il déserta l'Éternel, le Dieu de ses pères, et ne pratiqua point la voie de l'Éternel.
23 Fadawan Amon suka ƙulla maƙarƙashiya suka kashe shi a cikin fadarsa.
Et les serviteurs d'Amon conspirèrent contre lui et donnèrent la mort au roi dans son palais.
24 Sai mutanen ƙasar suka kashe duk waɗanda suka ƙulla wa Sarki Amon maƙarƙashiya, sa’an nan suka naɗa ɗansa sarki a maimakonsa.
Mais le peuple du pays fit périr tous ceux qui avaient conspiré contre le roi Amon et le peuple du pays établit son fils Josias roi en sa place.
25 Game da sauran ayyukan mulkin Amon, da abubuwan da ya aikata, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
Le reste des actes d'Amon, ses entreprises, est d'ailleurs consigné dans le livre des annales des rois de Juda.
26 Aka binne shi a kabarinsa a lambun Uzza. Yosiya ɗansa kuma ya gāje shi.
Et on lui donna la sépulture dans son tombeau, dans le jardin d'Uzza, et Josias, son fils, devint roi en sa place.