< 2 Sarakuna 19 >
1 Da sarki Hezekiya ya ji haka, sai ya kyakketa tufafinsa, ya sa tufafin makoki, ya shiga haikalin Ubangiji.
Ce qu’ayant entendu le roi Ezéchias, il déchira ses vêtements, se couvrit d’un sac, et entra dans la maison du Seigneur.
2 Ya aiki Eliyakim sarkin fada, Shebna marubuci da shugabannin firistoci, dukansu sanye da tufafin makoki, zuwa wurin annabi Ishaya ɗan Amoz.
Et il envoya Eliacim, intendant de sa maison, Sobna, le scribe, et les anciens d’entre les prêtres, couverts de sacs, à Isaïe, le prophète, fils d’Amos,
3 Suka ce masa, “Hezekiya ya ce, yau ranar wahala ce, da ta cin mutunci, da ta shan kunya, ga shi,’ya’ya suna gab da a haife su, amma ba ƙarfin da za a yi yunƙuri a haife su.
Lesquels dirent: Voici ce que dit Ezéchias: C’est un jour de tribulation, de reproche et de blasphème, que ce jour: des enfants sont venus jusqu’à l’enfantement, et celle qui est en travail n’a pas de forces.
4 Mai yiwuwa Ubangiji Allahnka ya ji dukan maganganun sarkin yaƙi, wanda maigidansa, sarkin Assuriya, ya aiko don yă rena Allah mai rai. Bari Ubangiji Allahnka yă tsawata masa saboda maganar da ya ji. Saboda haka ka yi addu’a domin raguwar da har yanzu suke a raye.”
Peut-être que le Seigneur ton Dieu entendra toutes les paroles de Rabsacès, qu’a envoyé le roi des Assyriens, son maître, pour insulter le Dieu vivant, et l’attaquer par les paroles que le Seigneur ton Dieu a entendues: fais donc une prière au Seigneur pour les restes qui ont été retrouvés.
5 Da fadawan sarki Hezekiya suka isa wurin Ishaya,
Les serviteurs du roi Ezéchias vinrent donc vers Isaïe.
6 Ishaya ya ce musu, “Ku faɗa wa maigidanku, in ji Ubangiji, ‘Kada abin da ka ji yă firgita ka, wato, waɗannan kalmomin da karen nan na sarkin Assuriya ya yi saɓo da su.
Et Isaïe leur répondit: Vous direz à votre maître: Voici ce que dit le Seigneur: Ne crains point à cause des paroles que tu as entendues, par lesquelles m’ont blasphémé les serviteurs du roi des Assyriens.
7 Saurara! Zan sa masa wani ruhun da zai sa yă ji wata jita-jitar da za tă sa yă koma ƙasarsa. A can zan sa a kashe shi da takobi a ƙasarsa.’”
Voilà que moi je lui enverrai un esprit, et il apprendra une nouvelle, et il retournera dans sa terre, et je l’abattrai par le glaive dans sa terre.
8 Da sarkin yaƙin ya ji cewa sarkin Assuriya ya bar Lakish, sai ya janye, ya kuma iske sarkin yana yaƙi da Libna.
Rabsacès s’en retourna donc, et il trouva le roi des Assyriens assiégeant Lobna; car il avait su qu’il s’était retiré de devant Lachis.
9 To, Sennakerib ya sami labari cewa Tirhaka, mutumin Kush sarkin Masar, yana zuwa masa da yaƙi. Saboda haka ya sāke aika manzanni zuwa wurin Hezekiya cewa,
Et lorsque Sennachérib eut entendu, au sujet de Tharaca, roi d’Ethiopie, des gens disant: Voilà qu’il est sorti pour combattre contre vous, et qu’il allait marcher contre ce roi, il envoya des messagers à Ezéchias, en disant:
10 “Ku faɗa wa Hezekiya sarkin Yahuda, kada ka bar allahn da kake dogara gare shi yă ruɗe ka cewa, ‘Urushalima ba za tă fāɗi a hannun sarkin Assuriya ba.’
Vous direz ceci à Ezéchias, roi de Juda: Que votre Dieu, en qui vous avez confiance, ne vous séduise pas, et ne dites point: Jérusalem ne sera point livrée aux mains du roi des Assyriens.
11 Ba shakka ka riga ka ji abin da sarkin Assuriya ya yi da dukan ƙasashe, yana hallaka su gaba ɗaya. Kai kuwa kana ji za a cece ka?
Car vous-même, vous avez appris ce que les rois des Assyriens ont fait à tous les pays, comment ils les ont ravagés: est-ce donc que seul vous pourrez échapper?
12 Allolin al’umman da kakannina suka hallaka, sun cece su ne, allolin Gozan, da na Haran, da na Rezef, da kuma na mutane Eden da suke a Tel Assar?
Est-ce que les dieux des nations ont délivré tous ceux qu’ont ravagés mes pères, c’est-à-dire Gozan, Haran, Réseph, et les enfants d’Eden, qui étaient en Thélassar?
