< 2 Sarakuna 20 >
1 A kwanakin nan sai Hezekiya ya kamu da rashin lafiya har ya kusa mutuwa. Sai annabi Ishaya ɗan Amoz ya zo wurinsa ya ce, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ka kintsa gidanka domin za ka mutu, ba za ka warke ba.”
En ces jours-là, Ezéchias fut malade jusqu’à la mort; alors vint vers lui Isaïe, le prophète, fils d’Amos, et il lui dit: Voici ce que dit le Seigneur Dieu: Donne des ordres à ta maison; car tu mourras, toi, et tu ne vivras pas.
2 Hezekiya ya juya fuskarsa wajen bango ya yi addu’a ga Ubangiji ya ce,
Ezéchias tourna sa face vers la muraille, et pria le Seigneur disant:
3 “Ya Ubangiji, ka tuna yadda na yi tafiya a gabanka da aminci da zuciya ɗaya, na kuma aikata abin da yake daidai a gabanka.” Sai Hezekiya ya yi kuka mai zafi.
Je vous conjure, Seigneur, souvenez-vous, je vous prie, comment j’ai marché devant vous dans la vérité et avec un cœur parfait, et comment j’ai fait ce qui vous est agréable. Et Ezéchias pleura d’un grand pleur.
4 Kafin Ishaya yă bar tsakiyar filin gida, sai maganar Ubangiji ta zo masa cewa,
Et avant qu’Isaïe eût franchi la moitié du vestibule, la parole du Seigneur lui fut adressée, disant:
5 “Ka koma ka ce wa Hezekiya, shugaban mutanena, ‘Ga abin da Ubangiji Allah na mahaifinka Dawuda ya ce, na ji addu’arka na kuma ga hawayenka; zan warkar da kai. A rana ta uku daga yau za ka haura zuwa haikalin Ubangiji.
Retourne, et dis à Ezéchias, chef de mon peuple: Voici ce que dit le Seigneur Dieu de David, votre père: J’ai entendu ta prière et j’ai vu tes larmes; et voilà que je t’ai guéri, dans trois jours tu monteras au temple du Seigneur.
6 Zan ƙara maka shekara goma sha biyar. Zan kuma cece ka daga hannun sarkin Assuriya. Zan kāre birnin nan saboda kaina da kuma bawana Dawuda.’”
Et j’ajouterai quinze années à tes jours; et même je te délivrerai de la main du roi des Assyriens, toi et cette ville, et je protégerai cette ville, à cause de moi, et à cause de David, mon serviteur.
7 Sai Ishaya ya ce, “A kwaɓa ɓaure.” Sai aka yi haka, aka shafa wa marurun, ya kuma warke.
Alors Isaïe dit aux serviteurs du roi: Apportez-moi une panerée de figues. Lorsqu’ils la lui eurent apportée et qu’ils l’eurent mise sur l’ulcère du roi, il fut guéri.
8 Hezekiya ya tambayi Ishaya, “Wace alama ce za tă nuna cewa Ubangiji zai warkar da ni, kuma cewa in tafi haikalin Ubangiji kwana uku daga yanzu?”
Or Ezéchias avait dit à Isaïe: Quel sera le signe que le Seigneur me guérira, et que je monterai dans trois jours au temple du Seigneur?
9 Sai Ishaya ya ce, “Ga alamar Ubangiji zuwa gare ka da za tă nuna cewa Ubangiji zai cika alkawarinsa. Kana so inuwa tă yi gaba da taki goma, ko tă koma baya da taki goma?”
Isaïe lui répondit: Voici de la part du Seigneur le signe que le Seigneur accomplira la parole qu’il a dite: Voulez-vous que l’ombre du soleil monte de dix lignes, ou qu’elle rétrograde d’autant de degrés?
10 “Ai, abu mai sauƙi ne inuwa tă yi gaba da taki goma.” In ji Hezekiya, “Gwamma dai tă koma baya da taki goma.”
Et Ezéchias dit: Il est facile que l’ombre croisse de dix lignes; et je ne désire pas que cela se fasse; mais qu’elle retourne en arrière de dix degrés.
11 Sai annabi Ishaya ya roƙi Ubangiji, Ubangiji kuwa ya sa inuwa ta koma baya da taki goma bisa ga magwajin rana wanda Sarki Ahaz ya gina.
