< 2 Sarakuna 19 >

1 Da sarki Hezekiya ya ji haka, sai ya kyakketa tufafinsa, ya sa tufafin makoki, ya shiga haikalin Ubangiji.
A LOHE ae la o Hezekia ke alii, haehae iho la ia i kona aahu, a hoouhi ia ia iho i ke kapa inoino, a komo aku la ia i ka hale o Iehova.
2 Ya aiki Eliyakim sarkin fada, Shebna marubuci da shugabannin firistoci, dukansu sanye da tufafin makoki, zuwa wurin annabi Ishaya ɗan Amoz.
Hoouna aku la ia ia Eliakima ka luna o ko ka hale, a me Sebena, ke kakauolelo, a me ka poe kahiko o na kahuna i hoouhiia i na kapa inoino, io Isaia la ke kaula, ke keiki a Amoza.
3 Suka ce masa, “Hezekiya ya ce, yau ranar wahala ce, da ta cin mutunci, da ta shan kunya, ga shi,’ya’ya suna gab da a haife su, amma ba ƙarfin da za a yi yunƙuri a haife su.
I aku la lakou ia ia, Ke olelo mai nei o Hezekia peneia, O keia la, he la pilikia, poino a me ka hoowahawana: no ka mea, ua hiki mai ka manawa e hanau ai na keiki, aohe ikaika e hanau mai ai.
4 Mai yiwuwa Ubangiji Allahnka ya ji dukan maganganun sarkin yaƙi, wanda maigidansa, sarkin Assuriya, ya aiko don yă rena Allah mai rai. Bari Ubangiji Allahnka yă tsawata masa saboda maganar da ya ji. Saboda haka ka yi addu’a domin raguwar da har yanzu suke a raye.”
Malia paha e hoolohe mai o Iehova kou Akua i na olelo a pau a Rabesake, ka mea a ke alii o Asuria kona haku i hoouna mai ai e hoino i ke Akua ola; a e ahewa aku i na olelo a Iehova kou Akua i lohe ai; nolaila e pule aku oe no ka poe i koe i loaa.
5 Da fadawan sarki Hezekiya suka isa wurin Ishaya,
A hiki aku na kauwa a Hezekia ke alii io Isaia la.
6 Ishaya ya ce musu, “Ku faɗa wa maigidanku, in ji Ubangiji, ‘Kada abin da ka ji yă firgita ka, wato, waɗannan kalmomin da karen nan na sarkin Assuriya ya yi saɓo da su.
I mai la o Isaia ia lakou, Penei oukou e olelo aku ai i ko oukou haku, Ke olelo mai nei o Iehova peneia, Mai makau oe i na olelo au i lohe ai, i ka mea a na kauwa a ke alii o Asuria i hoohiki ino mai ai ia'u.
7 Saurara! Zan sa masa wani ruhun da zai sa yă ji wata jita-jitar da za tă sa yă koma ƙasarsa. A can zan sa a kashe shi da takobi a ƙasarsa.’”
Aia hoi, e hoouna au i makani io na la, a e lohe no ia i ka lono, a hoi aku i kona aina; a e hoohaule iho au ia ia i ka pahikaua ma kona aina iho.
8 Da sarkin yaƙin ya ji cewa sarkin Assuriya ya bar Lakish, sai ya janye, ya kuma iske sarkin yana yaƙi da Libna.
A hoi aku o Rabesake, a loaa ia ia ke alii o Asuria e kana ana i ko Lebena, no ka mea, ua lohe ia, ua haalele oia i Lakisa.
9 To, Sennakerib ya sami labari cewa Tirhaka, mutumin Kush sarkin Masar, yana zuwa masa da yaƙi. Saboda haka ya sāke aika manzanni zuwa wurin Hezekiya cewa,
A lohe ia no Tirehaka ke alii o Aitiopa, i ka i ana ae, Aia hoi, ua hele mai ia e kaua mai ia oe: a hoouna hou aku la ia i na elele io Hezekia la, i aku la,
10 “Ku faɗa wa Hezekiya sarkin Yahuda, kada ka bar allahn da kake dogara gare shi yă ruɗe ka cewa, ‘Urushalima ba za tă fāɗi a hannun sarkin Assuriya ba.’
