< 2 Sarakuna 20 >
1 A kwanakin nan sai Hezekiya ya kamu da rashin lafiya har ya kusa mutuwa. Sai annabi Ishaya ɗan Amoz ya zo wurinsa ya ce, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ka kintsa gidanka domin za ka mutu, ba za ka warke ba.”
Tanī laikā Hizkija palika slims uz miršanu, un pravietis Jesaja, Amoca dēls, nāca pie viņa un uz to sacīja: tā saka Tas Kungs: apkopi savu namu, jo tu mirsi un nepaliksi vesels.
2 Hezekiya ya juya fuskarsa wajen bango ya yi addu’a ga Ubangiji ya ce,
Tad Hizkija savu vaigu pagrieza pret sienu un pielūdza To Kungu un sacīja:
3 “Ya Ubangiji, ka tuna yadda na yi tafiya a gabanka da aminci da zuciya ɗaya, na kuma aikata abin da yake daidai a gabanka.” Sai Hezekiya ya yi kuka mai zafi.
Ak Kungs, piemini lūdzams, ka es Tavā priekšā esmu staigājis patiesībā no visas sirds un darījis, kas tev patīk. Un Hizkija gauži raudāja.
4 Kafin Ishaya yă bar tsakiyar filin gida, sai maganar Ubangiji ta zo masa cewa,
Un kad Jesaja vēl nebija izgājis ne pusceļa caur pilsētu, tad Tā Kunga vārds uz viņu notika un sacīja:
5 “Ka koma ka ce wa Hezekiya, shugaban mutanena, ‘Ga abin da Ubangiji Allah na mahaifinka Dawuda ya ce, na ji addu’arka na kuma ga hawayenka; zan warkar da kai. A rana ta uku daga yau za ka haura zuwa haikalin Ubangiji.
Ej atpakaļ un saki uz Hizkiju, Manas tautas valdnieku: tā saka Tas Kungs, tava tēva Dāvida Dievs: Es tavu lūgšanu esmu klausījis, Es tavas asaras esmu redzējis, redzi, Es tevi darīšu veselu, trešā dienā tu iesi Tā Kunga namā.
6 Zan ƙara maka shekara goma sha biyar. Zan kuma cece ka daga hannun sarkin Assuriya. Zan kāre birnin nan saboda kaina da kuma bawana Dawuda.’”
Un pie tavām dienām Es vēl pielikšu piecpadsmit gadus, un tevi un šo pilsētu Es izpestīšu no Asīrijas ķēniņa rokas un pasargāšu šo pilsētu Sevis labad un Sava kalpa Dāvida labad.
7 Sai Ishaya ya ce, “A kwaɓa ɓaure.” Sai aka yi haka, aka shafa wa marurun, ya kuma warke.
Un Jesaja sacīja: ņemiet vīģu rausi. Un tie to ņēma un uzlika uz to trumu, tad viņš palika vesels.
8 Hezekiya ya tambayi Ishaya, “Wace alama ce za tă nuna cewa Ubangiji zai warkar da ni, kuma cewa in tafi haikalin Ubangiji kwana uku daga yanzu?”
Un Hizkija sacīja uz Jesaju: kāda ir tā zīme, ka Tas Kungs mani darīs veselu, un ka es trešā dienā iešu Tā Kunga namā?
9 Sai Ishaya ya ce, “Ga alamar Ubangiji zuwa gare ka da za tă nuna cewa Ubangiji zai cika alkawarinsa. Kana so inuwa tă yi gaba da taki goma, ko tă koma baya da taki goma?”
Un Jesaja sacīja: šī būs tā zīme no Tā Kunga, ka Tas Kungs šo lietu darīs, ko viņš runājis. Vai ēnai būs iet desmit kāpienus uz priekšu, vai desmit kāpienus atpakaļ?
10 “Ai, abu mai sauƙi ne inuwa tă yi gaba da taki goma.” In ji Hezekiya, “Gwamma dai tă koma baya da taki goma.”
Tad Hizkija sacīja: tas ir viegli, ēnai iet desmit kāpienus uz priekšu, - to ne, bet lai ēna iet desmit kāpienus atpakaļ.
11 Sai annabi Ishaya ya roƙi Ubangiji, Ubangiji kuwa ya sa inuwa ta koma baya da taki goma bisa ga magwajin rana wanda Sarki Ahaz ya gina.