C’est pourquoi Isaïe, le prophète, invoqua le Seigneur, et il ramena l’ombre par les lignes par lesquelles déjà elle était descendue dans l’horloge d’Achaz, de dix degrés en arrière.
12 A wannan lokaci, Merodak-Baladan ɗan Baladan sarkin Babilon ya aika wa Hezekiya wasiƙu tare da kyauta, domin ya sami labarin rashin lafiyar Hezekiya.
En ce temps-la Bérodach Baladan, fils de Baladan, roi des Babyloniens, envoya des lettres et des présents à Ezéchias; car il avait appris qu’il avait été malade.
13 Hezekiya ya karɓi jakadun, ya nuna musu dukan abin da yake a ɗakunan ajiyarsa, azurfa, zinariya, kayan ƙanshi da mai, wurin ajiye makamansa da kuma dukan abin da aka samu a ɗakin ajiyarsa. Babu wani abu a fadansa ko a dukan mulkinsa da Hezekiya bai nuna musu ba.
Or Ezéchias se réjouit à leur arrivée, et il leur montra la maison de ses aromates, son or, son argent, ses divers parfums, et aussi ses essences, la maison de ses armes, et tout ce qu’il avait dans ses trésors. Et il n’y eut rien qu’Ezéchias ne leur montrât dans son palais et dans tout son domaine.
14 Sai annabi Ishaya ya tafi wurin Sarki Hezekiya ya tambaye shi ya ce, “Me mutanen nan suka ce, kuma daga ina suka fito?” Sai Hezekiya ya ce, “Daga ƙasa mai nisa. Daga Babilon.”
Mais Isaïe, le prophète, vint vers le roi Ezéchias, et lui demanda: Qu’ont dit ces hommes, et d’où sont-ils venus vers vous? Ezéchias lui répondit: C’est d’une terre lointaine qu’ils sont venus vers moi, de Babylone.
15 Annabin ya yi tambaya, “Me suka gani a fadanka?” Hezekiya ya ce, “Ba abin da yake a ma’ajina da ban nuna musu ba.”
Mais Isaïe reprit: Qu’ont-ils vu dans votre maison? Ezéchias répondit: Ils ont vu tout ce qui est dans ma maison; il n’y a rien que je ne leur aie montré dans mes trésors.
16 Sai Ishaya ya ce wa Hezekiya, “Ka ji kalmar Ubangiji.
C’est pourquoi Isaïe dit à Ezéchias: Ecoutez la parole du Seigneur:
17 Lokaci yana zuwa da za a kwashe kome a fadanka da kuma dukan abubuwan da kakanninka suka tara har yă zuwa yau, a kai su Babilon. Ba abin da za a rage, in ji Ubangiji.
Voilà que des jours viendront, et que sera emporté à Babylone tout ce qui est dans ta maison, et tout ce que tes pères y ont amassé jusqu’à ce jour; il n’en restera rien, dit le Seigneur.
18 Za a kuma kwashe waɗansu daga cikin zuriyarka, na jiki da jininka waɗanda za a haifa maka, su zama bābānni a fadan sarkin Babilon.”
Mais on prendra même de tes fils, qui sortiront de toi, que tu engendreras, et ils seront eunuques dans le palais du roi de Babylone.
19 Hezekiya ya ce, “Maganar Ubangiji da ka faɗa ta yi kyau.” Gama ya yi tunani cewa, “Ai, ba ni da damuwa, tun da yake za a yi zaman lafiya da salama a kwanakina.”
Ezéchias répondit à Isaïe: Elle est bonne, la parole du Seigneur, que tu as dite: qu’il y ait paix, et vérité durant mes jours.
20 Game da sauran ayyukan mulkin Hezekiya, dukan nasarorinsa da yadda ya yi tafki da kuma bututun ruwa inda ya kawo ruwa cikin birni, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
Mais le reste des actions d’Ezéchias, et tout son courage, comment il fit la piscine et l’aqueduc, et comment il introduisit les eaux dans la ville, n’est-ce pas écrit dans le Livre des actions des jours des rois de Juda?
21 Hezekiya ya huta tare da kakanninsa. Manasse ɗansa kuma ya gāje shi.
Et Ezéchias dormit avec ses pères, et Manassé, son fils, régna en sa place.