Penei oukou e olelo aku ai ia Hezekia ke alii o ka Iuda, e i aku, E malama o hoopunipuniia oe e kou Akua au i hilinai ai, i ka i ana'e, Aole e haawiia o Ierusalema iloko o ka lima o ke alii o ko Asuria.
11 Ba shakka ka riga ka ji abin da sarkin Assuriya ya yi da dukan ƙasashe, yana hallaka su gaba ɗaya. Kai kuwa kana ji za a cece ka?
Aia hoi, ua lohe no oe i ka mea a na'lii o Asuria i hana aku ai i na aina a pau, ma ka luku loa ana ia lakou: a e hoopakeleia anei oe?
12 Allolin al’umman da kakannina suka hallaka, sun cece su ne, allolin Gozan, da na Haran, da na Rezef, da kuma na mutane Eden da suke a Tel Assar?
Ua hoopakele anei na akua o na lahuikanaka ia lakou, i na mea a ko'u mau makua i luku ai: i Gozana, i Harama, i Rezepa, a me na kanaka o Edena, ka poe ma Telasara?
13 Ina sarkin Hamat, da sarkin Arfad, da sarkin birnin Sefarfayim, ko na Hena da kuma na Iffa?”
Auhea ke alii o Hamata, a me ke alii o Arepada, a me ke alii no na kulanakauhale o Separevaima, o Hena, a me Iva?
14 Hezekiya ya karɓi wasiƙar daga manzannin ya karanta. Sa’an nan ya tashi ya tafi haikalin Ubangiji ya shimfiɗa wasiƙar a gaban Ubangiji.
A lawe ae la o Hezekia i na palapala mai ka lima mai o na elele, a heluhelu iho la ia mau mea: a pii ae la o Hezekia i ka hale o Iehova, a hohola aku la ia mau mea imua o Iehova.
15 Hezekiya kuwa ya yi addu’a ga Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda yake zaune tsakanin kerubobi, kai kaɗai ne Allah bisa dukan mulkokin duniya. Kai ka yi sama da duniya.
Pule aku la o Hezekia imua o Iehova, i aku la, E Iehova ke Akua o ka Iseraela, ka mea e noho ana maluna o na keruba, o oe no ke Akua, o oe wale no, o na aupuni a pau o ka honua; o oe ka i hana i ka lani a me ka honua.
16 Ka kasa kunne, ya Ubangiji, ka ji; ka buɗe idanunka ya Ubangiji ka gani; ka saurari kalmomin da Sennakerib ya aiko don yă yi wa Allah mai rai ba’a.
E Iehova, e haliu mai kou pepeiao, a e lohe: e Iehova, e wehe ae i kou maka, a ike; a lohe i na olelo a Senakeriba, ana i hoouna mai ai e hoino aku i ke Akua ola.
17 “Da gaske ne, ya Ubangiji, cewa sarakunan Assuriya sun hallakar da waɗannan al’ummai da ƙasashensu.
He oiaio no, e Iehova, ua luku aku na'lii o Asuria i na lahuikanaka a me ko lakou aina;
18 Sun jefar da allolinsu cikin wuta, suka hallaka su, gama ba alloli ba ne, katakai ne da kuma duwatsu, ayyukan hannuwan mutane.
A ua haawi aku i ko lakou mau akua i ke ahi; no ka mea, aole lakou he akua, aka, he hana a na lima kanaka, he laau, a he pohaku: nolaila, ua luku aku lakou ia lakou la.
19 To, ya Ubangiji Allahnmu, ka cece mu daga hannunsa, don dukan mulkokin duniya su san cewa kai kaɗai, ya Ubangiji ne Allah.”
Ano hoi, E Iehova ko makou Akua, ke nonoi aku nei au ia oe, e hoopakele mai oe ia makou mailoko mai o kona lima, i ike ai na aupuni a pau o ka honua, o oe no o Iehova ke Akua, o oe wale no.