13 Ina sarkin Hamat, da sarkin Arfad, da sarkin birnin Sefarfayim, ko na Hena da kuma na Iffa?”
Où est le roi d’Emath, le roi d’Arphad, le roi de la ville de Sépharvaïm, d’Ana et d’Ava?
14 Hezekiya ya karɓi wasiƙar daga manzannin ya karanta. Sa’an nan ya tashi ya tafi haikalin Ubangiji ya shimfiɗa wasiƙar a gaban Ubangiji.
C’est pourquoi, lorsqu’Ezéchias eut reçu la lettre de Sennachérib de la main des messagers, et qu’il l’eut lue, il monta dans le temple, et étendit la lettre devant le Seigneur,
15 Hezekiya kuwa ya yi addu’a ga Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda yake zaune tsakanin kerubobi, kai kaɗai ne Allah bisa dukan mulkokin duniya. Kai ka yi sama da duniya.
Et il pria en sa présence, disant: Seigneur Dieu d’Israël, qui êtes assis sur les chérubins, c’est vous qui êtes le seul Dieu de tous les rois de la terre; c’est vous qui avez fait le ciel et la terre.
16 Ka kasa kunne, ya Ubangiji, ka ji; ka buɗe idanunka ya Ubangiji ka gani; ka saurari kalmomin da Sennakerib ya aiko don yă yi wa Allah mai rai ba’a.
Inclinez votre oreille et écoutez; ouvrez vos yeux. Seigneur, et voyez: écoutez toutes les paroles de Sennachérib, qui a envoyé pour incriminer devant nous le Dieu vivant.
17 “Da gaske ne, ya Ubangiji, cewa sarakunan Assuriya sun hallakar da waɗannan al’ummai da ƙasashensu.
Il est vrai, Seigneur, les rois des Assyriens ont détruit les nations et toutes leurs terres,
18 Sun jefar da allolinsu cikin wuta, suka hallaka su, gama ba alloli ba ne, katakai ne da kuma duwatsu, ayyukan hannuwan mutane.
Et ils ont jeté leurs dieux dans le feu; car ce n’étaient point des dieux, mais des ouvrages de mains d’hommes, de bois et de pierre, et ils les ont détruits.
19 To, ya Ubangiji Allahnmu, ka cece mu daga hannunsa, don dukan mulkokin duniya su san cewa kai kaɗai, ya Ubangiji ne Allah.”
Maintenant donc, Seigneur notre Dieu, sauvez-nous de la main de ce roi, afin qu’ils sachent, tous les royaumes de la terre, que c’est vous qui êtes le seul Seigneur Dieu.
20 Sai Ishaya ɗan Amoz ya aika da saƙo zuwa wurin Hezekiya cewa, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, na ji addu’arka game da Sennakerib sarkin Assuriya.
Or Isaïe, fils d’Amos, envoya vers Ezéchias, disant: Voici ce que dit le Seigneur Dieu d’Israël: La prière que tu m’as faite touchant Sennachérib, roi des Assyriens, je l’ai entendue.
21 Ga abin da Ubangiji yana cewa game da shi, “‘Budurwar Sihiyona ta rena ka tana kuma yin maka ba’a. Diyar Urushalima ta kaɗa kanta yayinda kake gudu.
Voici la parole que le Seigneur a dite de lui: Elle t’a méprisé et elle t’a raillé, la vierge, fille de Sion, derrière toi elle a secoué la tête, la fille de Jérusalem.
22 Wane ne ka zaga, ka kuma yi masa saɓo? Wa kake gāba da shi har ka ɗaga muryarka, har ka tā da idanunka da fahariya? Kana gāba da Mai Tsarki na Isra’ila!
Qui as-tu insulté et qui as-tu blasphémé? contre qui as-tu élevé la voix, et porté en haut les yeux? contre le saint d’Israël.
23 Ta wurin manzanninka ka tara wa Ubangiji zagi. Ka kuma ce, “Da yawa kekunan yaƙina na haye kan ƙwanƙolin duwatsu, wurin mafi tsawo na Lebanon. Na sassare itacen al’ul nasa mafi tsawo mafi daraja na itacen fir nasa. Na ratsa har can tsakiyar kurmi, mafi kyau na kurminsa.
Par l’entremise de tes serviteurs tu as insulté le Seigneur, et tu as dit: Avec la multitude de mes quadriges je suis monté sur le haut des montagnes, au sommet du Liban: j’ai coupé par le pied ses hauts cèdres et ses sapins les plus beaux. Je suis même entré jusqu’à l’extrémité de ses limites, et la forêt de son Carmel,
24 Na tona rijiyoyi a ƙasashen waje na kuma sha ruwa a can. Da tafin ƙafafuna na busar da dukan rafuffukan Masar.”
C’est moi qui l’ai coupée par le pied. Et j’ai bu des eaux étrangères, et j’ai séché par les traces de mes pieds toutes les eaux fermées.
