< 2 Sarakuna 21 >

1 Manasse yana da shekara goma sha biyu sa’ad da ya zama sarki, ya yi mulki shekara hamsin da biyar a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Hefziba.
Manassé avait douze ans lorsqu'il devint roi, et il régna cinquante-cinq ans à Jérusalem. Le nom de sa mère était Héphziba.
2 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, ya bi munanan al’adun al’umman da Ubangiji ya kora a gaban Isra’ilawa.
Il fit ce qui est mal aux yeux de l'Éternel, selon les abominations des nations que l'Éternel avait chassées devant les enfants d'Israël.
3 Ya sāke gina masujadan da mahaifinsa Hezekiya ya rurrushe. Ya kuma gina wa Ba’al bagadai. Ya kafa ginshiƙin Ashera kamar yadda Ahab sarkin Isra’ila ya yi. Ya durƙusa wa dukan rundunan taurari ya yi musu sujada.
Il rebâtit les hauts lieux qu'Ézéchias, son père, avait détruits; il éleva des autels à Baal et fit une idole d'Astarté, comme avait fait Achab, roi d'Israël; il se prosterna devant toute l'armée du ciel et la servit.
4 Ya gina bagadai a haikalin Ubangiji, wurin da Ubangiji ya ce, “A Urushalima ne zan sa Sunana.”
Il bâtit des autels dans la maison de Yahvé, dont Yahvé avait dit: « Je mettrai mon nom à Jérusalem. »
5 Cikin filaye biyu na haikalin Ubangiji kuwa, ya gina bagadai na dukan rundunan taurari.
Il bâtit des autels pour toute l'armée du ciel dans les deux parvis de la maison de l'Éternel.
6 Ya miƙa ɗansa hadaya ta ƙonawa, ya yi sihiri da tsubu, ya tuntuɓi masu duba da masu ruhohi. Ya aikata mugunta ƙwarai a gaban Ubangiji, ya sa Ubangiji ya yi fushi.
Il fit passer son fils par le feu, pratiqua la sorcellerie, utilisa des enchantements et eut recours à des esprits familiers et à des magiciens. Il fit beaucoup de mal à Yahvé, pour l'irriter.
7 Ya ɗauki siffar ginshiƙin Asherar da ya yi, ya sa a haikalin da Ubangiji ya ce wa Dawuda da ɗansa Solomon, “A cikin wannan haikali, da kuma cikin Urushalima inda na zaɓa daga kabilan Isra’ila, zan sa Sunana har abada.
Il mit l'image gravée d'Asherah qu'il avait faite dans la maison dont Yahvé avait dit à David et à Salomon, son fils: « Dans cette maison et à Jérusalem, que j'ai choisie parmi toutes les tribus d'Israël, je mettrai mon nom pour toujours;
8 Ba zan ƙara sa Isra’ilawa su fita daga ƙasar da na ba kakanninsu ba, idan dai za su kula su aikata dukan abin da na umarce su, su kuma kiyaye dukan dokokin da na ba wa bawana Musa yă umarce su.”
je ne ferai plus errer les pieds d'Israël hors du pays que j'ai donné à leurs pères, si seulement ils s'appliquent à faire tout ce que je leur ai commandé et toute la loi que leur a prescrite mon serviteur Moïse. »
9 Amma mutanen ba su kasa kunne ba. Manasse ya ɓad da su, har suka yi muguntar da ta fi ta al’umman da Ubangiji ya hallaka a gaban Isra’ilawa.
Mais ils n'écoutèrent pas, et Manassé les séduisit pour qu'ils fassent ce qui est mauvais, plus que ne l'ont fait les nations que Yahvé a détruites devant les enfants d'Israël.
10 Ubangiji ya yi magana ta bakin bayinsa annabawa,
Yahvé parla par ses serviteurs les prophètes, et dit:
11 “Manasse, sarkin Yahuda ya aikata waɗannan ƙazantattun zunubai. Ya aikata mugunta fiye da ta Amoriyawan da suka riga shi, ya kuma sa Yahuda ta bauɗe ta wurin yin zunubi saboda gumakansa.
Parce que Manassé, roi de Juda, a commis ces abominations, parce qu'il a fait plus de mal que les Amoréens qui l'ont précédé, et parce qu'il a fait pécher Juda par ses idoles,
12 Saboda haka ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, zan jawo wa Urushalima da kuma Yahuda masifar da duk kunnen da ya ji, sai ya kusa suma.