20 Sai Ishaya ɗan Amoz ya aika da saƙo zuwa wurin Hezekiya cewa, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, na ji addu’arka game da Sennakerib sarkin Assuriya.
A hoouna aku la o Isaia ke keiki a Amoza io Hezekia la, i aku la, Ke olelo mai nei o Iehova ke Akua o ka Iseraela peneia, Ua lohe au i ka mea au i pule mai ai ia'u no Senakeriba ke alii o Asuria.
21 Ga abin da Ubangiji yana cewa game da shi, “‘Budurwar Sihiyona ta rena ka tana kuma yin maka ba’a. Diyar Urushalima ta kaɗa kanta yayinda kake gudu.
Eia ka olelo a Iehova i olelo mai ai nona; O ka wahine puupaa, ke kaikamahine a Ziona, ua hoowahawaha mai ia ia oe, a ua akaaka mai ia oe: o ke kaikamahine a Ierusalema, ua hooluli mai ia i kona poo mahope ou.
22 Wane ne ka zaga, ka kuma yi masa saɓo? Wa kake gāba da shi har ka ɗaga muryarka, har ka tā da idanunka da fahariya? Kana gāba da Mai Tsarki na Isra’ila!
Owai la kau i hoino ai, a i hoohiki ino ai? Maluna owai kau i hookiekie ai i ka leo, a hapai ai i kou maka iluna? maluna o ka Mea Hemolele o ka Iseraela.
23 Ta wurin manzanninka ka tara wa Ubangiji zagi. Ka kuma ce, “Da yawa kekunan yaƙina na haye kan ƙwanƙolin duwatsu, wurin mafi tsawo na Lebanon. Na sassare itacen al’ul nasa mafi tsawo mafi daraja na itacen fir nasa. Na ratsa har can tsakiyar kurmi, mafi kyau na kurminsa.
Ma kou poe elele ua hoino oe ia Iehova, a ua i mai, Me na halekaa o'u a nui, ua pii mai au i kahi kiekie o na mauna, i na aoao hoi o Lebanona, a e kua aku au i kona mau laau kedera loloa, a me kona mau laau paina maikai: a e komo aku au i ka halekipa o kona mokuna, i ka ululaau o kona kihapai ulu.
24 Na tona rijiyoyi a ƙasashen waje na kuma sha ruwa a can. Da tafin ƙafafuna na busar da dukan rafuffukan Masar.”
Ua eli iho an, a ua inu i ka wai malihini, a me ka poho o kuu wawae, ua hoomaloo au i na muliwai o Aigupita.
25 “‘Ba ka taɓa ji ba? Tun da daɗewa na ƙaddara haka. Tuntuni kuwa na shirya shi; yanzu kuma na sa ya faru, cewa ka mai da birane masu katanga tarin duwatsu.
Aole anei oe i lohe i ka manawa mamua, na'u no ia i hana, a i na wa kahiko, na'u no ia i hookumu? ano, ua hooko no au, i lilo ai oe i mea e luku ai i na kulanakauhale i hoopaaia, a lilo i mau puu opala.
26 Ƙarfin mutanensu ya tsiyaye, suka razana aka kuma kunyata su. Suna kama da tsirai a gona, kamar sabon toho kamar ciyawa mai tohuwa bisa rufin ɗaki wanda ya bushe saboda zafi, kafin yă yi girma.
Nolaila ua nawaliwali ko lakou poe kanaka, a ua weliweli a pihoihoi, ua like lakou me ka launahele o ke kula, a me ka laau uliuli, me ka weuweu maluna o ka hale, a me ka palaoa eleele mamua o ka opuu ana.
27 “‘Amma na san wurin zamanka da fitarka da shigarka da yadda kake fushi da ni.
Aka, ua ike au i kou noho ana, a me kou hele ana iwaho, a me kou komo ana iloko, a me kou inaina ana ia'u.
28 Domin kana fushi da ni reninka ya iso kunnuwata, zan sa ƙugiyata a hancinka da linzamina a bakinka, zan kuma sa ka koma a ta hanyar da ka zo.’