25 “‘Ba ka taɓa ji ba? Tun da daɗewa na ƙaddara haka. Tuntuni kuwa na shirya shi; yanzu kuma na sa ya faru, cewa ka mai da birane masu katanga tarin duwatsu.
N’as-tu donc point ouï dire ce que dès le commencement j’ai fait? Dès les jours anciens je l’ai préparé, et c’est maintenant que je l’ai exécuté; et des villes de combattants fortifiées seront comme des collines ruinées.
26 Ƙarfin mutanensu ya tsiyaye, suka razana aka kuma kunyata su. Suna kama da tsirai a gona, kamar sabon toho kamar ciyawa mai tohuwa bisa rufin ɗaki wanda ya bushe saboda zafi, kafin yă yi girma.
Et ceux qui y sont dedans, faibles de main, ont tremblé et ont été confondus: ils sont devenus comme le foin d’un champ, comme l’herbe verte des toits et qui sèche avant de venir à maturité.
27 “‘Amma na san wurin zamanka da fitarka da shigarka da yadda kake fushi da ni.
Ta demeure, ton entrée, ta sortie, et ton chemin par où tu es venu, je les ai sus d’avance, et même ta fureur contre moi.
28 Domin kana fushi da ni reninka ya iso kunnuwata, zan sa ƙugiyata a hancinka da linzamina a bakinka, zan kuma sa ka koma a ta hanyar da ka zo.’
Tu as été furieux contre moi, et ton orgueil est monté à mes oreilles: c’est pourquoi je mettrai un cercle à tes narines et un mors à tes lèvres, et je te ramènerai par la voie par laquelle tu es venu.
29 “Wannan zai zama alama a gare ka, ya Hezekiya, “Bana, za ku ci amfanin gonar da ya tsira da kansa, baɗi kuma amfanin gonar da ya tsiro daga na bara. Amma a shekara ta uku, za ku yi shuki, ku kuma girbe, ku dasa gonakin inabi, ku kuma ci’ya’yansa.
Mais pour toi, Ezéchias, voici un signe: Mange cette année ce que tu trouveras; en la seconde année, ce qui naîtra de soi-même; mais, en la troisième année, semez et recueillez, plantez des vignes et mangez-en le fruit.
30 Sau ɗaya kuma ragowar masarautar Yahuda za tă yi saiwoyi a ƙasa ta kuma ba da’ya’ya a bisa.
Et tout ce qui sera de reste de la maison de Juda, jettera des racines en bas et fera des fruits en haut.
31 Gama daga Urushalima za a sami ragowa, daga Dutsen Sihiyona kuma za a sami waɗanda suka tsira. Himmar Ubangiji Maɗaukaki za tă cika wannan.
Car de Jérusalem sortiront des restes, et ce qui sera sauvé de la montagne de Sion: le zèle du Seigneur des armées fera cela.
32 “Saboda haka ga abin da Ubangiji ya ce game da sarkin Assuriya, “Ba zai shiga birnin nan ba ko yă harba kibiya a nan. Ba zai kusace ta da garkuwa ko yă yi mata zoben yaƙi ba.
C’est pourquoi voici ce que dit le Seigneur du roi des Assyriens: Il n’entrera point dans cette ville, il ne lancera point contre elle de flèche; pas un bouclier ne l’occupera, et pas un retranchement ne l’entourera.
33 Ta hanyar da ya zo ne zai koma; ba zai shiga birnin nan ba, in ji Ubangiji.
Il retournera par la voie par laquelle il est venu; et il n’entrera point dans cette ville, dit le Seigneur.
34 Zan kāre birnin nan in cece ta, saboda kaina da kuma bawana Dawuda.”
Je protégerai cette ville, et je la sauverai à cause de moi et à cause de mon serviteur David.
35 A daren nan mala’ikan Ubangiji ya fita ya kashe dakaru dubu ɗari da tamanin da biyu a sansanin Assuriyawa. Da mutane suka farka da safe, sai ga gawawwaki ko’ina.
Il arriva donc en cette nuit-là qu’il vint un ange du Seigneur, et qu’il tua dans le camp des Assyriens cent quatre-vingt mille hommes. Et lorsqu’au point du jour il se fut levé, il vit tous les corps des morts et, se retirant, il s’en alla.
36 Saboda haka Sennakerib sarkin Assuriya ya tā da sansanin ya kuma janye. Ya koma Ninebe ya zauna a can.
Ainsi s’en retourna Sennachérib, roi des Assyriens, et il demeura à Ninive.
37 Wata rana yayinda yake sujada a haikalin Nisrok, allahnsa, sai’ya’yansa maza, Adrammelek da Sharezer suka kashe shi da takobi, suka gudu zuwa ƙasar Ararat. Sai Esar-Haddon ɗansa ya gāje shi.
Et lorsqu’il adorait dans le temple Nesroch, son dieu, Adramélech et Sarasar, ses fils, le frappèrent du glaive, et s’enfuirent dans la terre des Arméniens, et Asarhaddon, son fils, régna eu sa place.