Yahvé, le Dieu d'Israël, dit: Voici, je vais faire venir sur Jérusalem et sur Juda un tel malheur que, si quelqu'un en entend parler, ses deux oreilles se crisperont.
13 Zan auna Urushalima da ma’aunin da na yi amfani da shi a kan Samariya, zan kuma yi amfani da magwajin da na yi amfani da shi a kan gidan Ahab. Zan shafe Urushalima yadda mutum yake wanke kwano yă kife.
J'étendrai sur Jérusalem la ligne de Samarie et le fil à plomb de la maison d'Achab, et j'essuierai Jérusalem comme on essuie un plat, en l'essuyant et en le retournant.
14 Zan rabu da ragowar gādona, in kuma miƙa su ga maƙiyansu. Abokan gābansu za su washe suka kuma kwashi ganima daga gare su,
Je rejetterai le reste de mon héritage et je le livrerai entre les mains de ses ennemis. Ils seront la proie et le butin de tous leurs ennemis,
15 domin sun aikata mugunta a idanuna, suka kuma tsokane ni tun daga ranar da kakanninsu suka fito daga Masar, har yă zuwa yau.”
parce qu'ils ont fait ce qui est mal à mes yeux et qu'ils m'ont irrité depuis le jour où leurs pères sont sortis d'Égypte jusqu'à ce jour.'"
16 Ban da haka ma, Manasse ya zub da jinin marasa laifi har ya cika Urushalima daga wannan ɓangare zuwa wancan, ban da zunubin da ya sa Yahuda ta aikata, ta haka suka yi mugunta a gaban Ubangiji.
Manassé répandit beaucoup de sang innocent, jusqu'à remplir Jérusalem d'un bout à l'autre, sans compter le péché qu'il fit commettre à Juda, en faisant ce qui est mal aux yeux de l'Éternel.
17 Game da sauran ayyukan mulkin Manasse, da duk abin da ya yi, har da zunubin da ya aikata, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
Le reste des actes de Manassé, tout ce qu'il a fait, et le péché qu'il a commis, cela n'est-il pas écrit dans le livre des Chroniques des rois de Juda?
18 Manasse ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a lambun fadansa, lambun Uzza. Sai Amon ɗansa ya gāje shi.
Manassé se coucha avec ses pères et fut enterré dans le jardin de sa maison, dans le jardin d'Uzza; et Amon, son fils, régna à sa place.
19 Amon yana da shekara ashirin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya yi mulki shekara biyu a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Meshullemet’yar Haruz; ita mutuniyar Yotba ce.
Amon avait vingt-deux ans lorsqu'il devint roi, et il régna deux ans à Jérusalem. Le nom de sa mère était Meshullemeth, fille de Haruz, de Jotba.
20 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, yadda Manasse mahaifinsa ya yi.
Il fit ce qui est mal aux yeux de l'Éternel, comme avait fait Manassé, son père.
21 Ya bi duk gurbin mahaifinsa a kome, ya yi sujada ga gumakan da mahaifinsa ya yi wa, ya kuma durƙusa musu.
Il marcha dans toutes les voies où marchait son père, il servit les idoles que son père servait et se prosterna devant elles;
22 Ya rabu da Ubangiji Allah na kakanninsa, bai kuwa yi tafiya a hanyar Ubangiji ba.
et il abandonna Yahvé, le Dieu de ses pères, et ne marcha pas dans la voie de Yahvé.
23 Fadawan Amon suka ƙulla maƙarƙashiya suka kashe shi a cikin fadarsa.
Les serviteurs d'Amon conspirèrent contre lui et firent mourir le roi dans sa propre maison.
24 Sai mutanen ƙasar suka kashe duk waɗanda suka ƙulla wa Sarki Amon maƙarƙashiya, sa’an nan suka naɗa ɗansa sarki a maimakonsa.
Mais le peuple du pays tua tous ceux qui avaient conspiré contre le roi Amon, et le peuple du pays établit roi Josias, son fils, à sa place.
25 Game da sauran ayyukan mulkin Amon, da abubuwan da ya aikata, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
Et le reste des actes d'Amon qu'il a accomplis, n'est-il pas écrit dans le livre des chroniques des rois de Juda?
26 Aka binne shi a kabarinsa a lambun Uzza. Yosiya ɗansa kuma ya gāje shi.
Il fut enterré dans son tombeau, dans le jardin d'Uzza, et Josias, son fils, régna à sa place.

< 2 Sarakuna 21 >