No kou inaina ana mai ia'u, a no ka pii ana mai o kou haaheo iloko o ko'u pepeiao, nolaila, e hookomo au i ko'u lou i kou ihu, a me ko'u kaulawaha i kou lehelehe, a e hoihoi aku au ia oe ma ke ala au i hele mai nei.
29 “Wannan zai zama alama a gare ka, ya Hezekiya, “Bana, za ku ci amfanin gonar da ya tsira da kansa, baɗi kuma amfanin gonar da ya tsiro daga na bara. Amma a shekara ta uku, za ku yi shuki, ku kuma girbe, ku dasa gonakin inabi, ku kuma ci’ya’yansa.
O keia ka hoailona ia oe, e ai oukou i keia makahiki i ka ai uluwale, a ia makahiki aku i ka mea uluwale; a i ke kolu o ka makahiki e lulu oukou, a e hoiliili, a e kanu i na malawaina, a e ai i kona hua.
30 Sau ɗaya kuma ragowar masarautar Yahuda za tă yi saiwoyi a ƙasa ta kuma ba da’ya’ya a bisa.
A o ke koena i pakele o ka ohana o Iuda e kolo lea ke aa malalo, a e hua mai i ka hua maluna.
31 Gama daga Urushalima za a sami ragowa, daga Dutsen Sihiyona kuma za a sami waɗanda suka tsira. Himmar Ubangiji Maɗaukaki za tă cika wannan.
No ka mea, e puka aku auanei ke koena mai Ierusalema aku, a me ka poe i pakele mai ka mauna o Ziona aku: o ka ikaika o Iehova e hana mai i keia.
32 “Saboda haka ga abin da Ubangiji ya ce game da sarkin Assuriya, “Ba zai shiga birnin nan ba ko yă harba kibiya a nan. Ba zai kusace ta da garkuwa ko yă yi mata zoben yaƙi ba.
No ia mea, ke olelo mai nei o Iehova penei no ke alii o Asuria, Aole ia e komo maloko o keia kulanakauhale, aole hoi e pana aku i ka pua malaila, aole hoi o hele mai imua ona me ka palekaua, aole e hoahu i puu e ku pono ana ia ia.
33 Ta hanyar da ya zo ne zai koma; ba zai shiga birnin nan ba, in ji Ubangiji.
Ma ke ala ana i hele mai ai, malaila oia e hoi aku ai, aole ia e komo iloko o keia kulanakauhale, wahi a Iehova.
34 Zan kāre birnin nan in cece ta, saboda kaina da kuma bawana Dawuda.”
No ka mea, e malama no wau i keia kulanakauhale, e hoola no ia ia no'u, a no Davida kau kauwa.
35 A daren nan mala’ikan Ubangiji ya fita ya kashe dakaru dubu ɗari da tamanin da biyu a sansanin Assuriyawa. Da mutane suka farka da safe, sai ga gawawwaki ko’ina.
A ia po iho, hele aku la ka anela o Iehova, a luku aku la, ma kahi hoomoana o ko Asuria, i hookahi haneri a me kanawalukumamalima tausani: a ala ae la lakou i kakahiaka nui, aia hoi, he poe kupapau make lakou a pau.
36 Saboda haka Sennakerib sarkin Assuriya ya tā da sansanin ya kuma janye. Ya koma Ninebe ya zauna a can.
A haalele aku la o Senakeriba ke alii o Asuria, hele aku a hoi aku la, a noho iho la ma Nineve.
37 Wata rana yayinda yake sujada a haikalin Nisrok, allahnsa, sai’ya’yansa maza, Adrammelek da Sharezer suka kashe shi da takobi, suka gudu zuwa ƙasar Ararat. Sai Esar-Haddon ɗansa ya gāje shi.
A i kona hoomana ana ma ka hale o Niseroka kona akua, o Aderameleka, a me Sarezera, kana mau keiki, pepehi aku la laua ia ia me ka pahikaua, a holo laua i ka aina o Ararata. A noho alii iho la o Esarehadona, kana keiki, ma kona hakahaka.

< 2 Sarakuna 19 >