Un pravietis Jesaja piesauca To Kungu, un Tas tai ēnai lika iet desmit kāpienus atpakaļ pa tiem pašiem kāpieniem, ko tā bija gājusi uz priekšu pie Ahaza saules stundeņa.
12 A wannan lokaci, Merodak-Baladan ɗan Baladan sarkin Babilon ya aika wa Hezekiya wasiƙu tare da kyauta, domin ya sami labarin rashin lafiyar Hezekiya.
Tanī laikā Berodaks Baladans, Baladana dēls, Bābeles ķēniņš, sūtīja grāmatas un dāvanas pie Hizkijas, jo tas bija dzirdējis, ka Hizkija bijis slims.
13 Hezekiya ya karɓi jakadun, ya nuna musu dukan abin da yake a ɗakunan ajiyarsa, azurfa, zinariya, kayan ƙanshi da mai, wurin ajiye makamansa da kuma dukan abin da aka samu a ɗakin ajiyarsa. Babu wani abu a fadansa ko a dukan mulkinsa da Hezekiya bai nuna musu ba.
Un Hizkija par tiem priecājās un tiem radīja visu savu mantas namu, sudrabu un zeltu un dārgās zāles un to smalko eļļu un visu savu bruņu namu un visu, kas viņa mantās bija; nekas nebija viņa namā un visā viņa valstī ko Hizkija tiem nebūtu rādījis.
14 Sai annabi Ishaya ya tafi wurin Sarki Hezekiya ya tambaye shi ya ce, “Me mutanen nan suka ce, kuma daga ina suka fito?” Sai Hezekiya ya ce, “Daga ƙasa mai nisa. Daga Babilon.”
Tad pravietis Jesaja nāca pie ķēniņa Hizkijas un uz to sacīja: ko šie vīri sacījuši un no kurienes tie pie tevis nākuši? Un Hizkija sacīja: tie no tālas zemes atnākuši, no Bābeles.
15 Annabin ya yi tambaya, “Me suka gani a fadanka?” Hezekiya ya ce, “Ba abin da yake a ma’ajina da ban nuna musu ba.”
Un tas sacīja: ko tie laba redzējuši tavā namā? Un Hizkija sacīja: tie visu redzējuši, kas manā namā; nekā nav no manām mantām, ko es tiem nebūtu rādījis.
16 Sai Ishaya ya ce wa Hezekiya, “Ka ji kalmar Ubangiji.
Tad Jesaja sacīja uz Hizkiju: klausies Tā Kunga vārdu:
17 Lokaci yana zuwa da za a kwashe kome a fadanka da kuma dukan abubuwan da kakanninka suka tara har yă zuwa yau, a kai su Babilon. Ba abin da za a rage, in ji Ubangiji.
Redzi, dienas nāks, ka viss, kas ir tavā namā un ko tavi tēvi līdz šai dienai sakrājuši, taps novests uz Bābeli, nekas netaps atlicināts, saka Tas Kungs.
18 Za a kuma kwashe waɗansu daga cikin zuriyarka, na jiki da jininka waɗanda za a haifa maka, su zama bābānni a fadan sarkin Babilon.”
Un no taviem bērniem, kas no tevis nāks, ko tu dzemdināsi, taps ņemti, ka tie būs par kambarjunkuriem Bābeles ķēniņa pilī.
19 Hezekiya ya ce, “Maganar Ubangiji da ka faɗa ta yi kyau.” Gama ya yi tunani cewa, “Ai, ba ni da damuwa, tun da yake za a yi zaman lafiya da salama a kwanakina.”
Un Hizkija sacīja uz Jesaju: Tā Kunga vārds ir labs, ko tu runājis. Un viņš sacīja: lai notiek, kad tikai miers un drošība pastāv manā laikā.
20 Game da sauran ayyukan mulkin Hezekiya, dukan nasarorinsa da yadda ya yi tafki da kuma bututun ruwa inda ya kawo ruwa cikin birni, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
Un kas vēl par Hizkiju stāstāms, un viss viņa spēks, un ko viņš darījis, un par to dīķi un ūdens grāvi, un ka viņš ūdeni vadījis pilsētā, tas viss ir rakstīts Jūda ķēniņu laiku grāmatā.
21 Hezekiya ya huta tare da kakanninsa. Manasse ɗansa kuma ya gāje shi.
Un Hizkija aizmiga saviem tēviem pakaļ, un Manasus, viņa dēls, palika par ķēniņu viņa vietā.