< 2 Sarakuna 21 >
1 Manasse yana da shekara goma sha biyu sa’ad da ya zama sarki, ya yi mulki shekara hamsin da biyar a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Hefziba.
Manasseh [is] a son of twelve years in his reigning, and he has reigned fifty-five years in Jerusalem, and the name of his mother [is] Hephzi-Bah;
2 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, ya bi munanan al’adun al’umman da Ubangiji ya kora a gaban Isra’ilawa.
and he does evil in the eyes of YHWH, according to the abominations of the nations that YHWH dispossessed from the presence of the sons of Israel,
3 Ya sāke gina masujadan da mahaifinsa Hezekiya ya rurrushe. Ya kuma gina wa Ba’al bagadai. Ya kafa ginshiƙin Ashera kamar yadda Ahab sarkin Isra’ila ya yi. Ya durƙusa wa dukan rundunan taurari ya yi musu sujada.
and he turns and builds the high places that his father Hezekiah destroyed, and raises altars for Ba‘al, and makes an Asherah, as Ahab king of Israel did, and bows himself to all the host of the heavens, and serves them.
4 Ya gina bagadai a haikalin Ubangiji, wurin da Ubangiji ya ce, “A Urushalima ne zan sa Sunana.”
And he has built altars in the house of YHWH, of which YHWH said, “In Jerusalem I put My Name.”
5 Cikin filaye biyu na haikalin Ubangiji kuwa, ya gina bagadai na dukan rundunan taurari.
And he builds altars to all the host of the heavens in the two courts of the house of YHWH;
6 Ya miƙa ɗansa hadaya ta ƙonawa, ya yi sihiri da tsubu, ya tuntuɓi masu duba da masu ruhohi. Ya aikata mugunta ƙwarai a gaban Ubangiji, ya sa Ubangiji ya yi fushi.
and he has caused his son to pass through fire, and observed clouds, and used enchantment, and dealt with a familiar spirit and wizards; he has multiplied to do evil in the eyes of YHWH—to provoke to anger.
7 Ya ɗauki siffar ginshiƙin Asherar da ya yi, ya sa a haikalin da Ubangiji ya ce wa Dawuda da ɗansa Solomon, “A cikin wannan haikali, da kuma cikin Urushalima inda na zaɓa daga kabilan Isra’ila, zan sa Sunana har abada.
And he sets the carved image of the Asherah that he made in the house of which YHWH said to David and to his son Solomon, “In this house, and in Jerusalem, that I have chosen out of all the tribes of Israel, I put My Name for all time;
8 Ba zan ƙara sa Isra’ilawa su fita daga ƙasar da na ba kakanninsu ba, idan dai za su kula su aikata dukan abin da na umarce su, su kuma kiyaye dukan dokokin da na ba wa bawana Musa yă umarce su.”
and I do not add to cause the foot of Israel to move from the ground that I gave to their fathers, only, if they observe to do according to all that I commanded them, and to all the Law that My servant Moses commanded them.”
9 Amma mutanen ba su kasa kunne ba. Manasse ya ɓad da su, har suka yi muguntar da ta fi ta al’umman da Ubangiji ya hallaka a gaban Isra’ilawa.
And they have not listened, and Manasseh causes them to err, to do evil above the nations that YHWH destroyed from the presence of the sons of Israel.
10 Ubangiji ya yi magana ta bakin bayinsa annabawa,
And YHWH speaks by the hand of his servants the prophets, saying,
11 “Manasse, sarkin Yahuda ya aikata waɗannan ƙazantattun zunubai. Ya aikata mugunta fiye da ta Amoriyawan da suka riga shi, ya kuma sa Yahuda ta bauɗe ta wurin yin zunubi saboda gumakansa.
“Because that Manasseh king of Judah has done these abominations—he has done evil above all that the Amorites have done who [are] before him, and also causes Judah to sin by his idols—
12 Saboda haka ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, zan jawo wa Urushalima da kuma Yahuda masifar da duk kunnen da ya ji, sai ya kusa suma.
therefore, thus said YHWH, God of Israel: Behold, I am bringing in calamity on Jerusalem and Judah, that whoever hears of it, his two ears tingle.
13 Zan auna Urushalima da ma’aunin da na yi amfani da shi a kan Samariya, zan kuma yi amfani da magwajin da na yi amfani da shi a kan gidan Ahab. Zan shafe Urushalima yadda mutum yake wanke kwano yă kife.
And I have stretched out the line of Samaria over Jerusalem, and the plummet of the house of Ahab, and wiped Jerusalem as one wipes the dish—he has wiped, and has turned [it] on its face.
14 Zan rabu da ragowar gādona, in kuma miƙa su ga maƙiyansu. Abokan gābansu za su washe suka kuma kwashi ganima daga gare su,
And I have left the remnant of My inheritance, and given them into the hand of their enemies, and they have been for a prey and for a spoil to all their enemies,
15 domin sun aikata mugunta a idanuna, suka kuma tsokane ni tun daga ranar da kakanninsu suka fito daga Masar, har yă zuwa yau.”
because that they have done evil in My eyes, and are provoking Me to anger from the day that their fathers came out of Egypt, even to this day.”
16 Ban da haka ma, Manasse ya zub da jinin marasa laifi har ya cika Urushalima daga wannan ɓangare zuwa wancan, ban da zunubin da ya sa Yahuda ta aikata, ta haka suka yi mugunta a gaban Ubangiji.
And also, Manasseh has shed very much innocent blood, until he has filled Jerusalem mouth to mouth, apart from his sin that he has caused Judah to sin, to do evil in the eyes of YHWH.
17 Game da sauran ayyukan mulkin Manasse, da duk abin da ya yi, har da zunubin da ya aikata, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
And the rest of the matters of Manasseh, and all that he did, and his sin that he sinned, are they not written on the scroll of the Chronicles of the Kings of Judah?
18 Manasse ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a lambun fadansa, lambun Uzza. Sai Amon ɗansa ya gāje shi.
And Manasseh lies with his fathers, and is buried in the garden of his house, in the garden of Uzza, and his son Amon reigns in his stead.
19 Amon yana da shekara ashirin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya yi mulki shekara biyu a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Meshullemet’yar Haruz; ita mutuniyar Yotba ce.
Amon [is] a son of twenty-two years in his reigning, and he has reigned two years in Jerusalem, and the name of his mother [is] Meshullemeth daughter of Haruz of Jotbah,
20 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, yadda Manasse mahaifinsa ya yi.
and he does evil in the eyes of YHWH, as his father Manasseh did,
21 Ya bi duk gurbin mahaifinsa a kome, ya yi sujada ga gumakan da mahaifinsa ya yi wa, ya kuma durƙusa musu.
and walks in all the way that his father walked in, and serves the idols that his father served, and bows himself to them,
22 Ya rabu da Ubangiji Allah na kakanninsa, bai kuwa yi tafiya a hanyar Ubangiji ba.
and forsakes YHWH, God of his fathers, and has not walked in the way of YHWH.
23 Fadawan Amon suka ƙulla maƙarƙashiya suka kashe shi a cikin fadarsa.
And the servants of Amon conspire against him, and put the king to death in his own house,
24 Sai mutanen ƙasar suka kashe duk waɗanda suka ƙulla wa Sarki Amon maƙarƙashiya, sa’an nan suka naɗa ɗansa sarki a maimakonsa.
and the people of the land strike all those conspiring against King Amon, and the people of the land cause his son Josiah to reign in his stead.
25 Game da sauran ayyukan mulkin Amon, da abubuwan da ya aikata, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
And the rest of the matters of Amon that he did, are they not written on the scroll of the Chronicles of the Kings of Judah?
26 Aka binne shi a kabarinsa a lambun Uzza. Yosiya ɗansa kuma ya gāje shi.
And [one] buries him in his burying-place in the garden of Uzza, and his son Josiah reigns in his stead.